Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 61

Chapter 61

Babban Yaro Book 2 Complete Hausa Novel 1,207 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

wane hali yake ciki. Sunkuyar da kansa yayi cikin tawakalli yace." Allah ya kaimu lafiya Jahid ina cikin halin damuwa ina bukatar rarrashin." Kafadunsa ya dafa yana rarrashin sa da kalamai masu sanyi. Amjadu Rambo ya sanya ya je can *Mai takobi* ya karb'o nau'i kan abunci da abun sha, duk ya sanya ya shiga dasu gurin mu, tsabar damuwa da fargaba bata bari munci komai ba, ko da asubah ruwa kawai muka sha fafur abunci yak'i samun shiga a gurin mu, Ya Aminu dama ya tafi gida ni da Umma ne kawai sai granny Ko da muka yi sallahr asubah bamu koma ba, muna zaune daki daya muna jiran hukuncin ubangji, granny na zaune kan dadduma da carbi a hannu Umma na kwance gefan ta. Itama dai carbin ne a hannunta tana ja, cikin damuwa, ni kam ai fad'ar halin damuwar da nake ciki sai a hankali, a Dan baccin da ya kwashe ni ne nayi mafarkin gani ga Mimi a tsaye a wani gurin tana sanye da wasu fararan kaya duk jikinta fuskar ta dauke da wani irin annuri ta kara haske mutuka, hannu nake mik'a mata tana mik'o min NATA hannun tana min murmushi, so nake in kamo hannunta na kasa gani dai a kusa da ita amma na kasa kamo hannunta, gani nayi ta juya da sauri ba tare da tace min komai ba ta fara d'ago min hannunta kafin in Ankara na nema ta na rasa. Ni da kaina na fassarawa kaina wannan mafarkin tabbas Mimi zata yi nisa da rayuwar mu Mimi zata yi nisa damu. Shine fa tunda na tashi na kasa sukuni ina kwance kan wani k'aramin gado nayi lamo wasu irin hawaye masu zafi suna zubo min. ***** K'arfe bakwai dai-dai Jahid ya shigo a sibitin cikin mota ya tadda Amjad yana bacci a zaune ya bashi tausayi mutuka ya kalli su Rambo dake tsaye jikin motar yace."Kar Wanda ya tashe shi Ku k'yale shi ya samu bacci shima Hutu ne. A gurin shi." Gyada kai suka yi alamun sun amsa. Kai tsaye dakin da Mimi take ya nufa, lokacin mu bamu futo ba, shiyasa bamu ga zuwan shi ba, abun mamaki yana shiga dakin yaga nurses tsaye a kanta d'aya na goge mata baki daya na kokarin gyara gadon, yaji dadin yanda ya same ta, gaisawa yayi dasu, suka futa da sauri, shi kuma ya kalli Mimi fuskarsa a sake yace." Madam ya jikin ki."? A hankali tace"Da sauki." Yace." Me kike ji yana miki ciwo a jikin ki." Cikin ta ta nuna da hannunta." Yace." Kiyi hakuri zaji sauki insha Allahu." Mimi ta gyda kanta, gurin yayi shiru na minti biyu dago kanta tayi, cikin sanyin murya tace"Sun kashe shi ko."!!!? Jahid ya girgiza kansa alamar a'a saboda ya San ko wa take nufi.... Bude baki tayi zata yi magana yace." Ko in kira miki shi ne."? Gyada kanta tayi, ya mike da sauri ya futa, lokacin mun futo, muna zaune a wasu kujeru, granny ce ta tare shi tare da fadin"Kai Mujahid ka futo zigwi-zigwi ko kallon mu naka yi ba kun barmu cikin alhini da tashin hankali ko." Jahid shiru yayi mata kawai ya futa. Mik'ewa tayi tana gyara d'aurin zanin ta tace"Ku tashi mu shiga ciki muna da kafafunmu sai anyi mana iso Ku muje muga halin da take ciki baiwar Allah." Aikuwa bayan ta muka bi, ni da Umma. Mimi na zaune kan bed kanta a kasa hawaye na zurarowa a kuncin ta kuka take sosai, muka shiga, da sauri naje na rungume ta, tare