Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 31

Chapter 31

Dangin Ubana Book 1 Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kamar rarrashi yace "Umma please, Dan Allah ki duba lamarin nan" "Haisam Kenan, haryanzu baka fahimce ni ba Sam, bazan iya auran wani ba Bayan mahaifin ka zan cigaba da Zama haka har nima mutuwa ta riske Ni" "Umma ki dubi girman Allah ki sake tunani a Kai, kar ki manta fa Daddy shi ya taimaka mans muka fita daga cikin kuncin Rayuwa har muka dawo Mutane, kin San abubuwan da bazan iya lissafa su ba, yau yana neman abu a wurin Wanda zamu iya bashi Kuma mu hana shi, Idan mukayi hakan ba muyi Masa butulci ba kuwa?" A razane ta d'ago kanta ta kalli Haisam d'in kana ta sake kawar da kanta, ba Tace Masa komai ba magana yayi tayi Yana bata hakuri Amma bata tanka Masa ba har ya gaji yayi shiru mikewa yayi da niyar fita, har yasa Kai ya tsinkayo Murya Umma tana fad'in "Shikenan Na amince" Da d'an saurin sa ya dawo cikin d'akin ya d'an rungumeta ta kana ya sake ta yace "Yauwa Umma ta ai nasan Zaki amince" mikewa yayi Yana fad'in "zani na fad'awa Mummy" "Wa ya aike ka? Ka bari da kaina zan Sanar da ita dama yanzu zan Shiga part d'insu" Murmushi yayi yace "Shikenan Umma" Mikewa tayi ta d'auki mayafin ta, ta nufi part d'insu mummy ta tarar a parlor sun dad'e suna Hira sama sama kamun ta fad'a Mata cewar ta amince mummy murna yasa ta Kira daddy a waya ta Sanar mishi, yayi farin ciki sosai shima Nan take ya Sanar da Abba, Abba baiyi kasa a gwiwa ba yasa aka tura masa number ta Sannan mummy ta bata na Abba, Ba 'bata lokaci ya neman Soyayyar ta. Haisam kuwa d'akin Isha ya Shiga ya Sanar da ita labari Mai dad'i tayi murna sosai, Nan sukayi ta hirar su. *BAYAN WATA 5* Shirye shiryen biki su ke tayi duk da ba wani events zasuyi ba daga walima sai walima shima anan gidan su Ma'isha kawai za'ayi. Yayin da Haisam da Aysha wata soyayya ce Mai karfi ya Shiga tsakanin su kusan kullum suna tare, Ma'isha kuwa damuwa Sai abunda ya karu, Meerah kuwa kusan ko wani sati zata Zo ta duba lafiyar ta sannnan ta bata shawarwarin da ya Dace Amma Duk da hakan Isha ta kasa daina son Haisam. Alhamdulillah an d'aura Auren Umma da Abba sannan Amarya ta tare a gidan ta anan cikin garin gombe, Daddy ne yayi iya bakin kokarin sa ganin ya dawo da dukkanin aikin Abba a gombe. Ma'aruf kullum cikin Kiran Meerah yake Akan maganar Ma'isha, Amma Ma'isha Taki bada had'in Kai shi Kuma ya kasa hakura. Wannan Kenan "Isha please think about it Mana, Wallahi ma'aruf na sonki ke ko tausayin sa bakya ji? Ki duba kiga ni fa tun d'azu Yana waje Yana jiran ki Amma kin ki, ki saurare shi" "Nifa na Riga na fad'a muku bana son sa Kuma bazan tab'a son wani ba bayan Haisam meyasa Kika kasa fahimta na ne?" "To ai Banga amafanin hakan ba, tunda kin kasa fad'a Masa har yayi nisa da soyayyar wata hakan zai tabbatar miki da cewar kin rasa shi Kennan har abada" Hawaye na a idanun Ma'isha d'aya na bin d'aya, taji zafin maganar Meerah Amma Kuma tasan gaskiya ta fad'a mata sabida masu iya magana sukace shi Gaskiya d'aci gareta. "Na Sani Meerah, nasan kin damu dani kin damu da farin cikina gami da lafiya ta Amma Dan Allah kar kiyi kokarin sani Dole sai na Kula shi" Mikewa meerah tayi Tace "fine then Ni zan