Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 10

Chapter 10

Dangin Ubana Book 1 Complete Hausa Novel 1,190 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

bane" Umma Tace "uhmm yaro yarone baza ki tab'a ganin abinda nake hangowa ba" Haisam yace "Umma Me hakan yake nufi, kina nufin akwai wata matsalane idan akayi hakan?" "babba ma kuwa Haisam, Baffan ka mutum ne Mai had'ari ni dukiyar Nan wallahi bataw dame ni ba , dama don kai ne nake so a karb'a maka hakkin ka, ina ji ajikina akwai abinda yake Shirin aikatawa" Ma'isha Tace "Insha Allah babu ma abin da zai faru Umma, aniyar shi ya bishi" Ta amsa da "Amin Allah ya shiga tsakanin mugu da na gari" duk suka amsa da Amin.Nan dai Haisam da Ma'isha sukayi ta kokarin jaan ta da Hira tun bata kulasu har aka fara hirar da ita. "Ka gani ko malam ai tun farko Haka nace maka kayi Amma kayi kunnen uwar shegu da ma baza a kai Nan ba" "Kinga Rabi ni bana son Mai maita magana, Allah ya kaddara hakan Sai ya Faru in ma maganar kulleni da akayi ne ai ba yau na fara shiga cikin cell ba so Dan Allah ki kyaleni naji da abinda yake damina ko Kuma na sauke 'bacin ran a Kan ki" Rabi na jin hakan ta shi ta fice daga d'akin ba tare da tace komai ba, binta yayi da kallo ya ja wani dogon tsaki. 'dakinta ta nufa tana Zama Kenan taji an turo kofa, kallon kofar tayi ganin irin kallon da take mata tayi kirkirerren Murmushi Tace "Ayra Shigo ciki mana" Wacce aka Kira da Ayra naga ta Shigo ta zauna a bakin gadon dake d'akin Tace "Mamy wai Dan Allah me ke faruwane, naga duk kina cikin tashin hankali, nasan hakan bazai rasa nasaba da Abinda ya faru da daddy bane ba, Dan Allah me daddy yayi har aka Kama shi" "Babu komai Ayra, ai daddyn naku ma ya dawo komai ya Riga ya wuce kar ki tashi hankalin ki" "Amma Kuma Mamy ke naki hankalin ai a tashe yake just in 2 days ki duba Kika yanda Kika rame Kika lalace" "Ayra kin San fa bana son ina magana Kuma kema kina yi sabida haka ko ki bar maganar Nan ko ki fice min daga d'aki bana son Shir........" "Me yasa baza ki fad'a mata ba, ai Ayra ba karamar yarinya bace ba, ta girma ya kamata ta San halin da ake ciki tunda baza ki iya sanar da ita ba Ni zan fad'a Mata" Wuri ya samu ya zauna, yace " Ayra" ta amsa da "Na'am Daddy" "Kin tuna cousin brother d'inki Haisam?" "Eh daddy d'an Uncle Ahmad" "Good" Nan ya shiga jero mata abubuwan da ya Faru shekarun baya kamo yanzu, Murmushin gefen baki tayi tace "Daddy wai dama suna Raye na d'aukan sun mutu fa" "Suna Nan a Raye" "To shi Alhaji Mus'ab d'in me had'in shi dasu da yake son taimakon su kalen dangi kawai" Mamy Tace "Na Allah Kenan ba, tun ba yau ba nake nuna wa mahaifin ki abinda yake ba dai dai bane ba, Yana ciyar damu da haram, sanan yana tufatar da mu da haram" "Haba Mamy so kike daddy ya kashe kansa da wanne zaiji? Ni daddy dama mu gudu mu bar kasan wallahi" Mamy yarfa hannu ta shigayi tayi tana sallalalami ta ce " Ayra Ashe baki da hankali ban sani ba? Kina nufin goyon bayan mahaifin ki zakiya bayan Kin San abubuwan da yake yi haramun ne, dukiyan maraya fa yake ci, nasan kinyi karatu kinsan kudin da mahaifin ki yake ci wutane Amma wallahi kin bani Mama....... " "Ke ke ke, me haka nace me haka? " Mikewa yayi ya nufe ta yace "So Kika