Chapter 20
Chapter 20
you Yar daddy, I trust you shiyasa na saki wannan aikin sabida nasan Zaki iya but mind you kibi a hankali kar kaikayi ya koma Kan mashekiya" "hahaha insha Allah ba za'ayi hakan ba daddy your girl is very smart" "Allah ya dafa Miki" "Ameen daddy nagode, Ina tsarabata?" "Yana Nan Zo muje ki karb'a" Cike da murna ta Mike ta bi bayan sa. Bayan ta karb'o ledan da ya Mika ma ta ta nufo d'akin ta, ji tayi an Kira sunanta cikin sauri ta juya don ganin Wacce ke kiranta ganin mahaifiyar Tace tayi Murmushi Tace "Na'am Mamy" "Zonan ina da magana dake" tana Kai Nan ta shige d'akin ta Ayra ma tabi bayanta. __________________________ Please comment sharhi, ku duba yawan typing da nayi Amma wasu thanks kawai nake Samu please kuyi min sharri sannan kumin sharing. Milhaat ce Yar Terawa _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._ *DANGIN UBANA*🍃 Story & Written By Milhaart Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne. *🌍MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION📚🖊* *M. W. A* ```Kungiya d'aya tamkar da dubu.Masu Nazari da Aiki da Ilimi, Burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma Nishad'antar da masoyan ta.🤙🏻``` https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa ____________________________________ *Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.* Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️ *BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM* Page 25&26 ..................Da gudu tabi bayansa , ya nufi part d'insu da gudu ta Sha gaban sa "Yaya Dan Allah ka saurare Ni" Kallon ta ya tsaya yi kamar zai tanka mata sai Kuma ya kauce ya Shiga cikin gida da sauri, d'akin sa ya nufa Yana Shiga ya sa key ya rufe kofar Yana ji tana Kiran sunan sa had'e da bubbuga kofar tana fad'in "Yaya Dan Allah kayi hakuri wallahi kuskure aka Samu, bazan sake ba" Umma jin Karan buga kofa ta fito daga kitchen cikin sauri hannun ta d'auke da cokalin Miya alama tana girki ne, kofar d'akin Haisam ta nufa ganin Ma'isha na bubbuga kofar tana kuka Tace "Daughter lafiya? Ina Kika Shiga ne Kika tada Mana hankali iye?" Cikin kuka tana share hawayen da ke sauka a kuncin ta Tace "Umma ina Nan fa tun d'azu" "Ban gane kina Nan tun d'azu ba, bayan Haisam shi kad'ai ya dawo Kuma yana neman ki, hankalin mu ya tashi sosai sabida a tare kuka Saba dawo wa" "Umma da na gama lectures nazo inda yake ajiye motar sa, nayi ta jiran sa ban gan sa ba, Kuma na Kira layin sa a kashe a tunani na wani abun yake na shiga neman sa kawai sai na ganshi da wata suna hi....... " kukane yaci karfinta ta kasa karasa maganar dake bakin ta. Umma ruko hannun ta tayi suka dawo parlor,zaunar da ita tayi ta sa ta a gaba tana kallon ta , ita ko Ma'isha kukan ta to ta Rai rawa "lallai abinda nake zargi ya tabbata Soyayya ce a tsakanin yaran Nan tunda gashi har kishi take" zancen zuci take A bayyane Kuma gyaran murya tayi Tace "Daughter ki daina kuka wa ya gaya miki ana wa na miji kuka kiyo shiru ki daina kuka sai ya raina ki,kuma ma naga ai shi ya Miki laifi so shi ya kamata ya baki hakuri ba ke ba." Cikin shesshekar kuka Tace "A'a umma Ni na Masa laifi, da ban jira shi ya gama abinda yake ba, ni nayi tunanin kashe wayar sa yayi Ashe ba chajine, Kuma ku ma na tada muku hankali Dan Allah kuyi hakuri" ta karasa maganar tana kuka Mai tsuma zuciya. " Yi shiru daughter yi shiru tunda kin dawo ai Shikenan, duk tunanin mu wani abun ne ya same ki har shi kanshi Haisam d'in ya damu don yafi kowa ma damuwa 'bacin Raine kawai Amma zai huce ki daina kukan haka, zo muje kitchen ki tayani aiki." Riko hannun ta Umma tayi suka nufi kitchen, Nan ta Fara Taya ta wanke wanke da sauran abubuwan da ya dace. Haisam kuwa tunda ya Shiga cikin d'akinsa ban d'aki ya fad'a ya kunnawa kansa shower ba tare da ya cire kayan jikinsa ba, tsantsan 'bacin Rai da Jin haushin abinda tayine ya sa shi hakan, sannan ya kunna shower d'in ne don kar yaji kukanta, sabida bazai iya jure Jin kukan ta ba, Dole ne ya horata. "Ayra kiji tsoron Allah ki fad'a min abinda kuke shiryawa da mahaifinki, Ayra Ina guje miki abinda zai je ya dawo" "Uhmn Umma Kenan Amma kin San Daddy bazaiyi abinda zai cutar dani bako?" "Hakane nasan da hakan Amma ina so ki fad'a min abinda kuke shiryawa" "Mamy kiyi hakuri bazan iya fad'a miki ba , sabida daddy fa gargad'i yamin akan kar na kuskura na sanar da kowa Shirin mu" " Amma ai ni uwarkice ina da hakki Akan ki" "Shima Kuma yana dashi a kaina, please Umma ki fita daga cikin maganar nan, daddy yaki fad'a miki ne sabida yasan baza ki bada had'in Kai akai ba" " Hakan shi zai tabbatar da tsiya kuke Shirin aikatawa, ina so duk abinda zakiyi a rayuwar ki sa tsoron Allah a zuciyar Ayrah, shifa rayuwar Nan gajera ce, mahaifin ki bazai tab'a fahimtan hakan ba sabida shi na mijine ciwon 'ya mace na 'ya mace ne" Mikewa Ayrah tayi tare da fad'in "Kar ki damu Mamy nasan Kina Sona Baki son abinda zai cutar dani insha Allah Babu abinda zai sameni" "Ayrah Ni ba take nake ba, in tunanin abinda kuke Shirin aikatawa nee, Kar ki manta Haisam d'an uwan kine mahaifiyar sa Kuma kamar uwa take a gare ki, kamata ai idan Kika ga wani zai cutar dasu ki Kare su Amma ke da kanki?" Dafe kanta tayi Tace "Ya Rasullullah, Mamy wai wa yace miki cutar dasu zamuyi after all haryanzu ban shirya abinda nake sonyi ba, amma wallahi sai ya d'an d'ana kud'ar sa na wulakanta min mahaifi da yayi" tana Kai Nan ta d'auki ledar ta da ta Shigo dashi ta fice daga d'akin. Mamy Tace "Allah kana gani nayie iya bakin kokari na wajen ganar dasu Kuma sunki saurarata Allah ga bawan ka Nan Haisam bawan Allah da mahaifiyar sa ka kare su daga sharrin su, sannan ka Kare Musulmi a duk inda yake, ya Allah ka Shiga tsakanin mugu da na gari" Ni ko
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76