Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 28

Chapter 28

Babban Yaro Book 2 Complete Hausa Novel 1,215 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

mutu da wannan rayuwar." Hankalina ya kai k'oluluwar tashi jin abunda Mimi take fad'a ban tsaya naji Abunda Ummansu Munnu take cewa ba na futa daga d'akin. ba tare da sun ganni ba. Diri-diri nake harabar a sibitin kamar wata sabuwar mahaukaciya nayi waje da sauri na, bakin titi na tsya na tari a dai-dai ta sahu, na fad'a mishi idan zai kaini. Har kofar gidan Kawu Yunusa ya aje ni, nace"Bari in shiga ciki in karb'o maka kudinka." Kallo kawai d'an a dai-dai ta ya bita dashi. Ina shiga soron gidan naci karo da Musa zai futa yaci kwalliya cikin shaddar sa, gaishe shi nayi ya amsa yana was he min baki, tare da fadin "Husna kece a gidan nan da Safiya." ? Nace"E h Musa ga mai s dai-dai ta can bashi kudinsa don Allah." Da sauri ya futa ni kuma na shige gidan. Muka gaisa da Baba Mariya a muntunce sai tsokana ta take da amarya amarya ni dai nayi mata shiru, tace"Na ganki duk a furgice ." nace"Kawu yanan ko."? D'aga kanta tayi tare da fadin yana sama tare da d'aya Kawun naki Idiris nasan maganar auran ki suke yi." Mik'ewa nayi ina fadin"Yawwa dama gurinsu Nazo." Babu yabo babu fallasa nayi sallama dakin Kawun namu Wanda ya zame mana waliyi, daga ciki naji muryar shi yana fad'in "Shigo ko waye." Na shiga cikin mamaki suka Bini da kallo shi da Kawu Idiris na zauna muna gaisawa . Kawu Idiris yace." Daga ina kike da sassafe nan." ? Nace"Daga asibiti. " Kawu Yunusa yace."Waye babu lafiya."? Kuka na fashe musu dashi nace"Mimi ce ." Kawu Idiris yace."Mai ya same ta kiyi shiru kiyi mana bayani yanda zamu gamsu." Cikin kuka nace"Aman jini take sosai da kyar likitoci suka shawo kan Matsalar kuma sun ce lallai a bata abunda take so idan ba haka ba zuciyar ta zata buga da ko wane lokaci." Kawu Yunusa yace." To mu wannan ai bs hurumin mu bane zaki zo ki tayar mana da hankali da sanyi safiyar nan." Kawu Yunusa yace." Nima abunda na gani kenan kije ki Sanar da kanin mahaifin ta shine magana." Kallonsu nake cike da mamaki dama halinsu ne rashin zumunci da rashin taimako Sam 'yan uwan Babanmu basu da kara basu da kawaici kowa kansa ya sani da iyalinsa, mun sha wahala sosai bayan mutuwar mahaifinmu shiyasa nake jinjinawa aunt Hauwa ta ko wane fanni domin ta taka muhimmiyar rawa a gare mu, kafin Umma ta tsaya da k'afafunta. Nace." Kawu Wallahi nayi rantsuwa da Allah mutukar baku sanya Ya Aminu ya janye maganar auransa da Mimi ba to nima dole Ku warware nawa Ku mai da wa da Amjadu kudinsa, na aure da kuka karb'a, Mimi ba son Aminu Amjadu take so saboda haka yace. Zai auremu ni da ita Ya Aminu dole ya hak'ura tunda shi namiji ne idan yak'i hak'ura kuma to nima bazan aure shi ba." Jikinsu ne yayi sanyi jin abunda yarinyar take cewa, Suna murna arziki ya shigo musu gida ai ba za su Bari wannan dama ta kubce musu ba shiyasa suka yi ruwa suka yi tsaki kan al'amari idan banda rashin hankalin Asmau da kanta ta zo nema wa kanta kishiya. Babu ruwan su su dai burinsu suga tabbatuwar auran ta da Amjadu ko banza zai kira su Waliyyanta Kuma zai dunga tunawa dasu, duk abunda zai biyo baya babu ruwan su." Kawu Yunusa yace." Wannan ce matsalar taki."