Chapter 25
Chapter 25
a gaskiya Baba babu mahalukin da zan iya barwa Mimi domin nima idan nayi haka zan iya shiga cikin tashin hankali watak'ila ma nawa yafi nata tunda kowa ya shaida nafi sonta ita bata sona saboda haka ni ina gani kawai daga nan zuwa jini a d'aura mana aure da ita ba sai an jira lokacin da aka sanya ba, idan taji labarin haka nasan dole zata hak'ura ta fawwala Allah kasan dama ance kiyyayyar 'ya mace bata tasiri ina ganin Mimi zata hak'ura ta zauna dani."! Kawu ya gyada kansa yana Nazarin maganar Aminu Yaro Yaro ne, murmushi yayi yace." Aminu kenan, kamar ka manta abunda Dr yace akan Aishatu, Jin labarin d'aurin auranku zai iya sanyawa zucuyarta ta buga gaba daya ta mutu lokaci guda, kaga kuwa wannan sha'awar taka ba abun dubawa bace." Aminu ranshi ya b'aci da jin abunda Kawu yake fada murysrshi a kaurare yace." Kai ya kake ganin za'ayi." Kawu ya kalleshi cike da mamaki jin yana yi masa magana kazar-kazar babu Wani ladabi. Yace." Abunda za'ayi shine mu samawa Aishatu abunda take so domun samun ta da tabbatuwar lafiyar ta. Aminu ya watsa masa wani kallo tare da fadin"Kawu in na fahimce ka anan shine kana so kace min in hak'ura da Mimi in yaso Ku bats Wanda take so kome."? Kai tsaye..... Kawu yace." Shine abunda nake Nufi." Aminu ya guda kansa yana murmushi me ciwo yace." Impossible, bazai tab'a yiwu wa ba Kawu Mimi 'yar kace nima inda kara d'an ka ne nasan baza ka bawa Mimi bare ba gani a zaune, ina so saboda haka yanda aka karb'i kud'in aure na da Mimi to babu mahalukin da ya Isa ya hana tabbatuwar auramu idan ba Wanda ya hallice mu ba." Cike da d'umbun mamaki Kawu yake kallon Aminu ganin yanda yake wani irin huci!! Yace." Aminu ka fahimce ni mana ba wai ina k'in ka ban......... Kafin ya karasa Aminu ya daga masa hannu a fusace.!!! Yace." Kawu ga magana nan ta futo kanunamin bakai ka haife ni b.... Cike da b'acin rai Kawu yace." Rashin kunya zakayi min Aminu. " Daga kafad'a yayi tare da fadin "Babu maganar rashin kunya anan Kawu gaskiya ce ni nayi rantsuwar babu Wanda ya Isa ya hanani auran Mimi." Ganin tsageran cin da Aminu yake masa ne yasa ya fusata shima yace." Aminu indai nine waliyin Aishatu to baza ka aure ta ba." Aikuwa sai ya ingiza Aminu ta inda ya shiga sirfa masa rashin kunya wanda ya jawo hankalimu Kansu dukanimu mu k'araso gurin tare da tambayar ba'asi Abunda Aminu yake yi yayi bala'in konawa Umma rai ta cire hannunta ta zabga masa mari cikin tsawa tace"Na kara jin bakinka a gurinan Aminu sai na tsine maka, a tunanin ka wannan tsagerancin da rashin kunyar da kake yi shine zai sanya a baka auran Mimi ko meye."? Kawu yace." Kyaleshi ya zage ni son ransa lokacin sa ne." Wuce mu yayi tafi can bakin get ya zauna tare da masu gadi Fada sosai Umma take wa Aminu Tace" Haka ake soyayya da hauka Aminu ka futo da son zuciyarka a fili kana ganin mawuyacin halin da yarinyar nan take ciki shine zakaje gwara ta mutu a kan ka janye kudirin ka a kanta, me yasa ita lokacin da ka fad'i har ka kwanta a asibiti tace"Zata aure ka alhalin ga Wanda zuciyar ta take so Mimi yarinya ce me ladabi da gudun b'acin rain wani ta so ta faranta maka ta faran wa zuciyata ba tare da ta damu da nata farin cikin ba, shine yanzu tana cikin halin rai da rayuwa kake mummunan magana a kanta Aminu wannan ba soyayya bace."