Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 51

Chapter 51

Dangin Ubana Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

basu amsa key d'in motar ta fizge daga hannun Mardiya ta fad'a cikin motar baki a bud'e Duk suka tsaya kallon ta, ganin ta tada motar Kuma tana niyar tafiyane sukayiw saurin Shiga motar su ma. Suna Shiga ta fizgi motar da wani mugun speed. "oyoyo oyoyo Yarana" da gudu suka nufi inda mummy take suka rungume ta , Zama sukayi, Mummy kallon sa tayo Tace "Haba Auta baza kamin magana ba?" Turo baki yayi kana yace "Ai ni bakya Sona Su Sister Aymana da Aima kawai kike so" "Kai ma ina sonka nama fi sonka Akan kowa, kazo muje na baka chacolate" Jin an ambaci sunan chacolate da gudu ya nufi inda take, hannun sa ta rike, d'akin ta suka shiga Aymana da Aima na biye da su chacolate da Biscuits ta Basu kana suka fito, Channel ta Canza musu Tasa Nicklodeon suna ganin favorite channel d'insu ki wannen su ya samu gu ya zauna suka cigaba da kallon su. Mummy ganin Umma tayi shiru hakan yasa tace "Umman Yara lafiya dai ko? Ya na ganki haka?" Cike da kulawa take tambayar ta. Gyara Zama Umma tayi kana Tace "Uhmn Mummy Yara ina cikin damuwa Wallahi" "Sanar dani mene ne kuma ya faru?" "Yarinyar Nan Ce tazo har gida wajen Daughter" " Wace yarinya Kenan?" Mummy ta tambaya cikin rashin fahimta. Umma Tace "Aurajy Yar gidan malam Hassan" Zaro Ido mummy tayi tace "Ayrah kuma tare da Isha? Amma kin tabbata ita d'in ce?" "Kwarai kuwa ga Nan kamannin uwarta na gane ta" "Allahumma ajirni fii musibati, to ita Ma'isha me ya had'a ta da tsinanniyar yarinyar Nan? " "Allahu a'alam na biyo tane don naji dalilin zuwan ta har gida ta same ta, a ina take nema banji motsin ta?" "Ha'aa ai na d'auka suna chan sabida ba ta dawo ba" "Ikon Allah ko ta wuce asibiti ne?" "Anya yau ai tana off" "Shikenan Duk inda taje zata dawo ta same ni inji dalilin ta na magana da shaid'aniyar yarinyar Nan, da har zata zauna inuwa d'aya da ita" tana maganar cikin tsananin 'bacin Rai. Umma Kam kasa magana tayi, don ta ma rasa abinda zatace. "Rabi Anya kina tsoron Allah kuwa? Anya kina so ki Gama da duniya Lafiya kuwa? Shin kina son Shiga aljanna kuwa? Karfa ki manta cewar aljannar ki a karkashin kafata yake, Wallahi sai in take ta muga yanda zakiyi" "Mtsww kaga malam Dan Allah Kar ka Dame ni kaji ko kazo ka tsaya akaina kana damina da surutu" Nuna kansa yayi cike da mamaki yace "Ni Rabi? Ni malam Hassan kike fad'awa haka? Kar ki manta fa ni mijin ki ne" "Kai ka sani don ni Wallahi na dad'e da daina kallon ka a matsayin mijina idan kana son kwanciyar hankalin ka a gidan Nan ka sauwake min na tafi gidan mu" "Na fad'a miki bazan sake ki ba, Wallahi ko mutuwa zakiyi bazan rabu dake ba in ko Kika bar gidan nan to ki sani ban yafe miki ba, Wai ma shin kin San hukuncin Matar da ta nemi Mijinta ya sake ta kuwa?" "Ayyirriiiiiii har Kai ka Isa ka nuna min sanin Allah me ka sani a game da adddin ka, da ka sani baza ka Rika aikata abubuwan da kake ba" "Oh kina nufin ni jahiline Kenan ko?" "To me banbancin?" "Oho Wannan Kuma kai ta shafa, Dan Allah idan ka gama ka fice min daga d'aki" "Naji zan fita Amma ina bukatar ki yau a turaka ta" "Allah ya sauwake na had'a jikina da naka, a Bayan ma ban San abinda kake aikatawa bane yasa na saki jikina da kai" Kasa kasa yayi da murya yace "Rabi kiji tsoron Allah tun lokacin da yaron Nan ya Shiga comma kika kaurace min, ya kike so nayi ne Dan Allah Kar ki manta Ina da hakki fa Akan ki" "Kaje chan inda aka saba baka karb'a idan Kuma kaji haushi Kaje ka kara Aure mtsww" ta cigaba da kallon da take, kallon ta ya tsaya yi kana yace "Zanyi maganin ki dani kike zancen" Yana kaina ya fita. Da d'an karfi Tace "Do your worse, d'an halak ka fasa, tasan yaji abinda tace Amma yayi kamar bai ji ta ba, fita yayi daga gidan gaba ki d'aya Bai Kai awa d'aya ba ya Dawo tare da wata yarinya wacce baza ta wuce sa'ar Ayrah ba, a lokacin Mamy ta fito parlor Suna Kallo da ita da Nabila, Faisal da Sunusi kannen Ayrah. Malam hassan har cikin parlor suka Shiga da yarinyar , Mamy ko kallon inda suke batayi ba bare ya dame ta, Nabila ce tabi su da Kallo har suka haura sama sai da suka Shiga d'aki Nabila tace "Mamy Wace ce wanchan suka shigo tare suka da daddy?" "Kije ki tambaye shi mana, ba uban ki bane" Faisal yace "A gaskiya Mamy Wannan cin fuskan yayi yawa, har cikin gida daddy ya fara kawo Yan matan sa Bayan maganganun da muke ji a unguwa yana zubar Mana da mutunci Mana" (Yaran Malam Hassan guda hud'u ne, Ayrah sai Nabila da take binta sai Faisal sannan karamin cikin su Sunusi). Kallon su kawai Mamy take batace musu komai ba, Nabila Tace "Mamy Yanzu Dan Allah haka zamu zubawa baba Ido yana abinda ya ga Dama a gidan nan?" "Nabila!!! Nabila!!! Nabila!!! Sau nawa na Kira sunan ki?" Kai a kasa Tace "Sau uku Mamy" "Good idan Kika sake min maganar uban ku Wallahi tallahi sai na miki baki, ba ke Kad'ai ba har daku" ta karasa maganar tana nuna Faisal da Sunusi. Mikewa tayi ta shige d'akin ta, kallon juna su sukayi sannan ko wanne su ya Shiga taitayin sa. Isha gudu take sosai, tana driving d'inne ta Sanar musu da cewar Haisam ya farka. _________________________ Please comment and Vote Milhaat Ce Yar Terawa [7/13, 8:42 PM] Miilhaat: 🍃 *DANGIN UBANA*🍃 Story & Written By Milhart Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne. *🌍MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION📚🖊* *M. W. A* *Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.* Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️ *BISMILLAHIR RAHAMANIN RAHIM* Page 55&56 _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._ ```Continuation........``` Su Ma'isha na Isa asibitin fita tayi ba tare da ta kashe motar ba, gudu take sosai har ta isa

Table of Contents

Chapters

76 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});