? Gyada kaina nayi ina share hawaye na, Yace." Kar ki damu zan samu Aminu in rarrashi shi tunda kinji kin gani shikkenan Allah ya sanya alkairi." Ameen nace na mike hade da yi musu sallama. Tana futa suka cigaba da maganar cike da mamaki sukan ba damuwar su bace hakan burinsu tabbatuwar auran kawai. Ko da na koma asubitin tashin hankali na tarar domin Ya Aminu ya dawo ya tadda Surutun da Mimi take yi tamkar me motsuwar kwakwalwa take sambatu tare da fad'in sunan Amjadu , fad'uwa yayi a gurin hankalinsa a tashe, yana dafe k'irjinsa haki! Yake sosai, likitoci suka shigo dakin suka dinga fada sosai suka yi kora waje, nan suka dauki Aminu da bai San a wace duniyar yake ba, cikin tashin hankali suka yi wani daki dashi ganin yanda yake jawo numfahi da kyar oxygen suka sanya masa. Mimi jikin ya kara rike wa likitan ta kamar ya mammari su Umma haka yake ji ya dinga fada sosai da sosai itama Oxygen din aka sanya mata Dr din yana addu'ar Allah yasa kar jinin ya dawo mutukar jinin ya dawo da zubah to babu shakka sakamakon su ya nuna masa cewar zuciyarta zata iya daina aiki. *11/November/2019* [11/12, 11:13 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO* *Mallakar_BINTA UMAR* *LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA* *49* Hankalin Umma ya kai k'oluluwar tashi inda ta dinga wata irin zufa!! Gabanta yana wata irin fad'uwa su biyu kawai iyayen su suka Haifa ita da k'anwar ta, Aisha maihaifyar Mimi kenan tabbas idan ta rasa Mimi bata da wani Abu da ya dangaci k'anwar ta, Mimi take kallo a matsayin Aisha k'anwar ta, Aminu danta ne dole zata iya sarrafa shi ya hak'ura da Mimi a bata zabin ranta, ko da kuwa Shi Aminu zai rasa tasa rayuwar wannan hukuncin ta yanke, ba tare da bata lokaci ba ta sanya aunt Hauwa ta kira mata Kawu a waya yace gasu nan zuwa asibitin. Sunzo sun tadda badakalar da take faruwa Umma tace Ita ta Riga ta gama yanke hukunci Aminu ya janye auran sa a kan Mimi dole a aura mata Wanda take so. Kawu Yunusa yace." Muma maganar da take tafe damu kenan domin Asma'u taje har gida ta Sanar mana saboda haka tunda taga zata iya shikkenan dama kuma shi yaron Neman auran mutum biyu yazo ita da Mimi saboda haka kan Aminu baza mu bari a rusa wannan auran ba domin mu abun alfarin mu ne, hada jini da Amjadu saboda haka zamu tattashi Aminu." Wannan shawarar ita ce matsaya Babansu Munnu na tsaye bai ce komai ba sai da suka gama magana yace."Idan babu damuwa Aminu yazo ga Munnubiya na bashi sai a d'aura auran rana daya. Kawu Idiris yace." Mungode da wannan karamci zamu jira ya dawo hayyacinsa muji ta bakinsa. 4:35 Aminu ya farka masha Allah nuffashin sa ya dawo dai-dai budar bakinsa "Ina Mimi take kar kice min ta mutu Innalillahi wa'ina ilahi raji'un." Ya fada yana yunk'urin tashi zaune Dr Yayi saurin mai dashi ya kwantar yana rarrashin sa fafur Aminu yak'i zama dole sai an kaishi gurin Mimi, Dr da kansa ya Dora shi keke saboda jikinsa babu k'wari kai tsaye dakin da Mimi take ya nufa da shi. Mimi na kwance sambal hancin ta sakale da oxygen idanunta a rufe Aminu ya tsura mata ido zuciyarsa nayi masa zafi wai yanzu shi Mimi take gudu tafi son bare dashi, hak'ika Allah ya jarrabe shi da kaunar ta tun tana 'yar jaririyar ta, Ashe zan Ga wannan ranar ta bakin ciki, wasu zafafan hawaye ya share cikin zuciyar sa yace ."Ya zama Dole in hak'ura dake Mimi domin

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});