Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 64

Chapter 64

Babban Yaro Book 2 Complete Hausa Novel 1,211 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

muka iya haka muka hakura amma naji babu dad'i a zuciya ta domin naso inga baby nan wallahi ga yanda naji ubanta na fadin kamar si daya da Mimi, Jahid nayi ta kira a waya yak'i dauka saboda yasan zancan dokar asibitin CE, yana ganin kan Asma'u ba zai sanya ya karya ba. Amjad har gida ya kaimu Cikin motarsa, zuciya babu dad'i na futo daga motar ba tare da na jira su Umma da aunt Hauwa ba, barin su nayi tare dashi suna sallama, Ya Aminu ne kawai a gidan dama yasan da dawowar mu tunda aunt Hauwa tayi masa waya tsaf muka tadda gidan, rumfa na zube kan leda na fara kuka. Suka shigo suka same ni a haka aunt tace"Wannan wane irin shirme ne." ? Cikin kuka nace"Aunt don baki San yanda nake ji bane a zuciya wallahi Ashe duk gujewa mutuwa da muke yi akan Mimi tana jika aunt Mimi tasha wahala a rayuwar ta wallahi" aunt tace"Sai hakuri dukanin mai rai mamaci ne addu'a kawai zamu yi mata." Ya Aminu ya shigo dakin yana fadin"Wannan kukan da kike yi kina kara mata azaba ne idan ta fado miki a rai kiyi mata addu'a. " shiru kawai nayi musu. Ko da na koma makaranta ba wani sake ba, kullum muna tare da Munnu muna zancan Mimi da halayen ta na hakuri da ban dariyar ta da saurin kukan ta wani lokacin idan na tuno hae sai na share hawaye sai kawai inyi mata addu'a samun rahamar Allah. Kullum kuwa sai na damu Umma da zancan babyn Mimi nace ta nemi alfarma gurin Amjad ta dauko ta ta raine ta kamar yanda ta raini Mimi, Umma tace wannan kuma nice zanyi hidima tunda nice mamanta a yanzu, nan na dauki a niyar fad'awa Mujahid kudirina kan Baby Aisha, yarinyar da ta zama cikkakiyar mutum domin yanzu tayi k'wari sosai ta cika wataninta na haihuwa, Jahid yace." Zai fad'awa mahaifin ta ko zai amunce, dama ya karb'i babyn sa, yau kwana uku kenan, jin abunda Jahid din yace sai ya d'aga min hankali Ashe har sun bashi baby babu labari mu gamu a zaune kullum muna kwadayin ganinta, to yanzu da ya karb'a wa ya kaiwa? Ni kadai nake tambayar kaina, ina dawowa daga makaranta na fad'awa Umma halin da ake ciki, tace "Aikuwa bai kyauta mana ba, muma ai muna da hakki a kanta, gashi kwana biyu ya daina kiran Aminu a waya balle kusan halin da ake ciki." Nace"Umma to yanzu wa zai kaiwa babyn ma." Umma tace "Kakarshi mana." Shiru na minti biyu nace "Umma kakarshi bata da k'wari don Allah ki amunce a dauko ta." Umma tace"Ai dama bani naki amincewa mutukar zai bamu muna so hakkin sa ne." Nace "Nayiwa Jahid magana zai nemi alfarma a gurin shi." """" Rayuwa kenan duniya babu tabbas yau kwanan Mimi Hamsin da bakwai a karkashin kasa komai yayi farko yana da k'arshe Amjad ya sake ya barwa Allah komai ya tabbatar dukanin Abunda ya same shi daga Allah ne. A halin yanzu ya maida hankalin sa ne gurin k'ara bunk'asa harkokinsa na waje, a cewar sa mu'amula da turawa yanzu ya fara saboda wasun su sun fi muslumin mu amana da tausayi, tunda gashi da Dan uwanshi musulmi aka hada baki dashi gurin cutar shi da izgilanci ga Allah ga manzon sa, yana nan ya sanya matakan tsaro ko ta ina yayi lamfu bunkice yake sosai aka mutanan da suka kulla masa sharri, maganar company kuma tunda sun rusa shi babu wasu kudinsa da zai futo dasu ya