Chapter 17
Chapter 17
barmin shi ko in bar miki shi, Amjadu Mijin ki ne ki kwantar da hankalin ki." Shuru tayi ba ta sake cewa komai ba. Minti goma tsakani wayarta tayi kara dauka tayi tana lumshe ido na na tabbatar da cewar shine ya kira ta, mik'ewa nayi na fuce daga dakin domin bana son inji hirar da zasuyi ballantana i n shiga damuwa. Sai bayan Sallah la'asar Umma ta dawo gidan, jikinta duk babu k'wari tace" Asmau Zuba min ruwa inyi Alwala a hanya la'asar tayi min." Da sauri na zuba mata na mik'a mata ina nazarin ta, har ta shige band'aki Dakinmu na shiga jikina a sanyaye a zuciyata nace Akwai matsala gaskiya tunda naga Umma ta shigo gidan nan jikinta babu k'wari. Kusan Rabin awa da shigowar ta ta kwala mana kira. Ni da Mimi muka amsa a nutse muka Isa Rumfar, tana zaune da carbi a hannunta tace"Duk Ku zauna muyi magana." Zama mukayi ko wacce da Abunda take saka wa. Carbin ta aje ta kallemu tare da fadin "Babban al'amari ne yake tunkaro mu dani da Ku, ina so kuyi min adalci kuyiwa kanku a adalci bana son zumuncin Ku ya lalace saboda duk inda akace kishi to sai anyi shi ko ciki daya kuka futo Yanzu daga gidan Yunusa nake Wannan yaron da yake Neman Ku da aure tun safe ya turo magabatan sa, da kud'in aure harda sadaki yace." Nan da wata guda yake so, ayi komai a gama. Kawu Yunusa ya amsa musu hade da karb'ar dukiyar auran, kafin in futo daga gidan Aminu yaje da maganar shi ta cewar yana son auran ki." Tafad'a tana nuna Mimi da hannu, a cewar sa tun kina yarinya yake sonki ya ki fada ne kawai saboda yana ganin baza ki fi k'arfin sa ba, sai Kuma gashi lokaci guda wanki hula na Neman ya kaishi dare. Kawu Yunusa yace magana ta wuce tunda har ya bari aka karb'i kud'in auran ki. Sai dai yayi hakuri kawai. Yanzu halin da ake ciki yana babban asibiti na Malam Aminu domin fad'uwa yayi a gurin har na tawo bai dawo dai-dai ba." Umma ta k'arashe maganar ta zuciyar ta babu dad'i. Nace"Umma me yasa Ya Aminu bai yi magana da wuri ba har sai da ya bari aka karb'i kud'in auran ta, to ai itama Mimin. Zata shiga wani hali Kuma jiya mun gama magana da Amjadu cewar ya janye aurena saboda rashin dacewar haka, Mimi zai aura kuma daga baya azo ana kace nace." Umma tayi shiru fuskarta cike da alhini. A hankali Mimi tace." Umma ki kwantar da hankalin ki, Indai akan sona Yaya Aminu ya suma har ta kaishi ga kwanciya a asibiti insha Allahu ni zan share miki hawaye Dama nike son Amjadu bashi ba Asma'u yake so tuntuni zuciyata takasa yardar min da haka, Umma zan auri Ya Aminu ki kwantar da hankalin ki." Umma ta share hawayen ta, tace"A'a Mimi bazan miki dole ba bayan an kawo kud'in auran ki saboda son kaina ince ban yarda ba ga Wanda nake so ki aura duniya sai ta zage ni mutanan gari su dinga fadin"Don bani na haife ki ba shiyasa nake miki bakin cikin shiga cikin daula bayan haka kuma zuciyar ki tana son Amjadu idan nayi haka ban miki adalci ba, dole Aminu shine zai janye kudurinsa." Kuka Mimi ta sanya hade da rungume Umma tana fadin "Wallahi Umma da gaske nake babu abunda zaki nema a duniyar nan ban yi miki ba, mutukar ina dashi, Na hak'ura da Amjadu zan auri Ya Aminu." Cikin kuka ta k'arashe maganar. Rungume ta Umma tayi tana kuka, nima naji k'walla ta cika min ido nace"Umma yaushe zamu je asubitin ."