Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 25

Chapter 25

Dangin Ubana Book 1 Complete Hausa Novel 1,218 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

d'aura da fad'in "Yaya nane uwa d'aya uba d'aya muke dashi shi ya sha nono ya bar min kaga Kennan Ni Abban Ma'isha ne zanzo ka Kirani da Abba kamar yadda Isha take Kirana" Murmushi Haisam yayi yace "Insha Allah Abba" Daddy Har cikin ransa ya ji daddy, hakan zai tabbatarwa da Haisam ya zama d'an gida. Daddy yace "Daughter jeki ki Kira su Mummyn ku" Mikewa tayi had'e da fad'in to, tana Shiga d'akin da sallama ta Sanar dasu cewar daddy na Kiran su a tare suka fito, gaisawa suka Kuma yi Nan sukayi ta Hira tare yayin da Alhaji Abdallah sai Satan kallon Umma yake ta lura da hakan, hakan yasa duk take jinta wani iri, sai da karfe 11 tayi ya mike da zummar zai tafi daddy da mummy sukayi duk yanda sukayi suka sa ya Kwana. *TSOKACI* ```Shin wane ne Alhaji Mus'ab Aminu??``` Alhaji Mus'ab Aminu d'ane ga Alhaji Tahir Mus'ab da Hajiya Maryam Muhd, Tahir Mus'ab cikekken bafulatanin Gombe ne gaba da baya, shaharen Mai kud'i ne Wanda yayi suna a fad'in Nigeria suna da 'ya 'ya biyu dukka maza Mus'ab Wanda yaci sunan mahaifin sa sai kanin sa Abdallah sun taso cikin gata dukkanin su kuma sunyi karatu ne a kasan waje Sannan dukkanin su Business suka karanta, Bayan Mus'ab ya gama karatu a India ya dawo gida Nigeria, Bayan ya dawo ne ya da Yan kwanaki karayar arziki ya Kama mahaifinsa kasantuwar asarar da yayi zuciyar sa ta buga. Tun daga sannan mahaifiyar su ta kwanta rashin Lafiya yau da lafiya gobe ba lafiya a haka har ta shekara daga bisani ita ma ta rasu, da Taimakon Allah da na Mus'ab ya farfad'o da business d'in mahaifin nasu har ya samu Abdallah ma ya Zama mutum Shima ya fara business d'in. Tare suke koman su har suka samu sukayi aure, a Rana d'aya suka yi aure, Shi Mus'ab Yar Gombe ya samu ya aura Mai suna Maryam, shi Kuma Abdallah a yawon business d'insa ya had'u da fauziya, fauziya bahaushiyar kano ce, Bayan shekara biyu Fauziya ta haifi d'a na miji sai yayi wa Yayan sa Mus'ab takwara, Bayan shekaru uku ta haifi Yan biyu dukka mata wata hassana da Hussaina,daga Nan suka koma Kano da Zama sabida ya cigaba da lura da business d'insu na Kano d'in. Maryam hankalin ta kullum a tashe yake bata da wani buri da ya wuce ta samu ciki, kullum cikin kuka take Mus'ab shine Mai rarrashin ta. Cikin Muryar kuka Tace "Mus'ab Zaka rabu har dani ko? Ko Zaka karo min kishiya" Rungumeta yayi tsam a jikin sa yace "Bani da wacce ta fiki maryam, bazan tab'a miki kishiya ba insha Allah, kullum ina fad'a miki ki daina tada hankalin ki shi fa Haihuwar Nan na Allah ne" "Amma ai ganan Fauziya a Rana d'aya akayi auren mu yanzu yaran ta uku yanzu haka tana d'auke da cikin wata hud'u Ni ko 'batan wata ban tab'a yi ba, sama da shekaru 7" ta karasa maganar cikin kuka. Bubbuga Bayan ta yake yace "Amma ai ba dabarar ta bane Kuma kema ba laifin ki bane, tunda munsha zuwa asibito ci da dama har kasar waje munje duk zancen d'ayane dani dake duk bamu da matsala Kinga Kenan lokacin Haihuwar ne bata Zo ba, ki daina tada hankalin ki mu cigaba da addu'a" *AFTER 10 YEARS* Maryam ta tashi da zazzabi Mai zafi banda amai babu abinda take, cikiin tashin hankali ya kaita asibiti, Likita ya Sanar dashi labari Mai dad'in da ya dad'e yana son ji, farin ciki fal ransa ya Kira Abdallah ya Sanar dashi, dashi da Fauziya sunyi muran matuka, Bayan wata 9 Maryam ta sami