saka tada wani, suje kawai Wanda bai ji bari ba zai ji hoho.. Loptop ce a kan cinyar shi yana duba sakkonin da Anthony ya turo mishi tsawon lokuta dama wasu ya bashi amsa wasu bai bashi ba, ya bari ne in yaje can sai suyi maganar. Granny CE ta futo daga dakin ta ta zauna kusa dashi.. Hankalinsa na kan Loptop din bai dago ba yace." Ina Sweetheart yau banji motsin ta ba." Granny tace"Tana gurun Iyami tun safe da tayi mata wanka take bacci." Dariya yayi yace." Wannan Aishar ai rigamammiya ce tafi uwarta fitina." Granny tace"Mai suna Aisha kuka ne da ita ai." Yace." Granny ina tunanin cikin satin nan Zan tafi Chana kuma zan kai wata uku a can insha Allah, amma ina tunanin tafiya in barku fa." Granny tace"Allah ya taimaka ni kam babu wata chana da zan biki to kaji."!! Dariya yayi yace." Shikkenan zamu je da sweetheart d'ina OK." Hararshi tayi tace"Kaje ka bawa wa ita wannan garin ai ku da ku ga zaku iya zuwa." Murmushi yayi kawai ya cigaba da duba lptop d'insa. A hankali tace"Ni ko nace dama akwai wata magana da na yanke a kanka." Gyada kansa yayi tare da fadin"Ina sauraren ki." Tace"Mai zai hana ka nemi auran Hafsatu. Da zan ce ko yarinyar nan Asma'u to amma naga wannan yaron Dan albarka Mujahid yana nemanta ana barin halas Dan kunya ko ba haka ba ne."? Bata fuska yayi had'e da ya mutse ta yace."granny ki k'yaleni in huta tukkuna ni kam yanzu babu maganar aure a gurina sai an kwana biyu sannan. " Tace"Aikuwa dole kayi aure domin shine cikar mutum ka kai munzali kace baza kayi aure ba, baka Isa ba." 'Yar dariya yayi yace." Granny nayi aure har na samu riba mutuwa ta rabani da mata ta, ki k'yale ni na huta tukkuna zanyi amma ba yanzu ba." Tace." Ni kam bazan ta kallon ka a haka ba dole ni nayi maka aure. " dariya yake yana mamakin rigimar ta, yace." Ok kiyi min aure sai in barki da matar wallahi inyi tafiya ta tunda bani na saki ba." Granny ta hau zuba masa masifa, dafe kansa yayi yace." Ina aiki kin hani oh my god."!!! Iyami ce ta shigo da Baby Aisha a goye a bayanta tana motsi, alamun ta tashi. Granny tace" Ta tashi ne."? Iyami tace"Gashinan fa da alama Dadynta take so." Rufe loptp din yayi yana kokarin karb'a baby daga hannun granny sai murmushi yake, yarinya tayi mulmul da ita tayi wata irin kib'a hasken fatarta ya kara futowa Iyami ta iya raino gaskiya sai wani kamshi take yi, tana cikin kayansu na jira jira abun gwanin sha'awa, leb'anshi ya manna a kumcinta yana sakin ajiyar zuciya yace." Momyna 'yar rigima hummmm! Yau ba kuka kenan. "? Kamar yana da magana da babban mutum haka yake yin magana da baby Aisha. Granny tace"Aiki ya same ka kana magana kamar kana magana da babban mutum." Dariya yayi hade da kamo bakin baby yana Dan tsotsa yarinyar ta fara mamular leb'an shi da sauri. 'Yar dariya yayi ya cire bakinsa ya kalli Iyami dake zaune kusa da granny yace." Allah Iyami zanci tarar ki sweet heart dina yunwa take ji ga alamu nan na gani." Iyami tace"Afuwa Uban gida dama yanzu nake so in dama mata madarar ta, kaga ai bacci take kuma sweeh Hart din naka ci ne da ita Wallahi ." Dariya ya kyalkyale dashi jin yanda Iyami take fadi wai sweeh hart. Yace." Ungo ta ki bata bana so tayi kuka yanzu dai kin San halinta." Iyami ta karb'e ta da sauri ta futa...... Wayar shi tayi k'ara

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});