Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 65

Chapter 65

Dangin Ubana Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

masa komai ba,murmusawa ya kumayi kana yace "Am sorry Ayrah babu yanda zanyine,sabida Ina son ki Ina so na kasance Dake na har a bada,idan kin amince wallahi zan aure ki kuma na miki alkawari daga yau bazan sake kusantar ki ba har sai na mallake ki a matsayin matata ta sunnah." Mikewa tayi Tace "Bayan abubuwan da kamin Adnan? I won't fall for your lies anymore, ka cuce ni, ka wulakanta Ni, yanzu Kuma kazo kana gaya min maganar banza maganar wufi" ta karasa maganar tana kuka Mai tsuma zuciyar Mai sauraron. Ledan da ya shigo dashi ya ajiye, har kasa ya durkusa ya hard'e Hannayen sa alamun roko, hawayene suke gangarowa daga idanun sa Zuwa kuncin sa, cike da mamaki take kallon sa, cikin sarkewar murya yake fad'in "Dan Allah Ayrah, Kar ki min haka kiji tausayina Wallahi ina sonki Kuma Ina kaunar ki, bazan iya Rayuwa babu ke ba Ayrah" Tunda ya Fara maganar take kallon sa cike da mamaki, ji take kamar ta shake Masa wuya ya mutu. "Kana Sona kace?" Cikin sanyin Murya take magana. "eh Wallahi , ina sonki sosai fiye da tunaniin Mai tunanina" "Hmm to ina so ka bud'e kunnuwan da kyau kaji abinda zan Fad'a maka yanzu" magana take in a serious tune, ganin hakan ya mike ya tsaya da kafafun sa, Duk Jikin sa yayi sanyi. Matsowa kusa da shi tayi,har suna iya jin numfashi junan su, cikin Murya Mai d'an karfi Tace "Ni Ayrah Hassan na tsane ka, na tsane ka kuma bazan tab'a son ka ba" Yace "Ni Kuma ina sonki ina sonki Kuma bazan tab'a daina son ki ba" " Ohh haka kace? Haka kace?" Cikin d'aga Murya yace "Eh haka nace" "To tabbas nice ajalin ka Adnan" Murmushi yayi kana yace "Da nafi kowa Farin ciki idan Kika kashe Ni" Wani abu taji ya tokare ta a kirji, Bata Jin dad'in yanda Sam bai da mu da maganganun da take Masa ba, tsaki tayi ta shige d'akin ta. Kallon ta ya tsaya yi har ta shige d'akin, a bayyane yace "Wallahi sai na sace zuciyar ki kamar yadda nayi a baya." Kofan d'akin ta ya nufa ya tura a hankali ya hango ta zaune Akan gado tana aikin kuka, ji yayi ba dad'i, ledan hannun sa ya ajiye Mata ya fita gaba ki d'aya daga gidan. Alhamdulillah Haisam na samun sauki sosai don har ya Fara takawa, maganar sa Kuma ya Dawo normal, Duk da wasu kalmomin idan ya furta su kamar yaro. Wata Rana, Yana kwance a Kan gadon jinyar sa, Isha Kuma na zaune a gefen sa a Kan plastic chair kallon ta yake yayin da ita Kuma hankalin ta na Kan wayan ta. Muryar sa taji ya kira sunan da ya saba kiran ta dashi "Princess!!!" Ajiye wayar hannun ta tayi tace "Akwai abinda kake bukata ne?" Ta mike tana kallon sa shima kallon ta yake, da ta lura da yana kallon cikin ta, itama kallon cikin natan tayi Wanda a yanzu Yana cikin wata hud'u, ya Fara fitowa, da sauri ta koma ta zauna. Murmushi yayi kana yace "Princess Fad'a min abubwan da nayi missing Bayan na Shiga comma" Wasa ta shigayi da hannun ta kana ta Fara fad'in Duk abubuwan da ya faru, Kama daga yanda ya Shiga comma har aka Kawo shi asibiti, da shekarun da ya d'eba Yana kwance, Sannan ta Fad'a Masa tayi aure Amma Bata shekara ba mijinta ya rasu, sannan ta Fad'a Masa halin da Malam Hassan ke ciki da 'batan Ayrah. Ta karasa bashi labarin tana matsar kwalla, hankalin sa yayi mugun tashi Jin abubuwan da ya faru bayan kwanciyar sa, cike da jin tausayin ta yace "Yanzu ciki kike dashi?" Kai a kasa Tace "Eh" Ajiyar zuciya yayi kana yace "Allah ya raba lafiya" Ta amsa da amiin. Yace "ban San meyasa Baffana ya tsane ni ba , Bayan ya kashe min Uba Nima ya so ya hallaka ni, sunyi wasa da zuciya ta shi da Ayrah na kudiri aniyar d'aukan fansar abinda suka min Amma jin kaddarar da ta same su na tsinci kaina ina matukar tausaya musu, yanzu abinda yafi damuna shine Ina Ayrah take?" "An bin cika ta ko ina Amma ba labari, gidan TV da gidan radio Duk ansa cigiya Amma shiru" " Allah ya Kare ta" "amiin" " Amma ya Jikin Malam Hassan d'in?" "I don't know gaskiya but Yana nan a asibitin nan" "really tashi ki rakani" " A a Ya Haisam, babu inda zaka ce a haka Kar ka manta fa ba cikekken Lafiya gare ka ba, tunda haryanzu kafar ka na rawa, by the way meyasa ma zaka damu da wa'annan mutanen Bayan irin abubuwan da suka maka?" " It's simple...... " Mike Yana Mai gyara jallabiyar sa, ya d'aura da fad'in "They are my Family Princess, ai ba'a Canza wa tuwo suna" kallon sa ta tsaya yi tana tunaniin irin hali irin na Haisam ace Duk abubuwan da suka masa Amma ya damu dasu, ganin bata da niyar magana yace "Muje ko?" Ba don ta so ba, ta Mike tayi gaba yana biye da ita, girgiza kai yayi. Ward d'in da Malam Hassan yake suka nufa, kofan Isha ta tura had'e da yin sallama kasantuwar, uniform ne na asibiti a jikinta hakan yasa suka d'auka tazo Duba shi ne, Mamy na ganin Haisam biye da ita ta Mike tana kallon sa, shima kallon ta yake don bazai tab'a manta fuskar ta ba, sabida ta kasance tana nuna Masa so da Kauna tun Yana yaro ba kamar yadda Baffan nasa yake ba, Murya na rawa Idanun ta fal da hawaye Tace "Hai......sam!!" Malam Hassan da ke kwace Yana fuskantar bango yaji an Kira sunan Haisam ya juyo a hankali, yayin da Nabila ita ma ta Mike tana kallon sa, sabida ita Sam bata tab'a ganin d'an uwan nata ba. _________________________ Please comment & vote Milhat ce Yar Terawa [8/13, 8:26 PM] Miilhaat Writer✍🏻: 🍃 *DANGIN UBANA*🍃 Story & Written By Milhart Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne. *🌍MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION📚🖊* *M. W. A* *Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.* Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️ *BISMILLAHIR RAHAMANIN RAHIM* Page 69&70 _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._ ```Continuation......``` Murmushi Haisam

Table of Contents

Chapters

76 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});