Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 41

Chapter 41

Babban Yaro Book 2 Complete Hausa Novel 1,215 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

suka Isa badawa yayi parking a inda ya saba, kallonta yayi da lumsassun idonsa saurin dauke kanta tayi, ya saki murmushi tare da fadin "Kije ki huta kinji ko gobe ina jiran ki, kiyi min tanadi me kyau." Kofar motar ya bude mata hade da sumbatar hannunta guda, Mimi ta futa a hankali tana d'aga masa hannu, motar yaja ya bar gurin, dake da wutar NEPA a unguwar yasa matasa basu watse ba. Mimi ta tsallaka ta shiga lokonsu cikin sauri Hira muke da su Munnu amma hankalina da tunani na nakan Mimi gamin har k'arfe goma sha biyu saura bata shigo gidan nan ba, Umma ma ta leko dakin kusan sau uku tana tambayar ta shigo, aunt Hauwa ce ta kwantar da hankalin ta, tunda dai tana gurin mijinta,Ni da Munnu hirar muke Mimi ta shigo da sallama, duk muka bita da kallo, 'yar dariya tayi tare da fadin'Meye daga shigowa ta zaku zuba min ido."? Tsaki naja ina d'an hararata nace." Mimi dubi lokaci fa ke ko tsoro bakya ji, bakya ce masa dare yayi." Maryam dake danne-danne a waya tace "Wane irin tsoro tana tare da mijinta." Munnu tace "Nima dai abunda na gani kenan." Tab'e bakina nayi kawai ina kallonta ta tsallako har inda nake zaune k'amshin turaran sa ya buge ni, domin duk jikin Mimi k'amshin masifaffan turaran sa take, d'an rungume ta da yayi, sai naji zuciya babu dad'i wani irin kallo nake mata cike da zargi ina tunanin ko wani Abu ya shiga tsakanin ta dashi, tunda nasan halinsa ba hakuri ne dashi ba, mik'ewa nayi na futa daga dakin domin ji nayi wani irin fleelings na taso min jin k'amshin turaran sa sai na dunga tuno da salon soyayyar shi, Uwar dakin Umma na shifa duk mutane kwance a rumfa na tsallake su, kwanciya nayi kan gadon ta, gefan aunt Hauwa wacce take bacci sosai nasan gajiya ce." Lumshe idona nayi ina addu'ar kar Allah ya dora min tashin sha'awa ta a wannan daran nasan zan shiga mugun hali ga jama'a a gidan. **** Shima bashi bangaran damuwa da tsanani gajiya su suka dame shi, don haka yana shiga part dinshi yayi wanka ya futo parlor ya kwanta kan doguwar kujera lokaci guda bacci ya dauke shi, mai cike da mafarkai bar katai. **** Washe gari da kuncin zuciya na tashi har 'yan buki suka so su gane ganin naki walwala kamar jiya yasa suka dame ni da tambaya dole na sake na cigaba da wurda da mutane kamar yanda na saba. K'arfe bakwai dai-dai motoci sun fi ashirin kofar gidanmu da bakin layinmu duk na d'aukar amarya ne da 'yan uwanta kowa sai da ya samu guri wasu ma basuyi niyyar zuwa ba, mussaman makotanmu amma saboda su kashe kwarkwatar idonsu yasa suka dinga futowa daga gidan jansu su da gayyar 'yayansu suna fadin"Hali Yayi yau Dole suje suga gidan *Young millionaire* Estate din sai da ya kusa cika da mutane sai hauka suke da ihu hade da k'auyanci aikuwa karnuka na rufe a gurinsu suka dinga haushi sosai, saboda ganin sabon Abu. Kowa fadin albarka cin bakinsa yake game da kyau da tsaruwar gidansa ni da Munnu da ita kanta Mimi gidan ba bakonmu bane, saboda haka bamu damu ba, amma dai naga sauye-sauye a parlor ba kamar zuwana na baya ba. Mimi kuka take sosai da sosai ta rirrike Aunt Hauwa wacce take kuka a fakaice,ji nayi idanuna na kokarin kawo ruwa da sauri na fuce daga dakin, Umma kuwa dama kin zuwa tayi