Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 7

Chapter 7

Dangin Ubana Book 1 Complete Hausa Novel 1,213 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

mikewa Umma tayi had'e da Mika tana ambaton "La'ila ha illallalah Muhammaddar rasulullah" Ma'isha cikin muryar shagwa'ba tace "Umma zan biki mu kwana tare please" Murmushi tayi Tace "To Muje daughter" riko hannun ta tayi sukayi wa mummy Sai da safe suka fice, mummy Murmushi tayi ta girgiza Kai ta shige d'akin ta. WASHE GARI Bayan sun idar da sallar asuba Ma'isha ta dawo part d'in su, Kai tsaye d'akin ta tashiga ta yi wanka sannan ta fito don Taya mummy aiki a kitchen, Tana Shiga kitchen ta tarar da mummy juya ruwa a flask. "Mummy ina Good Morning" "Ahhhh 'yar Umma har Kun tashi?" Murmushi tayi Tace "Eh mummy" "To ya kuka tashi,ya Umman taku?" "Lafiya Lau Alhamdulillah" "Amma meyasa baki tsaya kin tayata aiki ba Kika dawo?" "Itace Tace na dawo, shiyasa Kuma Kinga , zamuje school, bara nayi wanke wanken" "A'a ki bari yarinyar nan zata Zo ta yi kije ki samu ki shirya naga har kinyi wanka je ki kawaii ki shirya" "mummy tun yanzu? Karfe 6 fa" "Ki dai sake dubawa 6:30 ne" Agogon bangon dake manne a kitchen d'in tace "Gaskiya lokaci yana gudu Bari naje na sa uniform" "Okay" Ta fice a kitchen d'in Bata d'auki lokaci mai tsawo ba ta dawo, a lokacin bakwai har ya wuce, a dining room ta tarar da mummy da Daddy bayan sun gaisa ta karya, a gaggauce ta fice tana musu sai ta dawo, inda ake parking mota ta nufa, ta tarar da driver da Haisam suna Hira cikin girmamawa ta gaida driver kana ta maida kallon ga Haisam tace "Good Morning Yaya" Murmushi yayi yace "Morning" Duk suka shige motar suka, ba su tsaya a ko ina ba sai makaranta. Haka rayuwa ta kasance wa ma'isha da Haisam a tare suke zuwa school Kuma su dawo a tare, sun shaku sosai haka ma mummy da Umma kusan komai tare suke, sannan daddy yana iya bakin kokarin sa wurin ganin ya cika alkwarin da ya d'auka wa Haisam, duk abunda yake so yanayi masa, a hakan har suka rubuta WAEC and NECO d'in su Kuma Alhamdulillah paper su duk yayi kyau. Daddy yayie matukar farin ciki hakan yasa bai 'bata lokaci ba wurin yi musu registration na JAMB ba,Kuma Alhamdulillah sun ci yanda a ke bukata duk su biyun a gombe state University sukayi(GSU) applying,suna zaman jiran admission. Da gudu ta shigo ta murna had'e da tsalle tana Kiran sunan Daddy da Mummy, Mummy dake kitchen ita da Umma cikin Sauri suka fito a tare sukace "Lafiya? Me ya faru?" Tambayar su yayi dai dai da lokacin da Daddy ya fito cikin Sauri daga d'akin sa, yace "Ma'isha me ya faru?" Sai tsalle take Haisam kusa hard'e hannu yayi Yana kallon ta, Umma Tace "Kai kunci gidan ku ana muku magana baza ku amsa ba?" Da gudu ta rungumi Umma tace "Admission ya fito kuma duk mun samu" Girgiza kai daddy yayi yace "Dad'i na dake ba a raba ki da shirme wallahi, shiyasa Kike Mana ihu a cikin gida?" " Daddy ai Dole ni da Yayana mun samu admission a department d'in da muke so" Umma Tace "Masha Allah, kice yanzu muna da Doctor da Kuma pharmacists a gida" Ta amsa da "Insha Allah" Mummy maida kallon ta tayo ga Haisam cike da kulawa Tace "Son ya naga Kai baka tsallen? Ko bakaji dad'in admission d'in bane?" "a'a mummy kawaiiii...... " Daddy ne ya katse shi yace "Toke Banda abunki hajiya Ma'isha tayi Shima yayi ya za a banbanta yaro da babba" Duk dariya sukayi, ya d'aura da fad'in "Allah ya taimaka, Haisam yaushe zaku karb'o admission d'in" " Ai