Chapter 20
Chapter 20
ki." Ya kashe wayarsa. Umma na kalla naga tana kallona nasan wayar handsfree ne taji komai Tace "Ki tashi kije su manya mutane basa son jira." Nace"Umma wane irin zance ne wannan k'arfe Tara na dare." Umma tace"Sai kinyi surutun dai ko ki tashi kije Kuma kar ki sake ki futa da wannan kayan na jikin ki, masu kaurin hayak'i Dan dare yayi ma da sai kinyi wanka, ki gyara fuskar ki duk ki goge wannan maikon na fuskar ki, don nasan bs hankaline dake ba sai ki futa haka. Mik'ewa nayi na shiga dakinmu wallahi dai dai Umma tace in sanja kaya amma da bazan sanja ba, material dinmu na anko na dauko na tusa a cikina ina nishi na fesa turare na me saukin kudi goge fuska ta kawai nayi da abun goge hoda na yafa mayafi karami. Takalmi plate na sanya a kafata na futo Umma ta bini da kallo cikin zuciyar ta tana tunanin kayan jikina domin sun futo da sassan jikina, Shiru kawai tayi nace"Umma na tafi." "To ki nutsu dai banda kaifin harshe nasan halin ki." Raina babu dad'i na futa daga gidan ina mamakin kallon da Mimi take Min tunda taga na futo. Dake dare ne kuma babu wuta a gari yasa bansha kallon gurin Samarin layinmu ba. Na karasa har inda motar tasa take fake. Sabuwar mota ce yazo da ita, fara tas! Daga yau ya fara shigar ta sai walwali take motar tayi kyau kuma daga ni zata ja kudi sosai. Cikin zuciyata nace"Kaji dadinka yanda ka samu duniya Allah ya baka lahira." Dake motar bata da duhu yana hangota sosai yake kallonta har ta k'araso ya bude motar tare da fadin"Bisimillah.." Kin shiga nayi na jinga jikin motar tare da fadin"Yau kam bazan shiga motar ka ba, domin bansan inda zaka kaini ba, in ka damu ka futo waje sai ka fada min abunda ya kawo ka." *8/November/2019* [11/9, 8:14 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO* *Mallakar_BINTA UMAR* *LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.* *46* Nafi minti goma da magana banji motsin sa ba, nace"Zan tafi tunda dai baza ka futo ni kam na daina shiga motar ka." Daga ciki naji muryar shi a hankali yace." Ki shigo ciki shi yafi arziki ko kin manta da yanda nake cikin jama'a ? Yanzu zaki zama abun kallo, bayan haka kuma ga sauro a gurin , bana kaunar cizon sauro." Nayi mamakin yanda yayi min magana Cikin kyakyawan lafazi nace" kayi alk'awarin baza ka kaini ko ina ba."? Kai tsaye yace." Eh nayi alk'awari." Motar na shiga wani irin sanyi da k'amshin sa suka cika min hanci. Ina kokarin rufe motar ne ya ziro hannunsa ya rufe jikinmu ya had'u gurin haka. Nace"Ka gani ko."? Kallona Yayi tare da fadin"Me kuma nayi."? Shiru nayi masa ina dauke kaina. Yace." Duk kin sanya sauro ya cika min mota dole a kaita car wash gobe. " Ni dai bance masa komai ba. Gyaran murya yayi tare da fadin"Babu gaisuwa ne."? A hankali nace "Ina wuni."? " Lafiya Lou ya halin ki."? Ya fada yana min wani irin kallo. Kauda kaina nayi zuciya ta tana wani irin bugawa bana son in kalleshi ballanta in rasa kuzari na shiyasa nake kiyayewa yana sanye da kananun kaya As'usuel ya kyau kamar ka sace ka gudu. "Ya jikin Momyna."? Yafad'a idanunsa tsaye a kaina." Nace"Da sauk'i dai." "D'azu kina min magana ban fahimta ba, me yake damunta."? Kai tsaye nace " Ciwon so."? 