yarta, yarinya kyakkyawa kama take sak da ubanta Amma da d'auki hasken fatar Maryam, kasantuwar Mus'ab ba wani haske yake dashi sosai ba. Abdallah najin labarin Haihuwar ya sa suka shirya dashi da matar da yaran sa hud'u , Mus'ab, hassana da Hussaina sai Autan su Faisal, Wanda a lokacin Mus'ab nada shekaru 10, Hassana sa Hussaina 8 years sai Faisal a lokacin bai cika shekaru 4. A Ranar suna Mus'ab ya Sanar musu da yarinya taci sunan mahaifiyar su wato Maryam Amma ana Kiran ta da Ma'isha, tun da sassafe suka shirya suka Kama hanyar Gombe a hanyar su ta zuwa gomben sukayi hatsari,Fauziya da 'ya'yan ta duk 4 suka rasu,yayin da Abdallah ya bugu sosai Yana kwance a asibiti Rai a hannun Allah. ________________________ Please comment and share Milhaat ce Yar Terawa 🍃*DANGIN UBANA*🍃 Story & Written By Milhaart Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne. *🌍MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION📚🖊* *M. W. A* ```Kungiya d'aya tamkar da dubu.Masu Nazari da Aiki da Ilimi, Burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma Nishad'antar da masoyan ta.🤙🏻``` https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa ____________________________________ *Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.* Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️ *BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM* Page 31&32 _Continuation........_ Tun daga Nan Abba yake kwance a asibiti, Rai A hannun Allah buguwar da yayi ne ya sa bai farka ba yayi dogon Suma, Satin sa d'aya a kwance. Su Fauziya Kuma da 'ya'yan ta tun a ranar aka kai su makwancin su, bayan ya farfad'o mutuwar tasu ta girgiza shi Kennan, tun daga Nan ya ji baya bukatar aure sabida gudun kar ya sake rasa su, hakan yasa ya bar kasan gaba ki d'aya ya Koma dubai, Yana kula da harkokin su na chan,sai lokaci zuwa lokaci yake zuwa duba su, Nan ma kwanaki biyu zuwa uku kawai yake musu ya koma,wani lokacin Kuma ya kwana hotel. Wannan Kenan. *CIGABAN LABARI* Abba ba don yaso ba ya Kwan,washe gari kuwa Ma'isha Bata sa Lectures a ranar akayi sa'a Haisam ma bayi da shi, a tare sukayi breakfast karfe 10 na safe flight d'in su Abba zai tashi. Bayan sun gama karyawa Abba yace dasu su fito waje akwai abinda zai nuna musu,Bayan sun fitane ya zaro key a aljihun sa ya mikawa Ma'isha, sa hannun tayi ta karb'a had'e da fad'in "Abba ajiye maka zanyi?" Yar karamar dariya yayi yace "A a My Isha,Taki Ce na Saya mikine sabida kokarin sa kike a school" Benz Ce baka sidik sai sheki yake wani uban ihu tayi had'e da salle,da gudu ta rungumi Abba had'e da yi Masa godiya "Abba Thank You Thank you" Shima rungumeta yayi Yana "fad'in mention Not Daughter, ki dai Kara kokari akan Wanda kike yi kinji?" Ta amsa da toh da gudu ta nufi gun Mummy tana nuna Mata,Duk sukayi Masa Godiya, Sannan suka koma cikin,Abba lokacin tafiyan sa ya kusa Amma bai ga Haisam da Umma ba,cike da kulawa yace "Yaya ya Banga sauran mutanen gidan ba?" "Eh suna part d'insu Amma yanzu nasan zasu Shigo" Aiko Yana rufe baki sai ga shigowar Haisam cike da girmawa ya gaidasu Duk suka amsa. Ma'isha da saurin ta Tace "Yaya ka gani Nima an Saya min mota babu ruwana da jiran ka bare ka jaa min ajii" Murmushi yayi yace "Masha Allah , congratulations gaskiya na tayi ki murna" Mikewa tayi Tace "Kazo muje kaga motar" wucewa tayi shi Kuma ya bi Bayan ta mummy girgiza Kai

Table of Contents

Chapters

76 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});