da fashewa da kuka INA fadin "Mimi ALLAH ya saka miki dukanin Wanda ya cuce ki." Rungume ni tayi tana kuka sosai. Umma da granny suka k'araso gurin suna rarrashin mu, mussaman ita Mimi din. Zama nayi kusa da ita hannuna cikin NATA, Yanzu zuciya ta tayi sanyi sosai na yarda mafarki karya ne tun daga Mimi zaune a gaba muna magana da ita..... Dakin suka shigo hade da sallama. Tunda nayi masa kallo guda na dauke kaina ina mamakin yanda hallintun sa suka jurkita mutum Dan gaye Dan kwalisa mai kudi mai kyau mai jiji da kansa amma lokaci guda kamanin sa duk sun sauya ya fyade lokaci guda, fuskarsa Tayi fururu, shi kanshi takalimin dake k'afafun shi na wanka ne, kayan jikinsa ne kawai masu kyau. Kai tsaye gurin Mimi ya nufa ya zauna kusa da ita inda bayana da nashi ya kusa haduwa sai nayi saurin mik'ewa daga gurin, na koma kusa da Umma na tsaya, shi da Mimi kallon juna suke yi sun kasa magana shine ma yayi k'arfin halin fadin "Momy ya jikin ki hope yanzu ba kyajin ko wane irin ciwo ko."? Gyada kanta tayi har yanzu hawaye bai daina zuba mata ba. Sosai yake rarrashin ta da kalamai masu dad'i ko kunyar Umma baya ji har sai da yaga ta saki tana dariya sannan ya daina shima ya saki jikinsa sosai ana hira dashi sama-sama shi da Umma granny na sanya musu baki. Kimanin Rabin a wa yayi ya mike tare da fadin zai je gida yayi wanka zai dawo bayan sallahr azahar. Sallama yayi wa su Umma ni bishi da wani mugun kallo na tsana da kyama ji nake bani da babban makiyi a duniya karma shi saboda guy a fiye son kanshi a duniya. ***** Takardar scanning ta futa Dr Jahid ya shiga damuwa sosai da yaga abunda yake faruwa wato baby girl dake cikin Mimi ta juya ma'ana kwanciyar ta ta sauya daga inda ake bukata tana zaune daram! Cikin Mimi gashi cibiyar ta ta nade mata wuyan ta, amma tana rayuwa a haka Cikin hukuncin Allah, lafiyarta lau, cikin ya nuna wata shida da kwana takwas wato ya shiga wata na bakwai duk wasu hallitu ubangiji ya gama abun shi, wahudun kahar Dole ya kwantar da Mimi a asibiti domin kula da cikin ta da ranar haihuwa, domin kar hankalin su ya tashi ya sanya yak'i fada musu abunda yake faruwa ganin yanda duk suka saki jikinsu har shi Amjad din da ya dakatar da komai na rayuwar sa, yanzu ta lafiyar matar sa yake. Ko da ya fada musu maganar bata gado basu kawo komai ba, har shi Amjad din ya yarda saboda Jahid din yace masa yana so Mimi ta samu cikkakiyar kulawa har ta haihu, shiyasa ya yarda da hakan. Kwananmu bakwai a sibitin Mimi ta warware sosai babu inda bata zuwa, domiin Jahid cewa yayi muna futowa da ita tana zurga zurga saboda shi yana gani kafin lokacin haihuwar tata kwanciyar baby ya dawo dai-dai kamar yanda ake so. Ganin ta warware sosai ya sanya na tafi gida saboda makaranta Mimi bata so tafiya ta ba amma da na rarrashe ta na kawo mata misalai sai ta hak'ura. Umma da Granny ne suke jiyyar ta sai Ummansu Munnu dake zuwa kullum tana kawo musu abunci bayan an sha ruwa, duk da cewa Amjadu yana iya bakin kokari su akan su, komai sai ya sanya an kawo musu na ci da bukatar rayuwa. Ni ma ina zuwa amma ba kullum ba, watarana idan muka taso daga makaranta ni da Munnu sai mu wuce aikuwa Mimi tayi ta murna, ranar yini muke ni da Munnu muna sanya

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});