Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 12

Chapter 12

Babban Yaro Book 2 Complete Hausa Novel 1,222 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ado hade da stons kana ganinsu kasan zasu ja kudi, takalmi me gidan ya tsa ne a k'afafun shi kamfanin Gucci Dan Asali yayi kyau har ya gaji inda kasan wani ango, *Ni ko nace ba dole ba za'a tafi neman aure* fuskarsa babu yabo babu fallasa ya futa, bodyguard d'insa suka mike da sauri, hannu kawai ya daga musu ya karb'i key hannun Doh-doh da kanshi ya futo da motar daga inda take mai gadi ya bude masa gate ya futa daga gidan suna daga masa hannu Kai tsaye gidan granny ya nufa, bai shiga gidan ba sai da ya gabatar da sallahr magariba a massalacin dake manne da gidan sannan ya shiga. Kamilar Dattijuwa na zaune kan dadduma da carbi a hannunta tana lazimi da alama ta idar da sallahr ne, zama yayi a kujera Yana jiran ta kammala, minti goma a tsakani ta shafa addu'ar ta, ta kalle shi bayan ta aje carbi tace"Babban mutum." Kallonta yayi cike da mamaki! Tace"Yau dole in kira ka da wannan suna Wannan kwalliyar ta burge ni sosai don har na fara kishin ka tun kafin kaje inda zaka je." Dariya ya sanya tare da fad'in"Ai kuwa sai da kiyi domin babu abunda zai hanani tafiya Neman aure, auran ma na mata biyu kece ta ukun. Kafin in cika so ta hudun. Hararsa tayi tare da fadin"Mace biyu ai bata kama ce ka ba kaji da guda daya, ta Isa." Yace." Ba kin ce zaki shiga kauyika ki samo min maganin k'arfi ba."? Zama ta gyara tana kallonsa tace"K'warai kuwa yau a can muka yini nida Iyami ga wani sassak'e can na karb'o maka Wanda za'a dafa shi da jar kanwa ya zama shine ruwan shanka, insha Allahu mai maganin yace zaka koma kamar zaki gurin k'arfi." Dariya ya kyalkyale da ita Sam! Ya manta da b'acin ran da yake ciki yace." Toum kinga sai in fara Neman aurena da hujja." Mik'ewa tayi tsakanin ta da Allah take fad'in"Ai mutukar zaka diman ci shan maganin matar ka baza tayi takaici ba." Cikin dariya yace." To kawo min na fara sha yanzu ya bi jikina nasan dai already kin had'a min." Tace"Yanzu kuwa a i mikewar da nayi zan dauko maka ne, NASA Iyami ta k'ukkula maka shi a farar Leda kullum ka dinga shan d'aya." Yace" maza ki kawo min uwargina." Bedroom dinta ta nufa, tana tafiya tana kara tisa maganar. Shi kuwa bayan shigewar ta dariya ya kama yana mamaki wai shi Granny zata bawa maganin k'arfi hummm! Yana zaune ta futo dashi cikin Leda viva sabuwa dal, dauru kusan ashirin ya karb'a yana dubawa, dauri daya ya dauko yana sansanawa, cikin haushi da takaici tace"Meye haka kuma zaka haramtashi fa." Cikin dariya yace." In na haramanta ma ai ni nawa ne kuma ni zan sha." Tace" To fasa dauri daya kasha a gabana." Aikuwa ya fasa hade da zukewa yace." Idan cikina yayi ciwo kece kin yadda." Tace"Na yarda wannan maganin bazai saka ciwon ciki ba sai dai ma ya gyara ka." Yace." Naji to zauna muyi magana dake." Granny ta zauna kusa dashi. Yace." Neman aure zanje fa." Granny tace." Alhamdullahi yau Allah ya kawo ni wannan lokacin. " Gyad'a kansa yayi yace." Mata biyu zan aura ya kika gani. " Shiru tayi tana nazari daga bisani tace"Ai Matsalar Ka ce abun ji." Murmushi yayi yace." Kar kiji komai duk zan iya dasu. B'ata fuska tayi tace"to naji amma dai ta biyun Hafsa ce ko."? Yace."Wacece Hafsa kuma."