Chapter 73
Chapter 73
ta tare a gidan angonta.Allah ya bada zaman lafiya amiin. *After 4 months* Malam Hassan duk wasu raunuka na jikinsa sun warke Amma sabida tashin hankali da ya Shiga ya had'u da shanyewan 'barin Jiki, duk wani kud'i da ake kashewa Faisal ne yake bada su, yayin da Mamy har ta cire Rai da ganin Ayrah, kullum sai tayi kuka. "Mamy nifa na gaji da 'bata kud'i na Akan wannan mutumin" Faisal ke wannan maganar Kama hab'a mamy cike da mamaki tace "Kaci gidan ku" had'e da masa dakuwa. "Yanzu Kai Faisal rashin hankalin naka ya Kai haka? Ubankane fa duk lalacin sa, ni na d'auka kayi Dana sanin abinda ka aikata Ashe ba haka ba, ka godewa Allah ma da ya kowa abun da sauki da yanzu Ana irga kwanakin da ka mutu, daba don Allah yasa yaran basu da gata ba wallahi na tabbata da yanzu baka raye" "Mamy dama tun chan kwanakin mutuwa ta basu yi bane, Kuma wallahi ko kad'an bana Dana sanin abinda na aikata, Ban so hakan ba, naso da shi d'in ne ya mutu ko hankali ya zai kwanta" Tasss Tass Mamy ta shafa Masa maruka har sau biyu, rike kuncin sa yayi Yana matsar kwalla. Mikewa Mamy tayi Tace "Ka fice min daga gani Kar Kuma na Kuma ganin ka anan, Kan kazo ka karasa min shi" Faisal kwallon mahaifin sa yayi da yake kallon su, cike da hawaye a idanun sa, Murmushin Takaici Faisal yayi kana yace "Mamy mari na kikayi? Akan mutumin da bai damu dake ba, mutumin da bazai San mutuncin ki ba? Shin kin San irin bakin cikin da muke ciki da ni da Yan uwana Akan irin abubuwan da yake aikata Amma ke sabida.......... " Shiru yayi ya kasa karasa maganar kallon mahaifin nasa ya Kuma yi ya fice yana matsar kwalla. "Zainabu!!! A hankali cikin sanyin Murya taji ya Kira sunan ta, da sauri har kafarta na hard'ewa ta nufi inda yake tana tambayar sa "Malam wani abun kake buka ne?" Kai ya girgiza mata alamun a'a cikin Muryar sa Wanda baya fita mai kyau yace "Da baki mare shi ba sabida duk abinda yake fad'a gaskiyane, na kasa Mai son zuciya da son Kai, ban damu da kowa ba, ban damu da komai ba in dai zan samu abin da nake so...... " Ajiyar zuciya yayi Mai d'an tsawo kana yace "Na cutar dake da ke da 'ya'yan mu, ban kasance miji na gari ba sannan ni ba Uba na gari bane da ko wani yaro yake fatan samu, ki yafe min Abu, Dan Allah" Cikin muryar kuka Tace "Na yafe maka mallam, dama ban rike ka a Raina ba irin wannan ranar na ke jira Wanda zaka gane koren ka kuma kayi Dana sani , Alhamdulillah Allah nagode maka" ta karasa maganar tana kallon sling na d'akin tana matsar kwalla. Faisal da dawowar sa Kenan ya manta wayar sa , yaji dukkanin maganar da suke Yar karama tsaki yayi a zuciyar sa yace "Yanzun ma tuban muzuru ne don dama halin sane" kofar ya bud'e ba tare da yayi sallama ba ya sa kai ya shige,Mamy da Malam Hassan duk suka kalle shi,kawar da kansa yayi kamar baiga kowa a gun ba, ya nufi inda wayarsa take ya sa hannu ya d'auka sannan ya fice, girgiza Kai many tayi a zuciyar ta Tace "Allah ka shirya min yaran Nan" kwasam Ayrah ta Fad'o mata a rai mikewa tayi ta fice ta samu d'an corridor ta zauna tana kuka mai cin Rai, tana Jin zuciyar tana mata zafi,tana addu'ar Allah ya bayyana mata Yar ta,ko da kuwa gawar tane,sai da tayi mai