Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 75

Chapter 75

Babban Yaro Book 2 Complete Hausa Novel 1,209 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Hararata nayi ganin ta juya baya zumb'ura baki nayi na shiga band'akin ta dake parlor. Ina tsungawa naga ni bu mai yauki na dilala daga gabana, dama tun da aunt ta sanyamu a gaba nake jin wani azabbaban feelings na taso min. Ruwan zafi cikin wata butar.k'arfe na dauka na daureye gurin sosai sannan na fito raina duk babu dad'i *30/11/2019* *BABAN YARO* *MALLAKAR BINTA UMAR *69* Shirye-shirye ta kowa wane fanni ya kammala Ya Aminu ya had'a lefe na gani na fad'a sosai Umma da aunt hauwa sukayi kokari a kansa, yanzu nawa lefan ake jira sai a fara Rabin goro kullum muna tare da Jahid a waya muna shirya tsarin buki da yanda zai kasance. Momyn Mujahid ce take kai kawo a parlor ta takasa tsaye ta kasa zaune wato Mujahid ya yaudare ta ya rufe ta sun hada baki da ubanshi ya bujerawa bukatar ta, lallai ne ka haifi da a cikin ka ya wulakanta ka lallai zata nuna masa iyakarsa, yanzu ta sakko daga sama dalili shi mijin NATA ya kira ta tazo taga kayan lefa kuma saboda sun raina mata hankali wai itace zata nemi masu kaiwa don haka baram!_baram suka rabu da mijin nata ta sauko a fusace jiran zuwan Jahid din take domin tayi masa magana ta k'arshe kan auran. Tunda ya shigo yaga tana kai kawo hankalinsa ya tashi yasan dole duk abunda yake b'oye wa ta sani, ko k'araso wa bata bari yayi ba ta karasa gurinsa a zafafe ta zabga masa mari Tana huci! Kamar zakanya tace"Ni zaka yaudara Jahid wato kun hada haki da ubanka kun rufe ni saboda baka dauke ni a bakin komai ba ko? Jahid yayi shiru hade da yin kasa da kansa. Ta cigaba da cewa "Wallahi in har nice na haifeka baza ka auri yarinyar da ta zageni ba, idan kuma kayi ganganinci auranta to babu shakka a ranar zaka sake ta ko kuma in d'aga maka nono don tsine maka zanyi wallahi tallahi kaji domin bazan yi kaffara ba."!!! Ta k'arashe maganar tata a zafafe! Ya wani irin huci! Jahid ya shiga cikin wani irin mugun yanayi a lokacin gumi ya dinga tsiyayar a jikinsa duk yanda yaso ya fahimtar da mahaifiyar sa al'amarin ta kasa fahimta. Wasu mazan sukan fuskanci matsala daga gurin matayen su a sanda zasu kara aure, shi daga gurin mahaifiyar shi ya fuskanci matsala. Mik'ewa yayi baya ko kallon gabansa, ya fita daga parlor. Wani irin kallo ta bishi dashi ta ta tabka wani irin tsaki, ta zauna kan kujera tana fadin" da in hada jini da talaka gwara duk abunda zai faru ya faru. Jahid kuwa kai tsaye b'angaran Amjad ya nufa a lokacin hankalin sa a tashe! Granny na ganinsa cikin wannan halin ta tabbatar babu lafiya, zama yayi kan kujera hade da dafe kansa, granny Tace "Tabbas komai yayi tsanani maganin sa Allah, Mujahudu akwai damuwa a tattare da kai. Ya d'ago kansa yana kallonta, kawai sai taga hawaye a fuskar sa yana zubah, cikin mamaki tace" kafadamun damuwar ka Insha Allah zan taya ka da addu'a. " Cikin karkarwar jiki ya warware mata dukanin abunda yake faruwa. Granny ta jima tana mamakin al'amarin daga bisani tace"Tabbas Hajiya Sa'a ta tabka babban kuskure, waye ya fada mata ana jayayya da al'amarin aure duk yanda bakason hada zuri'a da mutum idan Allah ya kaddara faruwan haka babu makawa sai ya faru idan tana tsananta kamar Yanzu Allah sai ya dauke ta ayi babu ita, tashi muje gurin ta." Jahid ya mike da sauri ita