Chapter 74
Chapter 74
razana sosai, tana fita daga gidan ta Kara gudun motar. Su Mardiya ko ina za'a je, me take Shirin aikatawa oho? ________________________ Kumin afuwa mun koma school shiyasa kuka jini shiru, Amma Alhamdulillah yau muka Gama exam. Please comment and share. Milhaat Ce Yar Terawa. 79&80 Continuation..............''' "Yane abokina" "Dallah Malam ina ka ajiye wayar Kane ina ta Kiran ka Amma baka d'aga ba, Ina ka Shiga ne?" " Afwan mun fita da baby ne ya ake cikine? " " Baka ga sakon da na tura maka ba" "A a ban gani ba Wallahi, dake wayar bata hannu na" Waro Ido yayi yace "Ban Gane ba Abdallah a hannun wa wayar take?" "Mardiya ce fa ta rike min wayar ne" "Innalillahi Shikenan asiri na ya tonu idan har mardiya taga sakon Nan don Wallahi nasan baza ta rufa min asiri ba" "Wai me ka turo min ne duk Naga ka Riki ce?" " Ka duba ka gani please ta bud'e ko bata bud'e ba" 'dan cire wayan yayi daga kunnen sa ya duba, Murmushi yayi kana yace "ba a bud'e ba ka kwantar da hankalin ka bata gani ba" Wani ajiyar zuciya ya sauke kana yace "Alhamdulillah dama Ayrah ce ba Lafiya nake so ka kawo Mana maganin zazzabi please" " Okay bara na je na sayo, yanzu zan Shigo gidan" " Okay" a tare suka katse wayar. Direct police station ta nufa, tana parking da saurin ta ta fito tana gudu ta Shiga, Police din dake Kan canter har ya tsorata sabida irin gudun da ta Shigo da dashi leka Bayan ta yake ko wani ne ya biyo ta yayinda mardiya Kuma sai faman haki take kamar numfashin ta zai d'auke, sai faman kallon ta yake Yana kifkifta Ido yace "Madam Lafiya wa ya biyo ka?" Da Yar hausar sa da bata gama nuna ba . Murya na rawa ta fara magana "Qawata wacce ake nema kwanaki ba a ganta ba naji labarin inda take" "To yallab'ai wani kawarki Kenn....... " Bai karasa maganar ba sai ga shigowar DPO Sara Masa yayi had'e da bankare kirjinsa Kallo d'aya ya Masa yace "relax" maida kallon sa yayi ga Mardiya yace Wace ce kike magana akai sannan ya sunan ta" "Ayrah..... Ayrah Alhassan" zaro Ido yayi had'e fa fad'in " kin tabbatar da abinda kike fad'a?" "Eh na tabbata" Maida kallon sa yayi ga Police din kana yace "Take her statement, Sannan ku shirya don dani za a fita" Sara Masa yayi had'e da fad'in " okay sir" Nan ta Basu dukkanin details din, dama ta bar karamar wayar tane a cikin motar Kuma wayan is on call taji maganar da suke, Luckily ya sa wayan a handsfree hakan yasa taji dukkanin maganar da suke. Number ta bawa Police din don yin tracking ai kuwa ba a d'au lokaci Mai tsawo ba aka gano inda Abdallah yake Nan da Nan suka Fara binsa a sace, da motar Ayrah sukayi amfani sabida bai santa da wannan motar ba, Bayan Abdallah yayi horn a gate d'in ba d'au lokaci ba Adnan yazo ya wangale Masa gate d'in, Yana Shiga tun Kan ya rufe kofar motar Mardiya ta sa Kai cikin gidan nan da nan polisawa sun fi biyar suka sauko daga cikin motar dukkanin su day bindigogi , Suna pointing din Adnan. Nan da Nan Adnan hankalin sa ya tashi, Abdallah da ya fito daga motar baki a bud'e yake kallon su, hannun sa rike yake da ledan magana, cikin wata iriyar murya kamar zaiyi kuka Adnan yace "Abdullah ya zaka min Haka?" "Wallahi tallahi ban San sun biyo ni ba" Mardiya ce ta fito