Chapter 37
Chapter 37
wa jama'a?" "Amma Yaya Ana uzuri ko?" "Eh Ana uzuri, Amma baza a d'aga bikin Nan ba, ranar jumma'ar Nan za'a d'aura auren. Abba ganin Daddy dagaske yake hakan yasa ya bar maganar suka Fara maganar kasuwancin su, Haisam kuwa Zama yayi dasu mummy Yana Basu hakuri had'e da wasa da kannen sa, sun girma sai wayo idan sukayi wata maganar zakace fad'a musu akayi, dab da sallar magrib Abba ya Shigo akan su koma gida. Umma ta kekashe Tace babu inda zata je anan zata kwana sabida ta kula da Ma'isha, Dole daddy ya hakura, Daddy ne yace "To kaji, kaima sai ka kwana anan, tunda gidan babu kowa baza ma kaji dad'in gidan ba." Murmushi yayi irin nasu na manya yace "To ya na iya da garen da ba wuya? Dole nima na kwana" Daddy ne ya maida kallon sa ga Haisam yace "Toh masu kanne taso muje Masallaci" suka wuce. Sosa keya Haisam yayi ya bi Bayan su. Ma'isha sai da gari ya Waye kana ta farka, mikewa tayi ta Shiga ban d'aki ta wasa ruwa kana ta d'auro alwala Sannan ta Shiga jero sallolin da ake binta, Bayan ta idar ne ta sauko parlor Jin muryar su Mummy a dinning room ne ya sa ta nufi gun, da sallama ta karasa inda suke ta jaa kujera ta zauna dukkanin su kallon ta suka Shiga yi cike da mamaki Umma tace "d'azun Nan fa na leke ta tana bacci, Amma gashi ta fito." Abba ne cike da kulawa yace "Daughter ya jikin naki?" Ta amsa da "Sauki Alhamdulillah" Daddy yace "Sannu daughter" Ta amsa da "Yauwa nagode Daddy." Mummy mikewa tayi ta shafa kanta had'e da tab'a wuyan ta Tace "Jikin naki da d'an zafi har yanzu" "Uhmn da sauki mummy" Haisam kuwa gyaran murya yayi yace "Princess ya jikin naki? Da fatan bakya jin komai yanzu?" Kirkirerren Murmushi tayi kana tace "Eh bana jin komai , sai Kaine da yake d'an sarawa kad'an kad'an" "Allah ya sauwaka, shima zai daina a hankali." Duk suka amsa da "Allah yasa" Kallon Mummy Ma'isha tayi Tace "Mummy nima a Samin abincin" Jika na rawa ta sa mata abinci, kallon ta suka tsaya yi Murmushi tayi Tace "Dan Allah ku daina kallo na haka sai ku sa na kware." Haisam yace "Ai Dole ne mukalle ki, Duk da Yan kwanaki kikayi bakya cikin mu, ji muke Kamar shekara kikayi" ya maida kallon sa ga su Umma ya d'aura da fad'in "Ko ba Haka ba" Umma ta amsa da hakane, dariya sukayi suna ta hirar su, dukkanin su sunji dad'in ganin Ma'isha a haka. Sai da aka Fara kiraye kirayen sallar azahar ,Duk mazan Suku fice zuwa Masallaci, Bayan sun idar da sallar kuwa asibiti suka nufa, Haisam office d'insa ya bud'e musu suka zauna kana ya fita, bai wani dad'ewa ba suka ya Shigo Meerah kuwa na biye da shi. Har kasa ta durkusa ta gaida daddy ne yace "Tashi ki zauna" Yana nuna mata kujerar dake fuskantar su, Bayan ta zauna ne ya Fara magana yace "Meerah nasan Daughters bata da kawar da ta wuce ki, sannan nasan kin San sirrukanta Dan Allah ina so ki fad'a min abinda Kika sani game da Wanda take so" Kai ta d'aga ta kalle shi kana ta maida kanta kasa Tace "Daddy ban sani ba, ban San Wanda take so ba" Abba yace "Please ki fad'a Mana gaskiya nasan Dole Akwai abinda Kika sani akai" Meerah har cikin ranta take so ta Sanar dasu gaskiya Amma idan ta tuna alkawarin da tayi wa Ma'isha sai ta fasa Tace "Abba da na sani wallahi zan fad'a Muku" Haisam ransa ya