Chapter 18
Chapter 18
a, to Shima dai d'an uwan soyayyar ne, amma taya za'ayi nayi soyayya da Kanwata?" Cikee da farin ciki tace " Au dama kanwar kace? " "Eh kanwatace da me Kika d'auka?" "Na d'auka budurwar ka ce" "To ki ajiye Kanwata ce,ai Ni bank da budurwa ban ma tab'a soyayya ba" "Na dai ji ban yarda ba" "Allah kuwa trust me ba wasa nake Miki ba,sai dai idan ke zaki nema min Yanzu" "A a idan Kuma na nema maka waccce Bata maka ba Kuma fa?" "Zata ma yi insha Allahu" "To Insha Allah zan nema maka waccce zata dace da kai" "Da kuwa naji dad'i sosai" Nan sukayi ta hirar su kusan na mintuna 20 kana ta Masa sai da safe suka sauke wayar a tare, kwanciyar ta tayi yayin da Haisam ya cigaba da abinda yake yi. ________________________ Ba na ganin comment d'inku Please kuyi sharhi sannan kuyi sharing. Taku a kullum Milhat Yar Terawa 🍃 *DANGIN UBANA*🍃 Story & Written By Milhaart Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne. *🌍MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION📚🖊* *M. W. A* ```Kungiya d'aya tamkar da dubu.Masu Nazari da Aiki da Ilimi, Burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma Nishad'antar da masoyan ta.🤙🏻``` https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa ____________________________________ *Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.* Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️ *BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM* Page 23&24 *...............WASHE GARI* Kamar kullum a tare suka shiga school tun karfe 7 na safe, Yau Haisam ya Riga Ma'isha Gama lectures hakan yasa ya zauna zaman jiranta a Mango garden na cikin School. Kiran Aysha ne ya Shigo wayar sa, picking yayi da sallama daga d'ayan 'bangaren ta amsa da "Wa'alaikassalam yallab'ai kana lafiya?" "Ina lafiya ke fa?" "Nima haka" "Masha Allah ka Shigo kuwa?" "Eh na Shigo" "Ok please kana ina ne nazo na same ka" "Ina mango garden" "Okay muna kusa ma gani Nan karasowa" Ya Masa da " okay" ya kashe wayan. Girgiza Kai Aysha tayi Tace "Qawata Kinga bawan Allan Nan, Yana da wani habit d'in da bana so wallahi" "Me Kenan fa?" "Bai tab'a Kirana ba tunda Amma idan na kirasa shi yake fara cutting call d'in which is very bad" ta karasa maganar kamar zatayi kuka. Mardiya Tace "It's not a big deal qawata tunda in Kika kirasa yana d'agawa Kuma yana sauraron ki ai Shikenan Kuma Nan gaba da kansa zai Rika neman ki" Huci tayi tace "Shikenan tunda kince Haka shiyasa a ko wani lokaci idan ina bukatar shawara Kai tsaye ke nake nema nasan zan samu solution" " I will always be here for you Qawata,yanzu dai tashi kije ki same shi before it's too late" Aysha tace "I thought tare zamu" "A a kaaai, kamata ai daga ke sai shi zaki fi fahimta" ta kashe mata Ido d'aya,duka Aysha ta Kai Mata ta kauce. Mikewa tayi ta Masa sai anjimu da jaddada mata idan ta gama zata kirata sai su koma gidan tare,tayi tafiyar ta, ba d'au lokaci mai tsawo ba kasantuwar LT d'in da take da mango garden ba nisa hakan yasa tayi saurin Isa inda yake. Da sallama ta karasa inda yake bayan sun gama gaisawa Nan ya mata umarnin da ta fito da handouts d'inta, Nan ya zari d'aya ya Fara mata tutorial d'in sunfi awa d'aya yana mata, Amma fa hankalin sa na Kan wayarsa minti minti yake dubawa daga bisani