kisa mata tsanata a ranta ko me kike nufi, wannan wani irin mumunar hud'uba kike Mata haka" "Amma malam kasan....." " Amma me, nace Amma me wallahi tallahi Rabi zan sab'a miki akan wannanw maganar wallahi daf kike da rasa auren ki" Mikewa itama tayi Tace " In rasa Mana ai auren Nan da shi da Babu duk d'aya" Cike da mamaki yace "Oh haka ma Kika ce ko?" "Eh Haka nace" "toh Shikenan kije ki na sak....." Ayra Tace "A'a daddy kayi hakuri Dan Allah, kar ka aikata, Dan Allah kar ka saki mamy" ta karasa maganar tana kuka. Tsaki yayi yace "Kinci Albarkacin Ayra, Allah ya miki Albarka Ayra" Ta amsa da amiin, yace "Naji dad'in maganganun ki hakan ne yake kara tabbatar min da cewar bazan wahala wurin d'aukar fansan da nake sonyi ba, Akwai aikin da nake so kimin, idan Kika min hakan na yafe Miki duniya da lahira." "Inshallah zan maka ko ma mene ne Daddy don samun albarkar ka" "Malam kar ka saka yarinyar Nan acikin matsalar ka ka fama Kai kad'ai" "a'a mummy mahaifina ne fa, matsalar da ai tawa ce, so kar ki damu" Murmushi daddy yayi yace "Good My Girl wuce muje kafun tayi poisoning mind d'inki" Ficewa sukayi a d'akin a tare suka bar ta ita kad'ai, Mamy ta rasa abinda yake mata dad'i, ajiyar zuciya tayi Tace "Ya Allah ka shirya min su ka ganar dasu gakiya." *BAYAN KWANA BIYU* Daddy na zaune a parlor shi da Haisam suna kallo suna Hira sama sama kasantuwar Yau lahadine yasa bai fita office ba, Mai gadi ya shigo bakinsa d'auke yake da sallama, suka amsa. Cikin girmamawa yace "Yallab'ai kayi baki" "Baki Kuma su wane ne Haka?" "Wai DPO ne da malam Hassan" "okay Ce musu su Shigo" " To yallab'ai" ya fice. Daddy yace "Son wai ina mutanen gidan Nan suke ne?" "Suna part din Umma" "Okay je ka Kira min su duka" Mikewa yayi tare da fad'in "to daddy." Tun daga bakin kofar parlor yake jiwo muryar su suna Hira suna dariya , da sallama ya shigo shima Yana daruyay duk da bai San dariyar me suke ba, yace "Nima nazo ne ayi hiran Dani" Umma tace "A'a you're not welcome here, yau ranar ta Mata ne" Yar karamar dariya yayi yace "Nikam dama nasan ba'a yina a gidan Nan Ma'isha kawai ake so" Ma'isha Tace "Ji Yaya fa dan Allah ni Kuma me ye nawa acikin maganar ku?" " Oh ma baki sani ba?" "Eh ban sani ba" "To ki taso Mana kawai ki shake min wuya na fad'a maki" Taso wa tayi ta nufe shi tana dariya yace "Ki karaso Nan kiga abinda zan Miki" Mummy Tace "Yaran Nan Basu da kunyan wallahi,Amma alhaji duk baya gani" Haisam yace "Laaa Kinga na Manta wallahi daddy ne ma ya aikoni wai nazo na Kira ku" Umma Tace " Kuma ka tsaya shirme ba" Mummy Tace "Lafiya dai ko? Nifa bana son irin Kiran Nan" Murmushin yayi Wanda ya kara bayyana kyawun fuskarsa yace "Lafiya Lau, Baffan hassane suka Zo" Dukkanin su Saida suka ji gaban su ya fad'i kallon juna Mummy da Umma sukayi a tare suka Mike suka fice a tare suka shiga dasu Malam Hassan. Mummy gefen daddy ta zauna yayin da Umma, Haisam da Ma'isha suka zauna a Kan three sitter dake d'akin DPO da Malam Hassan suka zauna a one one sitter dake kusa da su Daddy. Daddy yace "DPO shine kazo da kan ka? Ai da ka kirani zuwa office d'in" " A a y'allabai kasan an rufe case d'in Kuma

Table of Contents

Chapters

76 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});