yi mugun 'baci cikin 'bacin Rai yace "Wallahi karya take Daddy, da kunne na fa naji lokacin da suke maganar Amma yanzu Kuma don ta Raina Mana hankali tace bata sani ba" Daddy yace "Son calm down" Abba yace "Kinji ko Ameerah, Dan Allah ki fad'a mana wane ne, kece kad'ai zaki taimaka Mana wajen sama wa zuciyar ta abinda take muradi" Shiru tayi tana matsar kwalla, a tsawace haisam yace "Shegen taurin Kan tsiyane da ita, ranar babu yadda banyi da ita ba Akan ta fad'a Min Amma taki, na rantse da Allah idan wani abu ya sami princess...... " Daddy ne ya d'aga Masa hannu yace "Ya Isa , ya Isa " mikewa yayi ya kalli Abba yace "Mu tafi ko?" Abba Rai ba dad'i ya mike yana girgiza Kai, Sai da suka Isa kofar fita, Abba ne ya juyo ya kalle ta yace "ki yiwa girman Allah ki ceci rayuwar Isha wallahi tana cikin wani matsanancin hali dan Allah ki fad'a mana gaskiya wane wannan wanda Isha take so a ina yake kuma d'an waye?" Cikin Muryar kuka Tace "Wallahi ban sani ba,da na sani da na fad'a Muku" Girgiza Kai Daddy yayi yace "Allah shi kyauta" suka fice Haisam Rai a 'bace yace "Tirrr da qawa irin ki, Wallahi ko kaffara bazan yi ba kin San komai" "Ya Haisam ban....... " A tsawace yace "Get out of my office" a tsorace tayi hanyar fita sai da ta kusa fita yace "Kuma ki sani idan wani abu ya same ta kece sila" cikin kuka ta fice. Tana fita shima ya fita, rufe kofar office d'in yayi ya nufi gun su Daddy dake tsaye a jikin motar sa suna jiran sa , hakuri ya basu Duk suka shige motar suka koma gida, Bayan ya ajiye sune ya koma office don cigaba da aikin sa. Daddy da Abba ganin Isha na walwala hakan yasa suka d'an ji dad'i, ta wuni cikin farin ciki sai fara'a take,Nan suka Cigiba da shirye shiryen biki, Isha kuwa Duk lokacin da ta Shiga tashin hankali sai ta Rika ambaton '''la'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu Minal zalimin''' hakanne yasa ta ji sauki abun Sosai. Rana bata karya sai dai uwar d'iya taji kunya, yaune ranar da Haisam da Aysha suke jira, shine ranar da yafi shekaru har hud'u yana jiran wannan ranar, Bayan sallar jumma'a za a d'aura auren amma a kofar gidan su Aysha za a d'aura dalili kuwa shine mahaifin Aysha ne ya bukaci hakan. Bayan sallar jumma'a jama'a sun taru, ga Nan waliyin Ango Amma babu waliyin amarya, Abba ne ya bukaci da a d'an jira su, wurin shiru yayi kwasam suka jiyo horn d'in mota da gudu motar ta karasa rumfar da Mutane suke zaune, Kura motar ta tada mutanen daga masu Allah ya wadai sai masu zagi, sai wa'anda Kuma suke kokarin toshe hancin su. Kowa hankalin sa a Kan motar take kowa son ganin Wanda ke cikin motar suke son gani, ai kuwa Mahaifin Aysha suka gani da Kanin sa, inda su daddy suke suka zauna, Haisam kuwa fararen jamfa da garen sa Sannan kansa bakar hulace Kamar yadda takalmin sa yake Baki,sai baza kamshi yake, Murmushi yake abokanan sa na tsokanar sa babu ma Kamar Farukh, Malamin da zai d'aura auren ne yayi hamdallah zaiyi magana mahaifin Aysha ya dakatar dashi malam yace "Lafiya dai ko?" Ya amsa da "Uhmn lafiyar Kenan Akwai Wanda ya kamata ku gani kamun a d'aura auren na" Abba yace "Wane ne? Kuma yana ina?" Hannu ya d'aga ya nuna Masa jikin motar,
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76