Chapter 56
Chapter 56
Masa kofar,Kan gado ta koma ta zauna shi Kuma ya Shiga ban d'aki,alwala yayi Bayan ya gama ne ya fito ya wuce Masallaci ba tare da yace Mata uffan ba. Itama mikewa tayi ta Shiga ban d'aki tayi alwala ta shimfid'a sallah ya Shiga yin sallah,Bayan ta idar ta zauna Akan sallayar tana azkar. Ma'aruf Kuma bai dawo cikin gidan ba har sai da gari ya fara haske,ya Shigo har cikin d'akin bakin sa d'auke yake da sallama,tana zaune akan sallaya, d'ago kanta tayi ta kalle shi suna had'a ido ta kawar da kanta a hankali, amsa sallamar sa tayi had'e da fad'in "Ina kwana" Ya amsa da "Lafiya how was your night?" Tace "Alhamdulillah" had'e mikewa,sallayan ta nad'e kana ta Shiga ban d'aki, Jin saukar ruwa a shower ne yasa ya fice daga d'akin,Bayan ta gama ne ta leko taga baya d'akin fita tayi cikin sauri ta nufi kofar ta sa key. Gaban Mirror ta nufa ta zauna,kallon kanta tayi a mirror ko me ta tuna Naga ta girgiza kai had'e da Yar karamar dariya mai d'an sauti,Mai ta Shiga shafawa a jikin ta Bayan ta gama ne ta ciro kayan da zata sa, Riga da skirt d'in atamfa ta sanya a jikin ta, ba tayi wani kwalliya ba powder ta shafa sai kwallin da ta saka a idon ta sai lip glow. Fita tayi daga d'akin, parlor ta nufa kallon d'akin ta tsaya yi tana ganin kokarin iyayen nata had'e da sa musu Albarka, komai na d'akin Royal Blue ne da Sky blue ya haska d'akin sosai ga wani uban kamshi da d'akin keyi. Motsin da taji ne yasa tayi saurin maida kallon gun, a hankali take ta fiya har ta Isa kofar da take jin karar,a hankali ta Turo kofar had'e da kusa kanta ciki, kallon kitchen d'in ta tsaya yi tana Murmushi,ta shagala da kallon kitchen d'in har ta manta dalilin da yasa ta Shigo. Ido hud'u sukayi,kallon kallon suka Shiga yi wa juna,wani irin kallon yake binta dashi ganin yanda tayi matukar kyau Duk da ba wani cika take dashi sosai ba kayan yabi jikin ta,kamar a jikinta aka d'inka shi. Ganin kallon da yake mata yayi yawane yasa tayi sauri juyawa da niyar fita cikin Murya mai sanyi yace "Isha!!! A hankali ta juya tana kallon sa murmushi yayi kana yace "Kinyi kyau" Murmushi itama tayi had'e da fad'in "Thanks" ta juya zata fita yace "Hold on mana" ajiye spoon d'in dake hannun sa yayi ya nufe inda take hannun ta ya riko ya jaa ta izuwa gun gas cooker da yake girki da ita. Marfin tukunyar ya bud'e yace "Look Waifa gwanin ta zan miki Kuma sai naga baiyi yanda nake gani idan Mama tayi ba" Isha kusa dariya ta Shiga yi Tace " Me ne wannan d'in?" "Bakya gani Irish potatoes ne" "Eh na gani ina nufin me kake son girkawa?" "Chips Mana ai tunda kwanaki ka ka fad'a min kina son chips sosai sai na kudiri aniyar yi miki shi da kaina" Dariya take yi sosai shi Kuma ya rungume hannun sa yana kallon ta cikin Muryar dariya Tace "chips fa kace" ya ama da "Eh Mana" Dariya ta kumayi Tace "ba dai chips ba sai dai pourage" yace "Pourage Kuma gwate kenan fa?" "eh Mana ina ka tab'a ganin chips haka,ai da ka dage ka koya Kan irin ranar Nan tazo" " Uhmn Gaskiyar ki,ai ni yanzu ma gani nake kamar mafarki nake" Jin abinda yace ne yasa ta daina dariya kamar anyi ruwa an d'auke Tace "Ban gane kamar mafarki ba?" "Umm na d'auka bazan tab'a samun ki ba Isha" Murmushi