Chapter 18
Chapter 18
ta karba ta sha kadan. Nace "ki kwanta kiyi bacci zakiji sassauci. Kwanciya tayi tana lumshe idonta Sai dana ga bacci ya dauke ta sannan nima na kwanta ina sak'e-sak'e Cikin zuciyata. Bacci ya soma fuzgata naji kiran waya *haetbeat* tsaki naja na dauki wayar na kashe gaba d'ayan ta domin shi nake mutukar jin haushi a ganina duk shine ya jawo mana wannan masifar. Tun farko da bai nunawa Mimi yana sonta ba, ina ganin duk haka baza ta faru ba. Da tune-tune bacci b'arawo ya kwashe ni. ****** B'angaran Amjadu kuwa, tun bayan da Wakilansa suka zo suka Sanar masa da cewar An bashi guda cikin 'yan Matan da yake so ya aura sai gaban shi ya fad'i ya tunini ko Mimi ce, shine dalilin da yasa ya tambaye su kud'in wacce a ka karb'a a cikinsu nan Kawunsa yace." *Asma'u* yaji dadin haka don haka kafin su tafi sai da yayi musu kyauta ta mussaman. Shirye-shiryen bude company ya kammala yau saura kwana biyu gari ya dauka kafufin yad'a labarai in ka bude zancan kenan *Ranar Juma'a Biyu ga watan bakwai za'a bude shaharrarn company nan wato AmjaduAbulAbbas materials* za'ayi bononza a ranar abun dubu daya Dari biya abun dubu goma dubi biyar. Mutanan gari sun kunzige kudinsu suna jiran ranar domin su je su kwaso garab'asa. *** Washe gari muka tashi da jiki a sanyaye Mimi ta rame lokaci guda, shi ko Ya Aminu dama tunda Kawu Yunusa ya Sanar dashi cewar an fasa karb'ar kud'in Mimi ya watsake ko da ya tashi da safe tamkar Wanda bai yi ciwo ba, yanzu Mimi CE abun tausayi so ya tasa ta a gaba. Da kyar na rarrashe ta ta Karya kummalo Umma ta tsaya bakin kofar mu tana fadin "Menene wai naji kuna takkadama."? Zuciyata tace kawai ki fadawa Umma ko menene ko Allah zai sanya ta fahimta." Kaina a kasa nace"Umma ina ganin wa....Shiru nayi na kasa magana. Umma tace." Meye kika yi shiru."? Bakina na rawa nace"Umma don Allah Ya Aminu ya janye kudirin sa a kan Mimi akwai cutar wa a ciki, ya kamata Mimi a bata zabin zuciyarta Ya Aminu Namiji ne shi zai iya jure komai kinga Mimi ko yarinya ce mai karanci shekaru gata kuma mace." Shiru Umma tayi tana nazarin magana ta. Ajiyar zuciya ta sauke a hankali tace"Kin yi gaskiya Asma'u ni ma zuciyata batayi na'am da haka ba, saboda ina gudun zagin jama'ar gari tunda duk sun San komai Da Aminu da ke da Mimi duk daya kuke a gurina babu Wanda zan ce nafi so, amma kina ji da bakin ki tace ta amunce da Aminu kuma ko jiya Kawun Ku ya maimata min maganar babu gudu babu ja da baya tunda sunyi magana da mahaifin ta a waya yace ya bashi wuka da nama, Babansu Munnu ma har dashi cikin maganar kin ga bani da ta cewa." Nace "Umma kina da ta cewa mana don Allah ki sanya Ya Aminu ya janye magana.....kafin in karasa naji saukar Mari a kuncina Ya Aminu ne tsaye a kaina yana wani irin huci! Yace." Kina so naci ubanki Asma'u, wato kina zu ga Umma kina zuga Mimi kan su bujirewa Bukatata ko me? Ni kinsan halin da Zan shiga idan na rasa ta, ko kinsan irin son da nake mata, mutukar ina Raye a duniyar nan bani da mata sai Mimi, dake da ita kuje kuyi abunda zakuyi akin gama ya Riga ya gama." Yana gama maganar shi ya fuce daga gidan a fusace! Umma barin gurin tayi ni da Mimi mukayi shuru muna sak'e-sak'e A hankali naji tace"Asma'u don Allah kar ki kara wata magana kan al'amarin nan, kinji