tafi dama shine ya ce na rako shi, ki sani baza ki sake gani na ba a gidan ku, sannan zan fad'awa Haisam halin da kike ciki" ta Kama hanya zata wuce Ma'isha ta Sha gaban rike hannayen ta tayi tana kuka "Please don't do this to me Meerah ke ce kad'ai kike saurarata ke ce kad'ai Kika San damuwa ta Akan me zakimin irin wannan hukuncin Kuma Kar ki manta kin min alkawarin baza ki tab'a fad'a wa kowa matsala ta ba" Fin cike hannun ta tayi da karfi Tace "Dallah malama gafara min na wuce idan ke baki da shi to ni Ina dashi, idan baza ki bawa ma'aruf dama ba ya maye miki gurbin Haisam ba to Dole ne ki samu Haisam" Har kasa ta durkusa ta rike kafafun ta tana Mata magiya Akan Kar ta fad'a Masa. Meerah Sam Bata Jin dad'in ganin kukan ta Amma Dole ce tasa tayi Mata hakan, Dole ta samarwa kawarta farin ciki gudun Kar ta kamu da ciwon zuciya. Cikin murya Kamar fad'a Tace "Wallahi tallahi sai na fad'a Masa in dai baza ki kula ma'aruf ba ai zab'i na Baki" mikewa Isha ta tayi ta share hawayen ta Tace "Shikenan na amince wallahi zan kula ma'aruf, Dan Allah kar ki fad'awa ya Haisam Dan Allah" Murmushin samun nasara Meerah tayi kana ta sa hannu tana share Mata sauran hawayen dake fuskar ta. Cike da kulawa Tace "Am sorry Isha, ki daina kuka Sam bana jin dad'in ganin ki a Haka ne shiyasa nabi ta wannan hanyan, yanzu ki d'auko mayafin ki muje Yana chan yana jiran mu Amma ki wanke fuskar ki tukkunna" Ba musu tayi yanda Tace mata suka fita suka tarar dashi a cikin motar sa, jiki na rawa ya fito suka gaisa, Mai gadi tasa ya kawo musu kujera ya ajiye musu a inuwa, suka zauna daga bisani Meerah ta koma d'akin Isha tana jiran su, sai da suka gama hiran ma'aruf ya kirata ya maida ta gida, tun daga wannan ranar Isha ta fara kula ma'aruf lokaci zuwa lokaci Kuma Yana zuwa gidan su tun bata sake Masa har ta Fara Duk da ba son shi take ba, ma'aruf mutum ne mai abin dariya yakan sa taji ta manta Duk wata damuwar da take dashi in dai suna tare. *AFTER 1 YEAR* Sosai Ma'isha ke mayar da hankalin ta Akan karatun ta, Sannan Duk weekend a gidan Umma take yi, Haisam kuwa tunda Umma tayi aure aka rufe part d'insu ya dawo part d'insu mummy Yana d'akin sa kusa da na Ma'isha , idan suna gida sukan zauna a parlor suyi Hira Duk sanda ya kawo maganar Aysha kuwa sai tayi yanda tayi ta kawar da maganar. Ma'isha ne zaune da Ma'aruf a garden suna hirar su, labari yake Bata dariya take Sha sosai yayin da shi Kuma sai aikin kallonta yake. Haisam kuwa dawowar sa Kenan daga gun Aysha tunda ya Shigo gidan yake kallon su, ji yayi ransa ya 'baci Amma bai San dalilin hakan ba, ya d'auki kusan mintuna biyar Yana kallon su su kuwa Basu ma ji shigowar sa ba, kasantuwar motan da tint yasa Basu ganshi ba, ajiyar zuciya yayi Sannan ya fice daga cikin motar har ya wuce Ma'isha Tace "Yaya ka dawo?" Kirkirerren Murmushi yayi Sannan ya dawo mikawa ma'aruf hannu yayi suka gaisa turo baki Isha tayi Tace "Dama Yaya wuce wa zakayi Kamar baka ganmu ba?" "Am sorry princess , kin San hankali shine gani ban lura bane" kallon Ma'aruf yayi Wanda shima kallon sa yake yi, da sauri ma'aruf d'auke Kan sa gani yayi ya Masa kwarjini, maganar su sukayi tayi kana ya shige

Table of Contents

Chapters

76 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});