tana wani irin Taku tana tauna cin gum , tazo daf da Adnan Tace "Hello Mr Adnan" kana ta kauda Kai had'e da Murmushi Tace "Hello baby" "Mardiya kece?" Abdallah ke mata tambayar Nan cike da mamaki, tace "Eh nice kayi mamakin gani na ko?" "Ai dama na fad'a maka yarinyar Nan idan ta gani baza ta rufa Mana asiri ba" "ya Isa haka,ina yarinyar take?" DPO ya yi magana a tsawace . Adnan tun da ya gansu ya San Shikenan ya rasa Ayrah, shi ba hukuncin da za a Masa bane ma damuwar sa baya son rabuwa da ita, d'aya daga cikin Police din ne ya ture shi had'e da fad'in "wuce muje" jiki ba kwari ya Fara tafiya Yana tafiya biyu daga cikin polisawan Suna biye da shi sauran Kuma suna tsaye a waje, har da Mardiya aka Shiga ciki, har cikin d'akin da Ayrah take ya kaisu, Mardiya na hango kawarta ta saurinta ta ture Adnan ta nufi inda Ayrah ke kwance tana baccin ta hankalin ta a kwance. Kamar a mafarki ta ji Muryar Mardiya tana Kiran sunan ta, a hankali ta Fara waro Ido har idon ta ya bud'e duka ta tabbatar ba mafarki take ba, daga Chan nesa ta hango Adnan ya rakube a gefe Yana kallon ta daga shi sai vest sai boxer Yana kallon ta, idanun Sa sun canza daga launin fari suka koma jajir kamar zaiyi kuka. Kiran sunan ta da Mardiya tayi ne a karo na ba adadi ta ya dawo da tunanin ta gare ta, rugumar juna sukayi dukkanin su suna kuka. Basuyi wata wata ba suka sa masa handcuffs dashi da aminin sa Abdallah, Ayrah na ganin hakan ta yanke jiki ta fad'i. Haisam na kwance a d'akinsa dawowar sa kenan daga masallaci ya cire jallabiyar sa daga shi sai wando Wanda bai Kai gwiwarsa ba, ya Zo zai kwanta yaji ihu Kuma kamar Muryar isha, tsawaya yayi daga kwanciyar da yake son yi ya Kuma kin ihun ta tana Kiran sunan sa "Ya Haisam zan mutu" da gudu ya fita d'akinta ya fad'a, ya hango ta Akan gado tana mirginawa har tazo Fad'uwa yayi saurin tare ta kanta babu ko d'an kwali. Gashin kanta ya baje kamar wata mahaukaciya kuka take tana yarfa hannu had'e da rike Bayan ta a kid'ime yace "Princess mene ne, me ya same ki?" "Zan mutu Yaya, zan mutu bayana, Inna lillahi wa Inna ilaihirraji'un" "You're in labour princess" Blanket masu nauyi ya d'auko a Waldrop ya shimfid'a,Sau Kar da ita yayi a kasa yayi ganin ruwan ya fashe, ya gyara mata kwanciyar ta, bata kulawa ya farayi kasantuwar sa na likita, d'akinsa ya koma ya d'auko duk wani abunda zai bukata, ba wannan bane karo na farko ba da yake ganin mace a haka Amma bai San Meyasa hankalin sa ya tashi sosai ba, ko don Yana sontane oho. Duk wani abunda ya kamata ayi wa mace Mai haihuwa ya Mata, Yana d'an matsa Mata baya Yana Mata sannu had'e da fad'in "push princess" kusan awa d'aya suka d'auka a haka, gashi Umma bata gida dukkanin dasu Twins suna gidan Mummy, Abba da Daddy Kuma sunyi tafiya suna Germany sunje wani business trip, Mai aikin Kuma taje kasuwa don yi sayyaya. Wani nishi ta saki Mai d'an Kara , jariri ya Fad'o sai Jin kukan jaririn sukayi, wani ajiyar zuciya ya sauke shi zufa ita zufa, mikewa yayi ya gyara kwanciyar jaririn kana da taimakonsa mahaifa ya fito, Raba jaririn yayi da mahaifan, zanin ya sa ya nad'e jaririn a Kai kana ya kwantar Mata a kirjin ta, da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76