!!!! Umma ta karasa maganar ta tana haki! Kana ganinta zaka fahimci tana cikin tsananin b'acin rai da damuwa Cikin kuka na futar hayyaci nace"Wallahi tallahi Umma mutukar Ya Aminu bai janye kudirinsa ba nima bazan aure shi ba, sai dai mu zauna a haka, kawai a aura mata Wanda zuciyarta take so ta huta da wannan azabar da take sha." Umma tace." Ki kwantar da hankalin ki insha Allahu Mimi bata da Miji sai Amjadu dole a bawa zuciyarta hakuri abata abunda take so." Ya Aminu ya kalleni ya kalli Umma zuciyarsa nayi masa wani irin ciwo yace." Umma don bani da kudi bani da aikin yi bani da mota bani da babur bani da keken hawa kana bani da kudi a banki kuke mun haka,? Meye laifi na meye? Aibuna anan Zan kula da Mimi zan tsare mutumcin ta zan sanya ta farin ciki! Umma kar Ku kware min baya akan Mimi Ku duba halin da zan shiga a kanta soyayyar ta tana iya kashe ni!!!!! Umma ni danki ne baza ki so wani bayan ni ba, Umma ki dube ni da idanun rahama!! Ki tuna so da kaunar da kike min Umma ki bani Mimi domin itace farin cikin rayuwata."!!!!!!!! Ya k'arashe maganar sa hawaye na zubowa daga idanunsa Umma ta zube a gurin Tare da dafe k'irjinta tana salati aunt Hauwa da Ummansu Munnu suka rike ta hawaye ne ya fara zirarawo daga idanunta muryarta na rawa tace"Ya Allah ka ije mun wannan masifa da ta tun karo ni, Allah ka sanyaya min kasa kawo karshen wannan badak'ala!! Sai hawaye sharrrrrrrr-sharrrrrrrr suka fara zuba a kuncinta. Duk taurin zuciya irin ta aunt Hauwa hawaye ta fara sharewa ganin Umma tana kuka abunda zai sanya Umma kuka ba Karami bane hakuri kurum suke bata Ni ko da sauri na bar gurin bayan na warce wayar Munnu dake tsaye, wani d'an korido na nufa dake Cikin asibitin na fara Neman numbar sa, sai da tayi ringing sai uku ba a dauka ba, Sai ana hudu ne ya dauka muryarsa da yanayin bacci yayi sallamsa da sauri nace." Kanwa ta kar tsami! Kwarna fi ya kwanta. "!!!! Jin muryar yarinyar ya sashi mik'ewa zaune da sauri hade da yaye blanket din jikinshi na ci gaba da cewa " Yanzu haka muna babban asibiti na zana Mimi a kwance rai a hannun Allah bayan tafiyar ka, jini ya tsinke mata ta baki ta hanci!!!! Ta galabaita mutuka duk ta dalilin ka!!! Ina kara fada maka duk abunda ya same ta Kaine sila Kaine! Mujaza!! Mahaifiyar mu ta zubar da hawaye akan haka, mun zubar da hawaye a kan haka, duk wani mai imani ya kalli Halin da Mimi ta shiga a yanzu sai ya tausaya mata, insha Allahu duk wani sharrinka sai ya koma kanka ka cuce mu, ka yaudare mu, Ka azabatar da zuciyar Mimi akan sonka kullum kana fada cewar zaka aure ta, alhalin karya kake!!! Wallahi mutukar ka bari Mimi ta mutu baka yi Wani Abu akai ba nima sai na kashe ka."!!!!!!!!!!! Kamar wata mahaukaciya haka na k'arashe maganar..... Wata irin zufa ce ta keto masa duk da cewar akwai AC a dakin Muryarshi sanyi k'alau yace." Asma'u.!!! " saurin kashe wayar nayi na zube a gurin hade da fashewa da kuka mai cin rai. Mik'ewa yayi da sauri ya duro daga bed din toilet ya nufa ya dauro alwala ya futo yana kallon agogo bango uku shaura na dare, Jallabiya ce a jikinsa sai garan wando ya dauki wata rigar sanyi sa mai hula ya sanya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78