Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 19

Chapter 19

Dangin Ubana Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kana ta kashe wayarta ta kwanta taso yin bacci ta kasa ta dad'e a haka kamun bacci ya d'auke ta. Haisam wurin motar sa ya nufa duk a tunanin sa tana jiran sa, ganin bata Nan yace "to ina tayi ne?" Sa hannu yayi a Goshen sa yana ta waige waige bai ganta ba sai Kuma yace "Maybe bata zo ba nasan dai zata jirani" Daga bisani ya shiga Masallaci don yin sallah, har ya idar ya dawo Bata Nan Zama yayii a motar har wuri ta Fara duhu, tsaki yayi ya jaa motar yabar gun. Yana shiga gida d'akin ta ya nufa ya tura yaji a rufe, d'akin mummy ya nufa ya ga bata Nan, da sauri ya fice ya nufi part d'insu da sallama ya Shigo a tsatsaye ya gaida su yace "Mummy Ma'isha fa?" Cike da mamaki suke kallon sa Umma Tace "Lafiyan ka kuwa meya same ka Shigo a rud'e Haka?" "Umma banga Ma'isha ba, na d'auka ta dawone Kuma ban ganta ba" Mikewa Umma tayi Tace "Shirmen banza Kenan dama ta tab'a dawowa ba tare da Kai bane?" "Umma wall....... " Mummy ce ta katse shi da fad'in "Son kasan dai baza ta 'bata ba ko? Ka Kira wayar ta man" "Wallahi mummy wayata ce ta d'auke to nafi sa ran ta kirani ne bata same ni ba" Umma ce ta zaro wayar ta dake chaji ta Shiga dialling number ta Amma switch off kallon Haisam tayi Tace "A kashe" Kallon ta kawai yayi ya ma rasa abin fad'i,kana ganin sa Zaka gane Yana cikin tashin hankali, Ya dad'e a tsaye mummy Kam kallonta ta cigaba dayi yayin da Umma sai safa da marwa take tana Kiran layin Amma haryanzu a kashe. A tsawace Tace "To uban me kake jira anan? Kana ji an Fara Kiran sallar maghrib yarinyar Nan bamu San a wani Hali take ciki ba ka fita kaje ka Nemo min yarinya,Kuma wallahi kar ka kuskura ka ka dawo gidan Nan ba da daughter na ba kaji na Gaya maka." jiki ba karfi ya Shiga d'akin sa , cable d'in wayar sa ya d'auko ya fice ya fad'a motar sa, wayarsa ya zaro daga aljihun wandon sa kana ya sa a chaji, zaro Ido yayi don ganin fuskar wayar tasa da kyau a bayyane yace "15 percent to ya akayi wayar ta d'auke?" Tsaki yayi ya kunnata ya Shiga dialling number ta haryanzu a kashe, jaan motar yayi ya fita Masallacin unguwar su ya nufa yayi sallah, bayan sun idar ne ya Kama hanyar makaranta, duk inda yasan Ma'isha ke zuwa babu inda baije ba Amma Bata Nan, duk da cewar dare ne Amma Akwai student a school d'in. Haisam hankali a tashe ya Shiga motar sa ya nufi gidan su Ameerah, Ameerah qawar Ma'isha ce tun a secondary school yakan kaita gidan idan sun gama hirar su ya koma ya d'auko ta, Kiran layin Ameerah yayi da yaw Isa kofar gidan su. Mamaki ma abin ya bata sabida ba ya kiranta haka kawai sai da dalili, picking tayi bayan sun gaisa yake fad'a Mata yana waje had'e da tambayar ta suna tare da Ma'isha ta tabbatar Masa da rabuwar ta da ita yafi 2 weeks tun bikin kawar su da suka je yace "Ya Salam" Cike da kulawa tace "Lafiya kuwa? Wani abun ne ya Faru?" "Lafiya lau, sai anjima bari na wuce" "Baza ka Shigo ku gaisa da Mama ba? " "Zanzo wani lokacin ki gaishe ta" kitt ya katse wayar. Ma'isha kuwa tana chan tana ta baccin ta, da sallati ta farka ta kalli agogon dake d'akin ta taga karfe 7 saura mikewa tayi ta watsa