kuma dauki hijab dinta ta zura, suna fita motar Amjad na shigowa gidan, yana kwance a bayan mota ya hango Jahid din da granny sun nufi motar sa, duk da cewa Jahud ya fahimce shine bai tsaya ba, da gudu ya fafari motar sumar bar gidan.. Shi kuma Amjad sai dinga tunanin ko wanine babu lafiya cikin iyalin Jahid din, ya dauki granny domin taje ta dubasu. Sam bai kawo komai cikin ranshi ba, ya shiga gida yanayin tozali da sweetheart dinshi ya manta da koma. "Sosai granny take fahimtar da Momy amma ta gagara ganewa da k'arshe ma so tayi tai mata rashin kunya inda take fadin" Kinga Hajiya d'anki ko nawa da zaki dame ni lallai sai na yarda, shin kin Sam irin rashin mutumcin da yarinyar tayi min kuwa, tsinanniyar yarinya mummuna 'yar gidan malam shehu irin wannan har ta kalle mu ni da aminyata tace muna warin dauka da bleecing a i wallahi Jahid ya sake ya auri yarinyar nan sai na tsinke masa." Granny tace"Ki daiyi hakuri Asma'u yarinyar arziki ce Wallahi akasi aka samu kuma hada zuria dasu akwai albarka Hajiya baki San ko akwai rabo tsakininsu ba, sai ki mutu saboda wannan abunda kikayi ubangji baya so." Jin abunda granny tace ne yasa Many zuburowa! Tace"kaji ni da tsohuwar najadu tsohuwar kawai! To wallahi sai dai idan kece zaki mutu,au!! Fatan mutuwa kike mun, aikin banza to wallahi ba yanzu zan mutu ba." Jahid ya Dora hannunsa aka cikin tsantsar tashin hankali da nadamar dauko granny inda yasan wannan cin mutumcin za'ayi mata da bai dauko ta ba, ya zama dole duk son da yake wa Asma'u ya hak'ura da ita, domin yana hango mugun rikici a gaba idan ya aure ta Hausawa suka ce idan so cuta ne hakuri magani ne, nan ya mike ya futa daga parlor a karo na biyu, granny ta mike cike da taikacin da b'acin rai tace"Duk yanda naso nussashe dake kin kasa ganewa har kina Neman kiyiwa danki baki, ni zagin da kikayi min bai dame ni ba, tunda kin kwatanta hali irin na Asma'u da kike cewa bata da tarbiyya Shikkenan na barki lafiya." Momy yaja tsaki da k'arfi tana fadin "Allah ya rakataki gona, nace Umma ta gaida Ayshaaaaas."! Granny ko juyowa batayi ba cike da takaici da damuwa ta samu Mujahid tsaye a gurin yana kiranta, mota ya bude mata ta shiga da sauri suka bar gidan. A hanyarsu ne granny take rarrashin sa da kalamai masu sanyi kana tace " Tunda mahaifiyar ka ta nuna bata so tom shawarar da zan baka ka hak'ura ka kwantar da hankalin guri guda rashin Asma'u ba zai hanaka rayuwa ba insha Allah zaka cigaba da rayuwa Cikin amincin Allah da yardar sa, idan Aure kake so ka sake samun mace wacce zucuyarka ta kwanta maka sai is aura mutukar ta amunce din, wannan shine shawara kayi wa uwarka biyayya." Amjad yace." Granny ban taba nadama akan al'amarin auran nan ba sai yau, da Momy ta ci miki mutumci kawai domin kina so ki fahimtar da ita, insha Allahu na hak'ura da Asmau amma INA Neman wata alfarma agurun ki." Tace" kafad'a komeye insha Allah mutukar INA da iko dashi zanyi maka." Yace." Inaso al'amarin auran nan ya koma kan Amjad ba tare da sani ba inaso ne ranar d'aurin aure yaji bazata !." Granny tace'' hak'ika ka cika Aboki na gari Mujahid kuma idan kayi haka babu shakka ka kyauta min, domin ni kaina ina tunanin matar da zai je ya auro wacce zata kula da baby Aysha tsakani da Allah,Dole sai ita Asma'u da take a matsayin Uwa a gare ta, mungode mutuka da alkairi ka."

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});