domin ba k'aramin artabu aka sha da ita da Mimi ba, tana kuka Mimi na kuka aka futo da ita. Da kyar mutane suka futa daga gidan ko wacce tana jin ina ma itace a cikin gidan Mimi mussaman 'yan matan gurin. Munnu da Mimi kuka suke sosai, naja tsaki tare da fadin"Dallah Munnu ki tashi mu tafi ki rabu da ita." Mimi ta dago kanta tana kallona cikin hawaye take fadin "Haka zaka ce, ko ? Shine kika munafurce ni wato kin San bada ke aka d'aura auranan ba, kukayi min shiru ni yanzu yaya za'ayi na iya rayuwa ba tare dake ba." Kuka take sosai, nace"Haka Allah ya nufa kiyi hakuri mu zamu tafi." Tashi Tayi da gudu taje ta kulle kofar hade da tsayawa jikin kofar tana kuka, ni da Munnu muka bita da kallon mamaki! Nace" zaki bata kwalliyar taki tun kafin angon yazo." Cikin kuka tace"Asma'u baki yi min adalci ba, yanzu ke idan aka ce ki tafi ki barni a gidan nan sai ki tafi ki barni." Dariya ta bani sosai nace"Mimi mata nawa akai wa aure suka zauna su kadai kema kiyu hakuri dama mace 'yar haka CE." Tace"Ni dai na fada miki babu inda zaku je Wallahi." Tun muna d'aukar abun da wasa har mu ka dawo rarrashin Mimi amma kememe ta ki bude mana kofa, agogon dake manne a dakin na kalla k'arfe goma da kwata nace" Mimi dubi lokaci don girman Allah ki bude Mana kofa." Ki tayi, Munnu ta kwanta kan gado tare da fadin""Ki k'yaleta dole idan angon yazo komai abunta mu tafi, gwara mu d'ana gadon amarya." Bude bakina nayi zanyi magana naji muryar shi k'asa kasa yana kiran Mimi da "Momyna" yana kokarin bude kofar. Da sauri na janye ta daga jikin kofar na zaunar da ita kan bed din hade da rufe mata jikinta. Jan kofar yake yana kiran sunanta a hankali na gyara fuskata sosai naje na bude hade da juyawa. Idonshi yayi masa tozali da bayan Asma'u tana tafiya, take yaji yana nema ya fadin saboda abunda ya tsone masa ido, saurin kauda kansa yayi ya shiga dakin sosai hade da rufe kofar, babu yabo babu fallasa ya kalleni tare da fadin"Me ya hana Ku tafiya."? Idona tsaye kanshi yana sanye da jallabiya me ruwan tuka, fuskar shi fayau da ita, nace"Mimi ce ta hana mu tafiya amma tunda kazo zamu tafi yanzu.." Na fada ina kokarin futa, Munnu ta mike ta itama tana YAFE mayafin ta Da wani mugun gudu Mimi tayo kaina hade da rungume ni muka kusa fad'uwa ni da ita kuka take sosai tana fadin"Wallahi babu inda zaki je." Cike da mamaki nake kallonta kuka take haik'an sai naji tausayin ta ya kama ni da gaske murya ta ta karye tana rawa nace"Wai meye haka Mimi wannan abunda kike ba dai-dai bane gaskiya ni sake ni don Allah."! Kin sakina tayi ta cukyukuye min mayafi har d'ankwalin kaina na cire wa yalwatacciyar suman kaina ta bayyana, banyi ki tso ba, tunda aka wanke min kai sai na tattarashi guri guda na Daure da k'aton ribbom. Takaicin ta ya kamani, kokarin nake in janyo mayafina in rufe kaina dashi ganin yanda Yayi tsaye a kanmu hade da kura mana ido, kafin in Ankara mayafin ya fad'i kasa saboda yanda take rikeni rai a bace nace ja Tsaki tare da fadin"Ki sake dallah."!!! Ki Tayi har ilahi yau tana kuka. A hankali ya karasa kusa dasu, ya sanya hannunsa yana kokarin janye Mimi tana kara rungume ni kamar cingum, nima nawa b'angaran kokari nake in kwace kaina mussaman yanda nake jin hucin nuffashin sa kusa dani hade da k'amshin sa, yayi yayi ya janye Mimi taki

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});