ruwa kana ta tayi alwala tayi sallah wani uban yunwa take ji hakan yasa ta nufi kitchen food flask ta bud'e, farar Shinfa ta gani ta bud'e d'ayan taga stew tsaki tayi Tace "Mutanen gidan Nan da shinkafa nifa in ba tuwo ba duk shirme ne" plate ta d'auko ta zuba, kujerar dake Kitchen d'in ta samu ta zauna sai da ta cinye abincin Tass har ta Kara tasha ruwa tayi hamdallah, tasa Kai zata fita suka ci karo da Mummy Tace "Sorry mummy ban ganki ba ne" cike da mamaki mummy Tace "Ma'isha kece?" "Eh Mummy" "Yaushe Kika dawo?" "Tun kan la'asar" Mummy ta Shiga ta yarfa hannu Tace "Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un Amma Ma'isha Allah ya shirye ki,Ashe dawowa kikayi Kika sa Yayan ki wahalan neman ki yanzu ga chan Umman ku ta Hana shi zaman gidan na tace kar ya kuskura ya dawo ba tare dake ba Ashe kina Nan kina ta baccin ki" Turo baki tayi tace "To ai mummy...... " "Ai mummy me ke? Ki fita daga idona Ma'isha wannan wani irin rashin hankaline, me ya sami wayar ki mukayi ta Kira a kashe?" "Kashe nayi" Kai a kasa Tana wasa da yatsunta. "Ka jimin ja'irar yarinya ki tadawa mutane hankali ba gaira ba dalili, dama kije ki Kira shi yanzu, tun d'azu yaron Nan baya gida gashi tun safe bai sa abinci a cikin saba kuka tafi makaranta ke Kuma kina Nan kin zauna Kinci abincin ki in ba mugunta ba" "Mummy kiyi hakuri Dan Allah, wallahi na Kira layin sa ban same shi ba Kuma na gaji da jiran sa shiysa,Kuma na dawo a gajiye shiyasa fa na dawo gida Amma kiyi hakuri please" "Dallah gafara ki bani wuri ko na had'a kanki da ginin Nan Mara hankali kawai" Ficewa tayi da sauri don taga alama mummy zata iya buga Kan natan ta dad'e bata ga 'bacin ran mummy irin haka ba, da gudu ta Shiga d'akinta tana matsar kwalla, tana kunna wayar shigowar kiran Haisam ne ya shigo. Haisam a kishingid'e yake a cikin motar, parking motar yayi a kofar gida ya kasa shiga cikin gida don bai San irin masifar da zai Sha a gun sa ba, ta dad'e baiga umman sa a cikin irin 'bacin ran Nan ba. Jin Kiran ya Shiga ya zauna cike da kulawa yace "Princess Lafiyan ki kuwa? Kina ina nazo na d'auke ki?" Cikin sanyin murya Tace "Ina gida" Cike da mamaki yace "Gida wani gidan? Yaushe Kika dawo?" "Gida man Ya Haisam akwai wani gidane bayan namu? Kuma tun kan la'asar nake gida" Kashe wayar yayi, yayi horn Mai gadi ya bud'e Masa, Yana Shiga ya kashe motar ya fita ba tare da ya Kai motar parking lot ba, ya shige cikin gida da sauri, d'akin ta ya nufa, kofar d'akin ya tura da d'an karfi ganin ta Akan gado ya d'an ji sanyi a ransa sai Kuma ya fice daga d'akin tana Kiran sunan sa yaki kulata. *FEDERAL LOW-COST* Ayra kwance take Akan lallausar katifan ta, da sallama daddyn ta ya shigo tana ganin sa ta tashi Tace "Sannu da zuwa daddy Ashe ka dawo?" "Eh Yar daddy na dawo tun d'azu mummyn ki Tace min kina school, ya school d'in dai?" "Lafiya Lau daddy" "Komai normal ko?" "Eh Daddy" "Masha Allah, to ya maganar mu ta kwana? Da fatan kin Fara aikin da na saki?" "Hmm daddy Kennan ka kwantar da hankalin ka alkawari na maka sai na Kai makiyin mu kasa ko ta wace hanyance Kai dai kawai ka tayani da addu'a" "I trust

Table of Contents

Chapters

76 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});