tunda dai kince zaki taya ni addu'a tom na gode miki.". Murya na rawa take maganar Nima naji zuciyata ta karye nace"Mimi sai dai idan gani nayi am d'aura muku aure da Aminu shine zan daina magana domin nasan ki nayi a banza ne, bakin alkami ya bushe, amma magana kan al'amarin yanzu na fara." Shiru tayi tans kallona. Mik'ewa nayi na futa daga dakin zuciya nayi min zafi! *RANA BATA KARYA* Manyan attajirai da manya manyan 'yan boko 'yan siyasa masu mak'ami daban-daban Sarkin Kano sarkin Zazzau Sarki Katsina Jama'ar gari tsakunsu da kwarkatar su, sun hallara a wannan guri. Hayaniya ce ta tsananta tare Da jiniya wannan ya tabbatar min da cewa me girma governor ne ya iso bani kadai ba, duk wani Wanda yasan da akwai dabi tsakanin *Amjadu* da me girma *Governor* sai da yayi mamaki, tuni jama'ar gari suka fara ihu!! Suna fadin abunda ransu yake so ga me girma governor. Ko kunya babu me girma governor ya futo daga mota tare da jamarsa ya dinga ratsa jama'a Yana daga musu hannu hade da washe musu baki wai shi lallai ga governor tsagerun matasa masu goyon bayan Amjadu suka sanya ihu!! Da dariya suna fadin abun da yayi musu kan governor din, wasu na fadin"Ba mayi!!!! Sai da 'yan sanda suka tsawa tar sannan hayaniyar ta lafafa, can gurin da aka tanadar wa manyan baki governor ya nufa, police na biye dashi a baya domin sun tsorata da irin ihun da jama'ar gari sukeyi, Sai da suka ga ya zauna sannan suka koma gefe suka tsaya da bundigun su a hannu. Can na hango Mai citta shida abokanan shi, sai zare ido suke. Limamin babban massalacin jama'a na garin kano ne ya tashi ya bude taro da addu'a yayi karatun alkur'ani me girma sannan daya baya daya manya baki suka fara jawabi kowa yana yaba kwazo da jajircewa irin ta Amajdu 'Yan jarida a gurin baza su kirgu ba, domin wasu jamar gari na gida kowa na gaban TV Wanda bashi dashi kuma kunne shi mak'ale da waya ko redio yana saurara. Lokacin da Amjadu ya futo zai yi Jawabi Ihu!! Jama'ar gari suka sanya tare da fadin"Sai kayi fari me farar aniya ka iya ka huta *AmjaduAbulAbas* muna biye da kai insha Allahu *2004* taka ce sai ka zama shugabanmu." Ihu! Kawai suke, sun hana aji bayanin da yake, da kyar jami'an tsaro suka shawo Kansu suka yi shiru. *Amjadu* yayi jawabi me gamsarwa jawabin da ya ratsa zukatan al'umma Su Kansu manyan gurin sun jinjina masa kuma sunyi masa fatan alkairi.mai Martaba Sarki yaji dad'i sosai da samun hazikin Yaro a garin shi yana mutukar alfahiri da shi. K'arfe goma sha biyu da rabi taro ya watse saboda ranar juma'a ce za'a tafi massalaci, nan Amjadu ya bada sanarwar cewa jamar gari suje massalaci su dawo bayan an idar da sallahr za'a bude company daga nan har zuwa goma na dare. Haka akayi kuwa bayan an sakko jama'a sukayi ta tururwa company suna kwasar garabasa.Sai k'arfe daya na dare sannan aka samu saukin Jama'a. ***** Duk abunda yake faruwa a gari muna da labarin shi munji a redio Kuma mun gani a TV dake ranar sun bar mana wuta, abun mamaki Mimi yini tayi tana farin ciki. Amjadu ya sha addu'a gurin Umma, aunty Hauwa ma ba abar ta a baya ba, kusan a dai-dai ta sahu guda tayo da kayan da bata koma gidan ta ba sai bayan sallahr Isha'i. Ni ko tunda nayi masa kallon farko a TV ban sake
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78