'Yar dariya yayi hade da Sosa kansa yace." Allah ya bata lafiya, 'yan mata da dama suna fama da wannan lalurar a kaina." Kallonsa hade da bata fuska nace "Naga dariya kake yi kamar babu abunda ya dame ka, kasan kuwa Mimi tana jin jiki." Girgiza kansa yayi yace." Ban sani ba, amma yanzu zan sani muje ki rakani in siyo mata kayan dubiya sai kiyi min jagora gidan naku." Nace." Indai Lemo da ayaba ne kayan dubiyar bakin layinmu ma ana siyarwa." "Ba irinsu zan siyo mata ba." Yafad'a yana wani lumshe min ido tsabar munafurci. Nace"Ni kam babu inda zani in ka shiga ka duba ta haka babu Wanda zai ce maka don me." Siririn sajansa ya shafa hade da yin kasa da murya yace." Momyna tafi k'arfin haka a gurina ke dai kice baza ki rakani bane." Shiru nayi masa kawai Tsira min ido yayi yana kallona. Ta wutsiyar idona nake kallonsa, sai na tsargu na fara kare jikina ina motsu-motsu." Hannunsa ya sanya yana Jan k'aramin mayafina tare da fadin"Wannan gyalen dashi gwara babu domin babu abunda bana gani na jikin ki." Da sauri na buge hannunsa INA hararasa. Bai yi zuciya ba ya kara Jan gyale tare da fadin "Ai danni kikayi kwalliyar sai ki bari in duba da kyau."! Baki na rawa nace" Kayan alk'awari cikawa." Cikin wata 'yar iskar murya yace." Wane alk'awari nayi miki."? Shiru nayi masa ina kara takure jikina jikin motar. Gyaran murya yayi kamar wani munafuki yace." Dan kin samu ma nayi sha'awar kwalliyar ki, 'yan mata nawa ne suke so nayi sha'awar su basa gabana." Tab'e bakina nayi nace." Wannan abunda ya shefe ka ne bai shafe ni ba." Mayafin nawa ya kara ja a karo na uku yace." Kema ya shafe ki, tunda dai zaki aure ni dole kiyi hakuri dasu." Hannuna nasa naja mayafin hade da bata fuskata nace"Abunda kake yi haramun ne, bana so idan ka saba taba jikin 'yan mata to ni ba irinsu bace, bari kaji wani Abu da baka sani ba, Wallahi Sam bana sha'awar auran namiji mazina ci." Kallona Yayi da rai a bace! Nayi saurin kauda kaina Yace." Kawai don nayi niyyar ganin kwaliyyar ki zaki kirani da wannan kalamar." Ban tanka masa ba, ya cigaba da cewa"Kar in kara jin wannan mummunar Kalmar ta futo daga bakin ki, idan zina nake baza kimin addu'a ba? Ta inda Momyna tafi kenan ta iya lafazi da lallami da kalaman soyayya ke ko babu abunda kika iya sai hauka!!." Ya fada a harzuke.! Naji haushin abunda Yace. Nima na kaurara murya ta sosai nace"Ai ba karya nayi maka ba, nima sau nawa kana auna ni, kuma ranar nan a gabana naji kuna waya da budurwar ka, kana yi mata zancan 'yan iska." Yace." To ina ruwan ki da 'yan mata na."? Shiru nayi sai da na fad'i maganar nake da nasani nima kar ya dauka ko sonshi nake. Da sauri nace"Babu ruwana dasu gaskiya ce na fada maka." Shuru yayi min hade da zuba min ido kamar wani tsohon maye. Babu zato naji ya fuzge min mayafi na ya jefa shi kujerar baya. Da sauri na kare k'irjina sanin da nayi duk sun bullutsu ta saman rigata. Matsowa yayi sosai hade da kashe hasken motar tayi duhu sosai. Matseni yayi jikin kujera hade da Dora hannunsa saman k'irjina yana shafawa, A tare muka sauke ajiyar zuciya Cikin wata kasalalliyar murya Yace. " Wannan dai nawa ne ni nasan ni zan iya dasu, ko na aure ki ko ban aure ki, baza ki taba jin dadin wani da namiji ba idan bani ba, saboda haka kin jawowa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78