isarta kana ta koma ciki. Soyyaya ce Mai karfi ta Shiga tsakanin Abdallah da Mardiya musamman ma Mardiya da take ji baza ta iya Rayuwa babu shi ba, don ta shaku dashi. Adnan na bawa Ayrah duk wata kulawar da miji ke bawa matar sa, tasan tana son Adnan Amma da zaran ta bar gidan dole ne ma ya sake ta taya ma Za'ayi ka 'boye Mutum har na tsawon watanni 8? Mardiya da Abdallah na hango a wani d'an madaidaicin shopping complex , Hirar su suke suna d'aukan abinda suke so kana ganin su kasan masoyan Nan suna suna cikin farin ciki, Bayan sun gama suka nufi inda zasu biya kudi, Mika mata wayan sa yayi Sabida ya samu damar ciro wallet d'insa. Tana rike da wayar a hannun ta yayin da take Danna wayarta da d'ayan hannun ganin ana ta Kiran sa Tace "Baby ana ta Kiran ka fa" a Shagwab'ance tayi maganar ba tare da ya kalle ta ba yace "wane ne?" "Adnan" "Bari in na gama zan kira sa" "Okay" A dai dai nan ya gama dasu suka nufi hanyar fita,Yana gaba tana biye dashi,booth ya bud'e ya sa kayan dake hannun sa. Mardiya na tsaye tana kallon sa ji take kamar ta sace shi,Jin Shigowar message yasa ta kalli fuskar wayar nasan,zaro Ido tayi ta bude sakon, kasantuwar wayar ba Key, sai da ta gama karanta sakon tayi saurin fita a ciki,tayi kokari dai dai ta kanta. Sau biyu yana Kiran sunan ta Bata ji ba,a d'an razane ta amsa da ya Kira sunanta a karo na uku,cike da kulawa yace "Lafiyan ki kuwa?" Turo baki tayi Tace "Bana jin dad'ine" "Ban gane ba yanzun Nan fa lafiyar ki kalau" "Uhmn Nikam ka maidani gida" "Kin fasa cin kifin ne?" "Eh na fasa ka maidani gida" ta karasa maganar kamar zatayi kuka. "Ikon Allah,to Shiga muje" Had'e da bud'e mata marfin motar ta Shiga ta zauna,ganin ya zaga tayi saurin ciro karamar wayarta a jaka ta wurga a Bayan mota, ta yi saurin gyara Zama kana ganinta kaga Mara gaskiya. Kallon ta kawai yayi ya girgiza Kai kana yace "Baby na Mai abun mamaki" Murmushi kawai ta masa,suna Isa gida Bata Tsaya Hira dashi kamar yanda ta saba ba, ajiye masa wayarsa tayi,tayi saurin fita,bai Ankara ba har ta isa gate,da d'an karfi yace "Kin manta ledan naki" "Au Na manta" ta dawo da d'an saurin ta karba had'e da fad'in "Thank you bye" ta shige gida da sauri,ya d'anyi Jim yana tunanin canzawan ta, kafad'ar Sa ya d'aga kana ya Shiga,Yana tada motar ya bar wajen,hannun ya sa d'auki wayar sa ya Shiga dialling number Adnan. Da sauri ta Shiga cikin gida bata ma lura da Haisam da ke zaune a parlor ba ,shi Kuma tab'e baki yayi ya girgiza Kai ya cigaba da danna wayarsa,tana Shiga d'akin ta yatsar da ledojin da jakar dake hannun ta kana ta cire gyallen dake Jikin ta,Zama tayi a bakin gado kana ta Kara wayar ta a kunnen ta. Ta dad'e a haka kana Naga ta miki zumbur ta d'auki jakar ta da mayafinta ta yafa ta fita da sauri, Haisam da Ma'isha ta hango Amma tayi kamar bata gansu ba tayi ficewar ta da sauri had'e da d'an gudu. Ma'isha Tace "Ita kuma wannan fa?" Hararar ta yayi kana yace " miko mini takalmin ki na rike miki Naga Alama sun miki nauyine sai kije ki tambayeta" dariya kawai tayi. Mardiya kuwa motarta ta fad'a tun Kan ta Isa gate take Masa horn, da sauri ya bud'e don ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76