Chapter 11
Chapter 11
gurin da yake kafin ya mike ya shiga gida jikinsa a mutukar sanyaye, ya samu Umma na d'aurin sikari a rumfa zama yayi kusa da ita tare da fadin "Umma kinji gagarimun abunda mutumin nan ya dauko mana kuwa." Umma tace"Wane mutumin ? "Amjadu" Aminu ya fada jikinsa babu k'wari, tace "A ina kangan shi kai." "Yanzu muka gama waya dashi, Wai yana son ya auri Asma'u da Mimi lokaci guda." Umma ta saki ledar da take hannunta tana kallon Aminu cike da mamaki tace"Wannan wace irin magana CE."? Yace." Wallahi haka yace" Shiru tayi tana nazarin maganar daga bisani tace"Mimi da Asma'u Anya hadin yayi kuwa gaskiya Indai Yana so sai da ya zab'i d'aya a cikinsu." Aminu yace"Umma mutum me girma kamar wannan ko mata hudu yace." Zai aura a lokaci guda za'iya ya tsallake gidaje sama da miliyan yazo nan bamu aje ba bamu bawa wani ajiya ba, gaskiya ni bazan iya fada masa haka ba." Umma tace "Zaman kishi tsakanin Asma'u da Mimi akwai kwara Mimi sanyi hali Asma'u wayo da rashin kunya gata itace k'arama bana son abunda zai tab'a zumumcin su." Aminu yace." Sai dai idan sune suka so haka amma in sun hade Kansu babu wata matsala. Umma tace" Shikkenan zanyi magana dasu." Ya Aminu ya mike ya futa jikinsa babu kuzari. Mimi na daki a kwance ni kuma ina bakin rijiya ina wanki Umma ta kwala mana kira, aje sabulan hannuna nayi na amsa hade da cewa "Gani nan zuwa Umma. Ina zama Mimi ta shigo salo-salo Umma tace." Kun San abunda yake faruwa kuwa."? Girgiza kaina nayi, tace" A cikin Ku Wa ya tab'a furtawa Kalmar so." Nace"Umma waye." ? Hararata tayi tace"Wanda kuka sani mana." Kaina sai ya daure kawai domin ban fuskanci abunda take nufi ba." Tace"Ke ya baki KUDI hade da yi miki shopping ke kuma ya baki waya, shine nake tambayar wacece a cikin Ku ya taba cewa wance ina son ki,saboda yau ya bujoro mana da bukatar son ya aure Ku duk Ku biyun." Das!das! Haka gababa ya dinga fad'uwa, baki na rawa nace"Umma ban...ban fahimce ki ba." Mimi ta kalla tare da fadin"Ke dai nasan kin fahimce ni ko."? Mimi ta gyad'a kanta tare da fadin"Na fahimce ki Umma a gaskiya ni dai Kalmar so bata tab'a hadani dashi ba sai da ko ita Asma'u. " harara na banka mata nace"Ki fad'i gaskiya dai ko kinyi maganar aure dashi amma ni meye shafe ni da har zai ce zai aure mu ni dake, babu wata kyakyawar alaka mybe ma duk abunda yayi min saboda kene, Umma ni kam babu abunda ya shiga tsakanina dashi Mimi yake so." Na fada raina a bace. " Umma tace"Yanzu dai ya turo Aminu da sako saboda haka sai kuje Ku sasanta kanku." [11/5, 7:40 AM] .: Tab'e bakina nayi na mike hade da barin gurin. Wankina na cigaba da yi ina tunanin al'amarin lallai ma, wai yana so ya aure mu ni da Mimi kiji sai kace Wanda aka ce masa mun rasa majin aure aiko sama da kasa zata hade bazan aure shi ba, Mimi taje ta aure shi, ni gani nake ma kamar da wata manufa ya shirya hakan Ina kallon Mimi ta futo salo-salo ta shiga dakinmu kallo na bita dashi ina tab'e bakina nace"Kin had'u da aiki babba a rayuwar ki, Ya Aminu ne naga ya shigo cikin gidan da sauri hannunshi rike da wayar Mimi ya nufi dakinmu, babu wayar ya futo, da alama shi yake kiranta. Zuciyata naji babu dad'i naji ina son inji wace hira suke dashi, daurewa kawai nayi na cigaba da wankina, ina jiyo muryar Mimi k'asa-kasa tana magana...... Kwafa! Kawai nayi cikin zuciyata nace"wannan guy shigowar shi cikin al'amari mu ba k'aramin hatsari bane domin zai iya wargatsa mana zumuncin mu." Sai da na gama tsaf! Sannan na shiga dakinmu ina k'okarin cire kayan jikina Mimi ta kalleni baki na rawa tace." Asma'u kin San meye."