tayi Tace "Kasan mene ne?" Yace "A a sai kin fad'a" Sauke tukunyan tayi kana Tace "bari na nuna naka yanda akeyin chips sabida gaba" Kai ya d'aga had'e da fad'in "to" Nan ta Shiga fere Irish d'in shima wani wukan ta d'auko Yana Taya ta ,sai ta fere biyar bai fere d'aya ba tayi ta dariyar su sunayi suna Hira sama sama,Bayan sun gama ta soye shi had'e da soya kwai ta d'aura a gefe, a tare suka kai abincin dinning,zama yayi tayi serving d'insu suka fara ci. Bayan sun gama cin abincin a tare suka kai kitchen, a parlor ta zauna da niyar Kallo taji yace "d'auko mayafin ki mu shiga mu gaida su Mom" Mikewa tayi had'e da fad'in to, d'aki ta shiga ta d'auko hijab dinta har kasa, tana fitowa suka wuce part d'in su Mom, da sallama suka shiga mom ce na gani a tsaye ita da Mardiya. Baki a bud'e take kallon su Tace "Har kun tashi? Yanzu fa na ke cewa yarinyar Nan ta kai muku breakfast" Neman wuri yayi ya zauna had'e da fad'in "ai mun karya" "Shine kasa 'yata girki daga zuwan ta?" "A a ni nayi girkin fa" Mom kallon Ma'isha tayi Tace "Wai hakane?" Murmushi tayi kana Tace "Na daiyi Mom" "Yauwa nasan za'a Rina" Kama baki yayi yace "Lallai bakya tsoron Allah ina laifin ma kice mata tare mukayi?" Dariya kawai tayi Bata ce masa komai ba, mom Tace "Sai ka nemi wuri ka zauna ka bar ta a tsaye" Gyara Zama yayi kana yace "Yan zun Nan fa Kika ce Yar kice meaning ba sai ance Mata ta zauna ba tunda a gidan su take ko?" Tab'e baki Mom tayi, zuwa tayi ta riko hannun Isha ta zaunar da ita, Ma'aruf kallon Mardiya yayi cikin Murya kamar fad'a yace "Ke baki iya gaisuwa bane? Ko baki ga Mutane bane?" "Uhmn Yaya Kenan ai gani nake kamar Duk Kun manta dani shiysa, ina kwana?" Ya amsa da "lafiya" Maida kallon ta ga Isha tayi taace "Ina kwana Aunty Isha" Murmushi tayi had'e da fad'in " lafiya Lau kin tashi lafiya?" " Lafiya ya Amarci?" Murmushi kawai tayi bata ce Mata komai ba, kallon da Ma'aruf ya mata ne yasa ta ajiye food flask d'in dake hannun ta , had'e da kokarin barin gun. Mom ce Tace Mata "Ya haka Kuma anan Zaki bar min abincin? 'dauka ki Kai musu part d'in su" Cikin sauri ta d'auka ra fita. Ma'isha har kasa ta durkusa Tace "Mom ina kwana?" Cike da fara'a ta amsa da "Lafiya Lau ya kwanan bakonta?" Murmushi tayi had'e da fad'in "Alhamdulillah" Ma'aruf ma gaishe ta yayi Bayan sun gama gaisawa yace " Dad ya fita ne?" Ta amsa "Yana d'akin sa , ku shiga ku gaishe shi" mikewa yayi had'e da kallon Ma'isha yace "Zo muje" mikewa tayi Sim sim tana binsa a baya, d'akin Dad suka nufa Bayan sun gaishe shi ya musu nasiha da fatan Allah ya basu zaman Lafiya Mai d'aurewa, Nan suka tashi suka koma part d'insu kasantuwar Mom bata parlor d'in. "Mamy yanzu haka zamu zuba Ido muna kallon Daddy yana abinda ya ga dama a gidan Nan ki duba kiga yau ma ya shigo da mace" Faisal ke wannan maganar. Sunusi yace "Mata dai ai su biyune yau Kam" Faisal yace "Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un, that's it Wallahi yau d'in Nan zan yi maganin Yan iska" ya mike Yana huci yayi d'akin sa. Mamy kallon sa kawai tayi ta kawar da kanta, Sunusi yace "Mamy Wai baza kice wani abu bane ba?" "To me zance muku tunda
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76