Tace "Akwai abinda kake jirane? Naga sai faman duba time kake" "Hmmm eh, Time nake dubawa kar princess tayi ta jirana karfe 3 zata gama lectures" Tab'e baki tayi Tace "Wai dole Kai Zaka kaita gida ne?" "Eh Mana to wa zai kaita in bani ba?" Ganin yanayin sa ya canza tayi saurin fad'in "Lallai kana ji da ita sosai Naga karfe 2 yanzu da sauran time ai" Yace "Eh gashi wayata ta kusa d'aukewa ba chaji Kuma na baro cable a gida Dana saka a mota, kar ta Kira bata same Ni ba" Ta amsa da "Hakane" Yace "Anyways mu cigaba ko?" Ta amsa da "Toh" Nan ya cigaba da Mata tutorial d'in, ganin hankalinsa yayi nisa a abinda yake koya Mata tasa hannu ta kashe wayar tasa sannan ta maida ta ajiye. Sun dad'e a zaune a gun ya d'auki wayar sa ya Danna yaga a kashe tsaki yayi yace "Damn it!!!" Tace "Lafiya kuwa?" Yar karamar tsaki yayi yace "Wayar ta d'auke" "In time ne bari na duba maka a wayata" Yace "Yauwa please duba min." Aysha na duba time taga karfe 3 da kwata Tace Masa "2:30" Zaro Ido yayi yace "Wai tun d'azun Nan 30 mints kawai mukayi?" Tace "Eh" "Lallai time baya gudu" "Ko dai ka gajine? Mu bari sai gobe?" "A a kar ki damu mu cigaba kawai." Murmushin kyeta tayi ba tace Masa komai ba ya d'aura daga inda ya tsaya. Ma'isha tafi minti 20 tana jiran sa, Kiran wayarsa take Amma switch off sai ta tuna tana da Number Farukh ta shiga dialling har kusa yankewa ya d'auka cikin Muryar ta mai dad'in sauraro Tace "Ya Farukh ina wuni?" Ya amsa da "Lafiya" cikin Muryar bacci, Tace "Am sorry kana bacci na tashe ka ko?" Yace "Eh wallah but kar ki damu ya akayi?" "Dama na d'auka kuna tare da Yayana ne" "A'a mun rabu tun d'azu da mukayi sallar azahar but yace min zaiyi wa Aysha tutorail but ki kirasa ki ji" "Uhmn number a kashe, Amma Bakomai nagode sai anjima" ta katse wayar tayi ba tare da ta ji amsar sa ba. Girgiza kai yayi yace "kishi kumallon Mata, Amma guy d'in nan don ya raina min hankali yace min ba Soyayya suke da Ma'isha ba mtss" ajiye wayar yayi ya koma baccin sa, Ma'isha kuwa Mango garden ta nufa dake tasan wurin zaman sa Kenan yawanci. Tun daga nesa ta hango su suna zaune dai dai lokacin da Aysha take dariyan sunan wani scientist da ya fad'a dariya take sosai Shima ya fara taya ta a Fili Tace "Tutorial d'in kenan" har ta nufi inda suke sai Kuma ta Canza shawara ta koma, gate na makarantar ta nufa tana fita ta tari napep ta wuce gida, ita kanta taji ta wani iri sabida shine karo na farko da ta shiga napep sannan shine karo na farko data Koma gida ba tare da Yayan ta ba. Kiran sallah da akayi ne Haisam ya Mike a zabure Aysha ma mikewa tayi tace "Lafiya?" "Kamar kiran sallah fa nake ji?" "Eh Kiran sallah ne" Ajiye Mata handout d'in yayi da saurin ya bar gun ba tare da yace mata komai ba, baki bta bud'e ta tsaya kallon sa har ta daina ganin sa bata bar mamaki ba, wa'anda suke zaune a gefen su Kuma suka tsaya kallon ta, tsaki tayi ta wurga musu harara da sauri suka kau da kansu Tace "magulmatan banza kawai Mtssw" ta d'auki Jakarta da handout d'in da Haisam ya ajiye ta bar gun. Ma'isha na Isa gida ta tarar da su Mummy suna part d'insu Umma, hamdallah tayi ta shiga d'akin ta wanka ta fara yi ta d'auro alwala bayan ta idar da sallah ta kulle kofar d'akin ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76