Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 59

Chapter 59

Dangin Ubana Book 1 Complete Hausa Novel 1,195 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

da abinda yake rayawa a ransa. A hankali yake kusanto fuskar shi da na nata, had'e kansu yayi wuri guda suna jin numfashin shin junnan su sun d'auki tsawon dakika 6 a haka, tsintan Kan su sukayi suna sumbatar junan su, a hankali suke Shan bakin junan su, sun dad'e a haka, a tare Kuma suka janye bakin su suna wani irin numfashi yanda kasan sunyi gudu ne. Hannun ta ya rike suka shige bedroom d'insu, a Kan gado ya zaunar da ita, ya shige bathroom yayi wanka, Bayan ya fitone itama ta shuga, Bayan ta fito ne ta hango shi Yana ki shin gid'e a Kan gado daga shi sai Vest da gajeren wando, d'ago Kai yayi ya kalle ta, jikinta ya ke bi da kallo daga ita sai towel, zumbur ya mike ya nufe, Sa hannu yayi ya raba ta da towel d'in jikin ta, rintse ido tayi, Murmushi yayi ya sa hannu ya d'auke ta kamar wata Yar Baby, Akan gado ya dirar da ita Nan ya Shiga raba kansa da kayan dake jikinsa, niko ina ganin hakan nayi saurin barin d'akin na ja musu kofa, Nace bari na leka asibiti Naga a wani hali su malam Hassan suke. asha Amarci Lafiya. "Sister nifa gaskiya na gaji da yawon asibitin nan kullum Kenan mu muna hanyar asibiti, gashi Yan iskan Nan sun hana mu komawa makaranta wai strike" Murmushi Ayrah tayi Tace "Sunusi Kenan to yanzun me kake nufi? Zuwa asibitin ne baka so ko Kuma haushin ASSU kake ji?" " Duka" yace a takaice, Nabila Tace "Ni kaina na gaji Wallahi, kullum asibiti kullum asibiti" "To ai rashin Jin Faisal ne ya ja mana hakan, gashi Nan Yana chan a tsare na tabbata ba sake shi zasuyi Nan kusa ba" Nabila Tace "Nifa yamin dai dai Wallahi" Sunusi yace "To yanzu wa gari ya waya? Kin San dai hukunci Wanda ya kashe shine a kashe shi ko?" Cikin Muryar kuka Ayrah Tace "Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un wannan masifa dame tayi Kama?" Sunusi girgiza kai yayi ya fice abinsa , Nabila ganin Ayrah ta Shiga tashin hankali sosai Tace "Sister ya labarin Adnan ne Kam?" Hannun tasa ta share hawayen dake fuskan ta kana Tace "Yana Nan, kin San tun lokacin da yaji labarin aurena da Haisam ya rikice babu yanda baiyi dani ba Akan Kar na Masa hakan, na so na Fad'a Masa plan ne Amma na kasa gudun karya tarwastsa Mana shiri" " To yanzu ya ake ciki?" " Ya daina kulani babu yanda banyi dashi ba Amma yaki kulanai shiyasa na hakura Amma to my surprise jiya ya turo min da wani sakon da ya tsorata ni" Zaro wayar ta tayi a d'an karamin purse d'in dake hannun ta ta Shiga text d'in ta Mika wa Nabila ta fara karanta shi kamar haka. "Na tabbata kina cikin tashin hankali Sabida iftila'in da ya dirin muku a gida, Allah Kenan baki ga komai ba this is just the beginning" Nabila kallon ta tayi kana Tace "Me yake nufi da hakan?" Tab'e bako tayi Tace "I don't know Wallahi, and I love this guy so much" Muryar Mamy taji tana fad'in "Kwarai kuwa baki ga komai ba ko ince bamu ga komai ba, Ai Allah ba azzalumin bawan sa bane ba, sai Wanda ya zalunci kansa bare Kuma Kun tab'a maraya, yau tsawon shekara nawa haisam yake kwance rai a hannun Allah, ai naso da yana Raye yaga halin da mahaifin ki ya shiga kuma Wallahi masifa da bala'i yanzu kuka Fara gani, gashi chan Faisal shima taurin Kan Nasa