Chapter 55
Chapter 55
da kai mutumin." Gali yace." Yaron nan fa ya dawo wane shiri zamu yi a kanshi."? Governor yace." Na sani ai duk wani Abu da ya faru a gidan yarin gashi a gabana ina gani, akwai shirin da muke masa ni da su Alhaji Hashimu insha Allahu sai mun rusa shi. Alhaji Gali yace." Yana da kyau hakan , gaya nan ya kawo uban kayan abunci ." dariya governor yayi yace."ka d'ibi iya yanda kake so ka bawa Wanda kake so sauran a zubah a store na gidan, kar ka sake ka sakar mu, ka cuzguna musu abunci sau d'aya nake so a dunga basu haka ruwa ma sau d'aya zasu sha a rana." Alhaji Gali ya saki dariya tare da fadin"Yallab'ai ai ba sai ka fad'a ba, haka ce zata kasance insha Allah. " Dariya suka kyalkyale da ita sannan suka kashe wayoyin su, dukanin su suna cike da farin ciki da annushuwa. Amjadu kuwa bayan futar sa daga gidan prison din kai tsaye gidan marayu suka nufa. Nan ma duk wani Abu da ya sauke gudin prison din haka ya sauke musu, marayu da marasa galihu ranar murna da dad'i duk ya ishe su, sosai kuma yayi Rabon kudi, musaman mata masu raino rainon yara k'anano sosai suka samu kud'in a gurun shi. Sai daf da magariba ya koma gida. Granny da Mimi na zaune a parlor duk suna kallon abunda ya faru a TV. Granny ta hau share hawaye tana tuno iyayen sa , addu'a take masa Allah ya kare shi daga sharrin magauta tabbas idan ya zama shugaba a garin kano za'a huta dashi. Amma Sam bata yi masa sha'awar mulki. ********* K'arfe bakwai ta ranar lititin dai-dai tayi mana a babban hospital din Nasarawa dake jahar kano. Ranar ina da makaranta amma haka Na kashe ta saboda nasan ko naje babu abunda zan iya yi tun jiya nake Cikin halin damuwa INA wa Mimi addu'a Allah yasa ayi lafiya, Umma kuwa kwanan zaune tayi da carbi a hannu, a subar fari aunt hauwa ta iso gida saboda haka gari na waye wa muka nufi asibiti kowanne bakin shi da dauke da addu'a. Muna zaune suka shigo a sibitin Amjadu da granny sai Mimi dake rungume a jikinsa, ta kara yin haske sosai. Tana ganin Umma ta rugu da gudu ta rungume ta hade da fashewa da kuka, Umma ta fara rarrashin ta tana fadin"Mimi kina dauke da da lalura kina gudu, ki daina kuka kinji ko." Cikin kuka Mimi tace"Umma ki YAFE min ko da Zan mutu." Naji gabana ya fad'i jin abunda tace Kallonta nayi nace"Don Allah ki daina mana wannan maganar Mimi." Shiru tayi min ta k'araso gurin aunt Hauwa dake share hawaye rungume ta tayi tana kuka, aunt rarrashin ta take da kalamai masu sanyi. Hada ido muka yi dashi yana yana tsaye jikin kofa Yana kallonmu jikin sa sanye da shadda fara tas! K'afafun shi sanye da takalman me gidan ya tsaya baki , yayi kyau sosai da sosai, Idan ba idona ne yayi kin gizo ba sai naga ya fad'a idanunsa sun zurma ciki, a hankali ya k'araso kusa da Umma hade da Dan risanawa yana gaishe ta. Granny ma k'araso wa tayi tana tsokan Mimi alhalin itama Cikin zuciyar ta daurewa kawai take, tun kafin Suzo take share hawaye: Cikin k'arfin hali aunt Hauwa take rarrashin Mimi hade da karfafa mata gwiwa, shi kam Amjadu suna gama gaisawa da Umma bar gurin. Motar sa ya nufa, ya zauna bayan ya kunna karatun alk'urani, me girma yana saurara Muna zaune aka zo a tafi da Mimi. Duk muka bita da addu'ar samun nasara. K'arfe Biyu da kwata Dr ya futo ya same mu inda muke zaune. Umma ya kalle ta da ta zuba masa ido,Sam ta manta da wata surukutaka dake tsakanin su, tsugunawa yayi suka gaisa a mutum CE. Tace"Ina fatan anyi Lafiya Dr."