? Tsaki taja tace"Kamanta kenan kana so ka hadani da Innar ka kenan? Dama suna cewa sai abunda nace dakai kake yi baka zumunci dasu dukiyarka baka Mora musu sai dai su ji a gari." Shiru yayi kawai domin shi kanshi ya San baya kyautawa Sam baya ziyartar dangin mahaifiyar sa, sun gani da korafin sun hak'ura dole yanzu ya gyara ko don kada duniya ta zage shi, Granny ya kalla yace." Yanzu yaya kike so ayi. "? Zama ta gyara tare da fadin" Kaje ka nemi auran Hafsa yarinyar na da kirki kuma tana sonka." Ya mutsa fuskar sa yayi wannan bukatar ta granny baza ta yi wu ba, yace." Kiyi hakuri Granny bana so ayi Abu daga baya azo ana da an sani kin fi kowa sanin halina bana rufa-rufa yarinyar bata yi min ba, zan dai yi kokari gurin ganin naje mun gaisa dasu kuma zanyi musu alkairi sosai." Ajiyar zuciya ta sauke tare da fadin "Shikkenan to Ubangiji Allah yayi maka zab'i na alkairi " "Ameen yace yana kallon agogon dake daure a hannunsa. Mik'ewa yayi yace." Insha Allahu komai ya dai-dai ta zamu je ki ga kawayen naki ko kuma in ce kishiyoyin naki." Tace",Allah ya kaimu yanzu ma ace dasu ina gaishe su." Har ya futa ta bishi a bays hannuta rike da ledar magani tace." Ka manta kuma." Shiru yayi yana nazari,hannu ya mik'a ya karb'a sukayi sallama ta koma gida Mota ya bude ya zura ledar maganin kusa dashi ya zauna sosai hade da kunna motar mai gadi ne ya mik'e da sauri ya bude masa Gate ya futa daga gidan. Kai tsaye,....... Gidansu Asma'u ya nufa. *5/November/2019* [11/6, 5:13 PM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO* *Mallakar_BINTA UMAR* *LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.* *42* Yana tafe cikin mota yana sauraron wak'ar Joy mutumin shi, gyada kansa yake da alamun Yana jin dadin wak'ar, sai da ya kusa shiga unguwar tasu ne ya kira Mimi a waya, lokacin muna zaune a tsakar gida bayan mun gama cin abunci muna ta fama da wasu shegun cinna ku da suka addabe mu, dama duk lokacin damuna haka suke futowa a gidan ta cikin ramuka suyi ta cizon mu. Wani ne ya cije ni a hannuna ina ta faman sosawa hade da haska gurin da toch din wayar Mimi neman sa nake in kashe, kira naga ya shigo wayar *Heartbeat* abunda na gani kenan, siririn tsaki naja hade da mik'a mata wayar ta karba hade da tashi daga gurin, Umma ta bita da kallo tana girgiza kanta. Minti uku sai ga ta ta futo da wayar a hannu tana sink'e kai Umma tace "Waye ya kira ki harda barin gurin."? A hankali tace" Amajad ne, yazo Umma." Sakin fuska tayi tace" To masha Allahu, alamu sun nuna ke yake so, tunda gashi ya kira ki a waya yazo zance maza je ki shirya Ubangiji Allah ya sanya alkairi." Umma ta k'arashe maganar cike da murna da farin ciki. Mimi ko kunya ta shiga dakinmu da sauri, sai abun ya bani mamaki ganin d'azu take kuka tana cewa ta hak'ura dashi ta barmin amma dubi yanda take rawar kafa saboda zuwan sa. Ni dai shiru nayi kawai, har ta futo Cikin shiri sai zabga kamshi take. Tace"Umma sai na dawo." Umma tace." Ki gaishe shi da kyau kuma ki iya ladabi da biyyaya." Tace"To tana k'okarin futa sai farin ciki take. Hira muke da Umma sama-sama nake jin ta domin a lokacin bana cikin hayyacina wani irin lami bakina yayi sai kace mace mai yaron ciki haka nake jin wata irin kasala da sagewar gwiwa jiki

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});