abinda ya jaa wa kansa" Nabila Tace "Haba Mamy maganganun ki sunyi tsauri dayawa Kar ki manta fa ke uwace, Mamy idan uwa tana yawan sawa d'anta Albarka tab'arbarewa yake bare kuma kin Masa mugun fata Dan Allah, Mamy ki Mana addu'a Allah ya Kawo Mana d'auki" " Ni bazanyi musu mugun baki ba, Sannan ni bazan musu addu'a ba" tana kaina ta fice daga gun, ta shige d'akin Malam Hassan, hawaye ne ke gangarowa daga idanun sa kallon sa tayi ta jaa wani uban tsaki Tace "Nasan maganar da mukayi ne da yaran Nan yasa kake kuka to Wallahi baka ga komai ba, Duk Wanda yaci Amana to ba Makawa amanar Allah zata ci shi." Ta jaa kujera ta zauna ta d'aura kafa d'aya akan d'aya ta Shiga danna wayar ta. Malam Hassan kuwa tunda wannan abin ya same shi ya daina magana, sai dai Ido kawai. Tun daga Wannan ranar Isha da Ma'aruf wani soyyaya mai karfi ya shiga tsakanin su kullum a like suke da juna idan kaga sun rabu to ya fita office ne, a haka har suka gama cin amarcin su, har ta koma bakin aikin ta, sannan lokaci zuwa lokaci ta kan je gidan Umma ko kuma gidan Mummy wasu lokutan Kuma tare da Ma'aruf d'in suke zuwa. Mardiya kuwa,tun ranar da ta kai musi abinci bata sake Shiga part d'insu ba,idan sun had'u a gun Mom sukan gaisa, kawancen nata da Ayrah tayi baya sosai ba kamar da ba kasantuwar Ayrah idan bata gun aiki to tana gun mahaifin ta, Itace Kad'ai take kula dashi Mamy kuwa da ta gaji da jinya gidan su ta koma, Ni ko Nace Anya Mamy bata d'auki zafi dayawa ba kuwa? *AFTER SOME MONTHS* Meerah ce ta Kawo wa Isha ziyara , Bayan sun gama hirar su ne suka fito tare har gun motar ta ta rakata, suna tsaye suka hango motar Ma'aruf parking yayi ya fice a motar yazo inda suke, Bayan sun gaisa ne ya ce "Barina na shiga part d'insu mom Dad ne ya dawo" "okay Nima gani Nan shigowa yanzu" "Okay ya shige ciki" Yana wasa da key d'in motar dake hannun sa,Isha binsa tayi da Kallo tana Murmushi , Meerah Tace "Wannan kallon fa?" "Hmm Bangane ba mijina ne fa" "Oh sai yanzu Kika San cewa mijin kine ko?" " Tun da dad'ewa Nasan da hakan" "Uhmnn manyan Mata, Amma naji Dad'i Gaskiya da Kika kwantar da hankalin ki no wonder Mana Naga sai Fresh kike kina kyau, Anya ma ciki kike dashi ba?" "Dallah malama bana son sa Ido...... " Motar Mardiya ce ta shigo ta faka, Bayan ta fito wurin su ta nufa, Isa wurin su ke da wuya suka jiyo wani uban Kara, juyawan da zasuyi suka hangi part d'insu Mom ne yake ci da wuta ga Warin gas ya maimaye gun gaba ki d'aya. Dukkanin su babu Wanda ya Isa mosawa a gun, suna Tsaye suna kallon ikon Allah, Mai gadi be ta fito daga ban d'aki hannun sa rike yake da buta yana kokarin d'aure mazargin wandon sa, Yana fad'in "Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un, ba kowa a ciki ko?" Nan ne fa Isha ta d'aura hannu a kai ta kwarma wani uban ihu, ta yanke jiki ta Fad'i , Mardiya kuwa suman tsaye tayi daga bisani ta Fad'i sumammiya, Meerah kuka ta shigayi tana nemon taimako. ________________________ Rashin comment d'inkune yasa jikina Duk ya mutu da typing d'in,Dan Allah ku bani had'in kai Nasan Kuma Kun kosa da kuji yadda labarin zai kasance Please Comment and share Milhaat ce Yar Terawa 63&64 '''Continuation.....''' da gudu Mai gadi ya nufo su, Yana ta ambaton

Table of Contents

Chapters

76 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});