? Cikin kwantar da hankali yace." Alhmdullahi anyi nasara insha Allahu an samu damar Ciro k'wayar hallitar da izinin ubangiji d'ayan zai cigaba da rayuwa cikin hukuncin Allah kuma zata haife shi lafiya." Ajiyar zuciya Umma ta sauke tana tayi ma Dr godiya duk ta rasa yanda zata yi Sauri kawai nake na idar da sallah ta tun a sujjadar k'arshe nake godewa Allah. Granny da aunt Hauwa baki har kunne sai addu'a suke masa. Ciki ya koma ya futo da wani Abu cikin kwali. Kai tsaye hanyar futa ya nufa. Motar Amjad ya nufa domin yasan yana nan. Yana ganin zuwan Jahid din gurin shi ya futo daga motar yana bin hannunshi da kallo cikin fad'uwar gaba. Bakinsa na rawa yace." Meye wannan."? Jahid yace." Alhmdullahi wannan hallitar ce da aka ciro dole zaka gani sannan ka binne domin ubangji ya soma fidda masa hallita ." Zuciyarsa babu dad'i yace." Jahid Dole sai na gani hummm? Kawai a binne ubangji Allah ya bani wani." Cikin sanyin murya ya fad'i maganar. Ajiye kwalin Jahid yayi ya dafa ka fad'ar Amjad d'in yana fad'in"Colm down Aboki na, ba dole sai ka gani ba, hakkin kane Dole a nuna maka, amma insha Allah ni anan zan sanya a binne shi, ka kwantar da hankalin ka." A tausashe ya k'arasa maganar. Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke yace." Ya jikin Momyna. " ? Dr jahid yace." Alhmdullahi jikinta da sauki hakama babynta insha Allahu zata samu kulawa ka kwantar fa hankalin ka." Hamdala yayi a fili yana godewa Allah yace." Muje in ganta OK." Ganin yanda ya daga hankalin sa yasa Jahid din kasa yi masa musu, domin babu halin yace. Masa ba'a futo da ita ba tukkuna, dole ya jagoran CE shi har dakin da Mimi take kwance. *22/11/2019* [11/23, 10:28 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO* *MALLAKAR_ BINTA UMAR* *LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI* *60* Lokacin da zasu shiga dakin da Mimi take ji nayi kamar in biso domin na k'agara na ganta, Ashe bani kad'ai ba har su Umma, nauyi ya hanata magana granny tace"Muma zamu iya shiga gurin ta ne."? Mujahid yace." A'a granny Ku bari a futo da ita shima Dan dai mijinta ne, kuma in na hanashi zai iya shak'eni ga yadda yake muzurai."! Dariya suka yi ni kam yak'e kurrum nake yi nasan da babu shi tsaf! Mujahid zai shiga dani gurin Mimi. Kusan Mintuna ashir yayi a ciki sannan ya futo domin shi Mujahid din tunda ya raka shi ya futo ya koma bakin aiki. Kallonsa muka yi dukaninmu, Tsayuwar sa ya gyara kusa da kakarshi ya futo da wani farin hankici daga aljihun sa, yana goge fuskar sa. Granny tace"Ya jikin nata ta farko amma."? Girgiza kansa yayi kamar ba yaso yace." Bata farko ba amma dai Jahid yace." Zuwa magariba zata farko insha Allah." Hamdala tayi tana kallon mu cike da farin ciki tace"Kunji abunda Mujahid yace ko. ? Muna sauraren ikon Allah." Umma tace"Shine abun dubawa kuma shine abun godiya." Shiru ne ya ratsa gurin na minti biyu kana yace." Zan wuce ina sa meeting da ma'aikatana
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78