? Kai tsaye nace"sai kin fada." A hankali tace"Wai Amjadu ne zai zo bayan sallahr Isha'i zai kawo mana tsarabar mu." Ba tare da na kalleta ba nace"zai kawo miki tsaraba dai." Har da ke ai." Girgiza kai nayi nace" ni kam bana son komai nashi, ban sani ba ko sai kunyi aure sannan zan daina jin haushin sa." Tace"Waye ya fada miki zan aure shi." Cike da mamaki nake kallonta na kasa cewa komai ma, na cigaba da saka kayansma tace" bazan Iya hada miji dake ba Asma'u, gwara in hak'ura in bar miki shi." Muryar ta na rawa ta k'arashe maganar. Sai ta bani tausayi mutuka nace"Mimi zaki iya hakuri da ruhin ki Ashe? Zuciyar ki tana mutukar kaunar mutumin nan, idan kikayi haka to zaki jefa kanki a halaka, wallahi in har don ni zakiyi haka, to bari kiji wallahi zan iya sadauakar miki da komai na rayuwata domin ki samu farin ciki, ballanta d'a namiji ki kwantar da hankalin ki, ni ba bakuwar zafi bace, Sam Amjadu baya gabana, a yanzu na bar miki shi zan cigaba da yi miki fatan alkairi har karshen rayuwar ki." Kuka tq fashe dashi hade da rungume ni sosai take kuka nima sai na tsinci kaina da share hawaye tace"Asma'u kin San Allah sai dai in mutu da sonshi mutukar kika ce baza ki aure shi nima na hak'ura gwara soyayyar shi ta zama ajalina." Yanda take fad'ar maganar tana shashshekar kuka hade da wani irin Abu yasa hankalina yayi mugun tashi Mimi kuka take wiwi tana dukan k'irjinta hade da fadin"Me yasa zuciyata zakiyi min haka.? Meyasa kullum kike azabtar dani akan son mutumin nan, Asmau da nasan inda zanje in jefar da zuciya ta da najefar na huta da masifa" tana wani irin kuka ta k'arashe maganar. Hankali a tashe nace"Mimi meye haka? Mai yayi zafi? Kina so ki kashe kanki ne? Kike dukan kirjinki." Cikin kuka tace" Asma'u gwara in mutu akan i n rayu a duniyar nan, kwata-kwata zuciyata ba tayi min adalci ba, Asma'u na san ke Amjadu yake so amma saboda sharrin zuciya kullum sai take fada min karya ne, ni yake so, kinga kuwa wannan zuciyar bata da amfani a gare ni, Tunda tana kokarin sanya min abunda bazan samu ba." Cike da tausayin ta nace" Mimi yaya zaki ce baza ki samu ba, kinga na farko dai mutumin nan ya fad'i kirkin ki da kyawun halin ki kyawun zuciyar ki, ko wannan ma amsa ce ta ki gane cewar yana sonki, ki saka a ranki baki da Miji sai Amjadu insha Allahu zan iya bakin kokarina gurin ganin tabbatuwar auran Ku." Hawaye ne kawai yake zubo mata na sanya gefan zanina INA share mata, da kyar na samu tayi shiru dadin da naji ma Umma ba taji ba yara sun cika gidan suna siyyaya. ********* K'arfe shida dai-dai ya futo cikin kyakyawan shiri yau, shigar manyan kaya yayi wata lafiyayyir galila ce a jikinshi skyblue dinkin babbar Riga da 'yar ciki taji lafiyayyan sirfani na masu hannu da shuni yau mutumin Ku ya sanya hula inda ta kara futo masa da ainihin kyawun sa hade da kwarjinsa, hannunsa daure da agogo shi mai tsada sai zabbuna na azirfa guda uku a ya tsunsa masu wani irin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78