daddy mun karb'o" "Sharp sharp Kenan, anyways congratulations to you both" A tare Ma'isha da Haisam suka amsa da "Thank you daddy." "Emmm yanzu abunda za'ayi ku biyuni sai muyi maganar kud'in registration d'in don Ina so a Fara Lectures daku" ya wuce d'akin sa su biyun suka bi bayan sa mummy da Umma Kuma suka koma kitchen. Daddy ya Basu dukkanin kud'in da suke bukata,washe gari a tare sukaje sukayi registration tun safe suka fita basu dawo har sai dab da magrib a gajiye suka dawo,hakan yasa dawuri sukayi bacci. Bayan sun gama registration,suka Fara Lectures d'insu yanda ya kamata. Daddy na gani zaune a office, kwankwasa kofar da akayi ne yasa ya d'ago kansa yace "Come in" sannan ya cigaba da rubuce rubucen da yake, Jin an shigo ya d'ago kansa don ganin Wanda ya shigo Murmushi yayi yace "Bismillah zauna" Ba musu mutumin ya zauna, hannu ya Mika Masa suka gaisa, mutumin ne ya ce "naji Labari kaje gida har Sau Uku baka sameni ba, gashi kuma ban Sanka ba" "eh hakane kamar yanda nace maka a waya wata magana nake so muyi da Kai Mai muhimmanci, shiyasa ma kaga na takura kazo office Dina" Murmushi yayi ya gyara Zama yace "Business ne Kennan, kasan na dad'e ina so na fara business da company ku Amma Allah baiyi ba" Daddy yace "Malam Hassan zamu Zo Nan d'in ma Amma kamun Nan....." Wayarsa ya zaro a aljihun gaban rigar sa gallery ya shiga ya Mika Masa wayan yace "ko Kasan wannan?" Karb'an wayan yayi ya dad'e Yana kallon sa, a zuciyar sa yace "Wannan kamar Haisam, Kai ba shi bane ya akayi ya Zama Haka maybe kamane" A bayyane Kuma yace "Yallab'ai ban sanshi ba Gaskiya" ya Mika Masa wayan, Kan wani hoto ya koma ya Kuma Mika Masa wayan yace "Wannnar fa da fatan ka gane ta?" Yana karb'an wayan yana ganin Hoton a raza ya Mike hannun sa rawa yace "Zainab, wannan kamar Zainab dama tana raye ne, Zainab ce fa matar Yayana ko? Ko dai Kama ne ya naga ta canza?" _______________________ Please share and comments Milhat ce Yar Terawa 🍃 *DANGIN UBANA*🍃 Story & Written By Milhaart Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne. *🌍MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION📚🖊* *M. W. A* ```Kungiya d'aya tamkar da dubu.Masu Nazari da Aiki da Ilimi, Burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma Nishad'antar da masoyan ta.🤙🏻``` https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa ____________________________________ *Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.* Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️ *BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM* Page 11 and 12 Daddy Shima mikewa yayi yace "hakan na nufin ka santa Kenan?" Malam Hassan Sai kallon sa yake ya kasa cewa komai, girgiza Kai daddy yace "calm down, calm down ka zauna" Jiki a sanyaye ya zauna Idon sa akan hoton Sai zare Ido yake Yana kallon Hoton, daddy yace "Na dad'e ina neman ka tsoratan da kayi hakan ya tabbatar min da maganar da Zainab ta fad'a min Akan ka gaskiya ce" Murya na rawa yace "me me me ta taa fad'a maka? Kar ka yarda da ita makaryaciya ce" "Give a good reason da zan gano cewar makaryaciya ce" "Ashe dama tana raye ni na d'auka ta mutu" Maganar da yake ta maimaitawa Kenan. Daddy yace "Bata mutu ba,ko ince Basu mutu ba,Ashe dama Kaine Wanda yasa aka Kona musu gida ina da labarin gidan ya Kama da wuta nayi iya tunanin Duniyar Nan ya akayi wuta ya Kama,ashe Kaine?" Mika Masa

Table of Contents

Chapters

76 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});