Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 48

Chapter 48

Dangin Ubana Book 1 Complete Hausa Novel 1,204 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kaina hakan nakeji" "Allah ya kyauta ya mana Mai kyau" Meerah ta amsa da "Ameen" Nan sukayi ta hirar su har Saida akayi sallar Isha ta tafi. Mummy kuwa bata tafi ba har Saida daddy ya taso daga gun aiki yazo ya d'auke ta suka wuce gida. Ma'aruf na kwance ya rasa me ke Masa dad'i kallon silin d'akin ya tsaya yi yana tunanin mugun Hali irin na kanwar sa jin an turo kofa ne yayi saurin d'ago kansa ganin ta yayi a tsaye tana kallon sa wani dogon tsaki ya jaa had'e da fad'in "idan kina tunanin kinzo bani hakuriy ne to kin makaro don ba sauraron ki zanyi ba sabida haka ki fice min daga d'aki" ji ba karfi ta fice tana fita ya mike ya kulle kofar da key ya Koma ya kwanta, wayar sa ya d'auka da niyar Kiran Isha a waya har yayi dialling yayi saurin kashe wa tsaki ya jaa yace "mtsww to me ma zance mata, she has all the right to be angry, Mardiya kin cuce Ni" da Wannan tunaniin bacci ya sace shi. Washe Gari "Auta je ki dubo yayin ki har karfe 9 bai fito ba ko Lafiya" Jin an ambaci sunan sa sai da taji gaban ta yayi mugun fad'iwa , Mama ganin bata Mike ta a d'an tsawace Tace "Ke Lafiyan ki kuwa? Tunanin me kike haka?" Zumbur ta mike had'e da fad'in "Babu" tayi saurin barin gun, d'akinsa ta nufa, kirjin ta na duka uku uku ta kwankwasa kofar had'e da sallama, jin bai amsa ba ta tura kofan a hankali ta shiga, hangoshi tayi a kwance yana danna wayar sa har ta Isa kansa bai sani ba, zagayawa tayi don ganin abinda yake, hoton Isha ta gani yake kallo Duk ya manta kansa , gyara Murya tayi a razane ya d'ago kai ya kalle ta, a tsawace yace "Ke Wace irin dakikiyace da zaki shigo min d'aki ba sallama?" Cikin sanyin murya Tace "Nayi sallama baka ji bane" "Oh na Zama makaryaci kenan ko?" Ka ta d'aga Masa alamun a'a. Yace "Uban me ma ya kawo ki d'akina" "Mama ce tace Nazo na Kira ka karya" "Naji fice min daga d'aki" Tace "Yaya Dan Allah kayi hakuri nasan ban kyauta ba ,Dan Allah ka rufa min asiri Kar ka fad'awa su Mama" "mtsww Ce miki akayi ban San me nake ba? Dole ma na gaya musu jira nake Baba ya Dawo na Sanar Masa komai da komai ya kamata su San shaid'aniyar da suka Haifa" Durkusawa tayi tana kuka Tace "Dan Allah Yaya Kar kamin haka Wallahi zasu tsane ni" " Mtsww Wannan Kuma ke ta shafa, indai na rasa Ma'isha Wallahi kema sai kin rasa farin cikin ki, sabida Ma'isha itace farin cikina" "Inshallah baza ka rasa ta ba yaya,zanje har gidan su na bata hakuri Dan Allah Kar ka Sanar musu." Nagode kwaraai da Addu'an ku, Allah ya bar kauna,gamo da Typhoid da malaria nayi Kun san Basu da mutunci😅 Ina sonku fans Allah ya bar Kauna _________________________ Please comment and share Milhaat ce Yar Terawa [7/6, 1:26 PM] Miilhaat: 🍃 *DANGIN UBANA*🍃 Story & Written By Milhart Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne. *🌍MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION📚🖊* *M. W. A* *Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.* Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️ *BISMILLAHIR RAHAMANIN RAHIM* Page 51&52 _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._ ```Continuation.......``` "Naji na amince bazan fad'a musu ba, Amma da sharad'i" "Mene ne shi Wallahi zanyi Koma mene ne in dai Bai fi karfina ba" "Okay kije ki bata hakuri idan ta hakura Shikenan" "To Amma yaya kana ji fa ranar Tace Baza ta tab'a yafe min ba" "Wannan Kuma ke ta shafa, don wallahi idan Isha taki aure na hmmmm...... " Girgiza kai yayi had'e da ciza leb'en sa yace "Idan taki aure na, na rantse da girman Allah sai na muzguna Miki mark my words" ya karasa maganar yana nuna ta da Yar yatsa mikewa yayi kana ya fice. Bin Bayan sa tayi da Kallo girgiza kai tayi Tace "Za'ayi auren nan,Kuma Insha Allah daga Kai har ita sai kunyi dana sani." Sai ta fice d'akin ta ta nufa ta Kira Ayrah ta Sanar da ita abinda ke faruwa, Sannan ta Sanar mata da zata je gidan su Isha anjima Kuma tana so ta mata rakiyi, Ayrah ta amince don daga jin muryar kawar tata tasan tana cikin damuwa. Mama na ganin sa Tace "kana Lafiya kuwa? Meyasa baka fito ba tun d'azu?" "Ina kwance ne mama" "Okay zauna ka Karya sabida ina so mu yi maganar kayan lefen Nan" Ji yayi gaban sa ya fad'i, zama yayi had'e da fara cin abinci. Bayan sun gama wayar ne ta fita, dinning itama ta nufa suka zauna suna cin abinci, Bayan sun gama ne ta fita da niyar zuwa gun Aiki, Amma ba gun aikin ta nufa ba, gidan su Ayrah taje, Basu d'au wani lokaci Mai tsawo ba suka nufi gidan su Isha, Suna Isa Kwankwasa karamin gate d'in gidan Sukayi bayan sun gaisa da Mai gadi Mardiya Tace "Dan Allah Baba gun Ma'isha muka Zo da fatan tana ciki?" "A'a bata Nan" Ayrah Tace "Dan Allah ka San inda taje ne?" "Eh to Dama gun zuwan ta Basu wuce wuri biyu ba zuwa uku" Tace "Ina da ina Kenan?" "Gidan Baffan ta ko asibiti, Amma na fi sa ran tana asibiti" A tare suka ce "Toh Mun gode" motar da suka Zo da ita suka Shiga kana sukayi hanyar asibiti, Bayan sun Isa asibitin da Isha ke aiki Kai tsaye pharmacy suka nufa, wata pharmacists suka gani Bayan sun gaisa ne suka tambaye ta Ma'isha ko tazo ta tabbatar musu da cewar yau bata Zo ba tana shift. Tsaki Ayrah tayi kana Tace "Ai na fad'a miki da Mun fara zuwa gidan Baffan nata tukunna" "Mtsww kina da matsala Wallahi Yanzun da kafa muka zone? Kar ki manta fa sa motata muka Zo Kuma man ciki ni Na saka bake Kika samin ba mtsww" tana kai na tayi gaba bin Bayan ta Mardiya tayi Tace "Banga laifin ki ba, Ni na jawo wa kaina da na rako ki, Sannan sannin Kanki ne mu ba matsiyata bane bare kice zaki min gorin

Table of Contents

Chapters

76 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});