? Je ki d'aura abunci da sauri ana idar da sallahr magariba sai muje." Mik'ewa nayi na nufi kicin. *7/November/2019* [11/8, 11:36 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO* Mallakar_BINTA UMAR LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA. 44 A gurguje na kammala dafa abunci shinkafa da faduka nayi wacce taji allayyahu da albasa, Bayan mun idar da sallahr magariba ne muna shirye-shiryen tafiya sai muka ji sallama Umma ta futo da sauri Yaya Aminu ne da Musa da Kawu Yunusa suka shigo, Umma tace"Kaddai an sallame shi." Kawu Musa yace." Gashinan kina gani dama nace Zai farfad'o Suma yayi." Ya Aminu ya zauna kan tabarma hade da dafe kansa. Nida Mimi muka futo muka tsaitsaya Dariya nake wa Ya Aminu ganin yadda ya fyad'e lokaci guda. Sallama Kawu Yunusa yayi suka tafi ni da Musa kuwa babu Wanda ya kula kowa. Umma tace"Maza je ki kawo masa abunci." Kicin na nufa da saurina. Mimi ta zauna gefansa tana yi masa ya jiki. Abunci na kawo na aje gabanshi Naje na dauko ruwa pure watar babu sanyi,yace." Kije ki siyo min me sanyi." Umma ta mik'o min ashirin tare da fadin"Ki siyo guda hudu. Hijab din Umma na zura na futa daga gidan da sauri Ya Aminu bai ci abincin sosai ba ya aje cokalin ya mike ya bar gurin. Duk muka bishi da kallo. Umma tace"Cuta ta samu manya ." murmushi nayi kawai Mimi kuwa tashi tayi simi-simi ta shige dakinmu Nida Umma bamuyi hirar arziki ba muka tashi Ina shiga dakinmu na tadda Mimi ta juya baya tana Kuka harda shashsheka. Cikin mamaki nace"Mimi kuka kike yi."? Banza tayi min Da sauri naje na birkitota sai naga idonta yayi mugun ja sai ajiyar zuciya take. Zama nayi kusa da ita hade da rike hannunta nace"Mimi nasan kin amsawa Umma ne domin ki kwantar mata da hankali. Nasan bakya son Ya Aminu Amjadu kike so Mimi me zai sa baza kiyi wa kanki gata ba zaki jefa kanki cikin mummunan hali. Kinsan bakya son Ya Aminu me yasa kika amsawa Umma." Hannuna ta rike tamau! Naji jikinta sai karkarwa yake Tace." Asma'u na rasa yanda zanyi da zuciyata nayi-nayi incere son Amjadu abun yaci tura ji nake kamar zan mutu Mimi zuciyata tana azabtar dani kan abunda bazan samu ba, don girman Allah ki taya ni da addu'a zuciya tabar cutar dani, soyayyar da nakewa Amjadu Allah ya cire min ta gaba daya ta koma kan Ya Aminu." Kuka nasa saboda tausayin ta tabbas so bala'i ne hannunta NA rike dake yin wani irin karkarwa nace"Mimi zan sanya ki a adduata in sha Allahu, kinga na farko ke kika cuci kanki d'azu da Umma tayi miki maganar Aminu sai ki nuna rashin amincewar ki, tom kinga daga baya baza kije mata da wata magana ba. Zan cigaba da taya ki addu'a Ubangiji Allah ya yaye miki ya zab'a miki mafi alkairi." Sosai take kuka ina rarrashinta Sai kuma naji ta fara wani irin tari!! Na mike da sauri na dauko mata ruwa D'ago ta nayi na fara bata, Tana shan ruwan tana tari da idonta yayi jazur Cire ledar ruwan nayi na bugun bayan ta. Tare da yi mata sannu. Dana ga tarin yak'i sauk'i futa nayi da sauri na dauko gishiri a kicin na zo na Dan gwala mata a baki. Tafi minti goma tanayi sannan ya lafa. Sai haki! Take. Ruwan na mike mata
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78