Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 68

Chapter 68

Babban Yaro Book 2 Complete Hausa Novel 1,213 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

muke yi da ita kawai naji wani mugun kamshi ya bak'unci hancina sawun tafiya naji na kalli kofar shigowa da sauri, wasu hamshakan mata ne suka shigo cikin ya tsine fuska sukayi sallama, na d'ago Cikin nutsuwa nake amsa musu, Hajiya Fatima ta kalleni ya a mutse tace"Da'alama kece "Asma'u ko."? Babu walwala a tare dani nace" Nice." Kallon banza tayi min ta wani ya mutse fuskar ta had'e da tofar da miyau! "She is ugly girl!!." Ta fad'a tana kallon Momyn Jahid dake bin tsakar Gidanmu da kallo kamar Wanda take Neman wani Abu.... Wani irin tsinkewar zuciya naji lokacin da tafad'i min wannan Kalmar kallo nake binsu dashi cikin mamaki!! Momy Jahid ta kalleni a wulakance tace"Ke! Ina uwarki kwad'ayyaya gurun ta nazo ni." Umms ta futo tana fad'in "Asma'u ke da waye ne."? Cikin takaici da jin haushi nace "Umma wad'annan sakarkarun matan ne suka shigo mana gida babu sallama ko wacce tana fama ra karnin bleecing sune har suke kiran wani da mummuna."! Momy Jahid ta kawo min wani bahagon mari tare da fadin" Ke don ubanki kin San kuwa ni wacece a gari nan. "? Kaucewa nayi da sauri ina fadin " Sanin ko ke wacece bai dame ni ba nasan dai ke macace mara tarbiyya mace mai izgil...... Kafin in karasa Umma ta gwab'e min bakina tare da fad'in"Asma'u baki da hankali ko."? Nace. " Umma kin..... Tsawa tw buga min tare da fadin",wallahi in bakiyi shiru ba ranki zai b'aci a gurina."!!Momy Mujahid tace "Ki k'yaleta ta zageni da kyau! Nagode Allah da ya nuna min halin ki tun kafin Dana ya aure ki dama jama'ar gari na fadin haka a kanki,to bari kuji gargadi na daku da babban murya tun wuri Ku janye jikin Ku domin har indai nice mahaifiyar Mujahid wallahi bazai aure ki ba bazan hada jini da talakawa fakirai irin Ku ba, mutsiyata kawai." Mamaki ne ya lullub'e ni jin Ashe da da mahaifiyar Jahid nake magana naji tsoro da kunya sosai amma lokaci guda naji wata irin muguwar tsanar matar domin a rayuwata na tsani masu kudi marasa kaunar talaka ya rab'e su. Cikin daki na shige cike da takaici a fili nace "Wallahi kinci darajar Mujahid ne kawai." Ashe taji duk da k'asa kasa nayi maganar aikuwa naji tana fad'in"Da kin sani kin dake ni kamar yanda kikayi NIYYA marakunyar yarinya kawai. " Umma kuwa hakuri kawai take basu Hajiya Fatima ta daka mata wata irin tsawa "Dallah rufe mana baki."? Umma ta rike hab'a cike da mamaki! Hajiya Fatima ta cigaba Da cewa" DUk laifin naki ne ai hausawa suka ce ido na mudu ba yasan k'ima, in banda abunki ina mu INA Ku kwadayi ne ya rud'e ku kuma kinyi a banza domin dai d'anmu bazai auri yarinyar Ku ba." Umma taji zafin maganar da Hajiya Fatima ta fad'a to dake kowa na da nashi hankalin, sai ta share kawai tace "Shi aure nufi ne daga Allah idan Mujahid shine mijin Asma'u babu mahalukin da ya isa ya hana, idan kuma bashi bane Allah ne masa ni don haka Ku kwantar da hankalin Ku." Momy Jahid ta Ciro d'aurarrun kudi cikin jakar ta dauri uku ta watsa ma Umma a jiki cikin izgili tace"Ki tofar da bakin miyau na bakin ki domun kinyi sab'o Wallahi Mujahid bazai auri yarki ba mutukar ina Raye. "!!! A fusace taja hannun Hjy Fatima suka futa daga gidan. Umma ta shigo inda nake tana fad'in" Ikon Allah Ashe haka wasu masu kud'in suke? Ashe mahaifiyar Mujahid bata da kirki shikam yaron kirki dashi lallai albasa bata tayi halin ruwa ba." Nace Umma ki k'yaleta badai Jahid ne bata so na aura tom ni. Kuma sai na aure shi sai inga ya zata yi."! Umma tac"A'a ni bana yi miki sha'awar auran shi tunda uwarsa bata so ko anyi anyi auran ma to ba dad'i zakiji ba, kowa ya shaida cewar matar shi mutuniyar kirki ce kingani ke babu Matsalar kishiya tunda ta amunce ko ka bata amunce mijinta ya aure ki ba tom Allah da manzon sa, sun hallasta amma gaskiya matar nan ta bani tsoro." Nace"Umma ki kwantar da hankalin ki, kamar yanda kika fad'a cewa aure nufi ne na ubangiji to ni ina nan kan bakana Wallahi babu gudu babu ja da baya sai dai in Jahid din ne yace ya janye maganar aure na tom sai in hak'ura. " Umma tace "To Allah ya zab'a abunda yafi alkairi dai." Amin nace zuciyata duk babu dad'i. Kuka sosai Momyn tasa take da kyar ya shawo kanta tayi shiru yace." Ki fada min ko menene Mommy" Tace"Wai ni yau ka kajawo wa zagi a gurin wadanda basu isa ba, Mujahid yau matar da kake Neman auranta ta zage ni ta kirani karuwa wai mai bleecing sai ta kara fashewa da kuka sosai har da dafe kanta." Jahid ya sunkuyar da kansa cike da mamaki anya kuwa Asma'u zata iya zagin Momyn sa kamar yanda ta fad'a to wai ma shin a ina suka had'u da juna ne.? *27/11/2019* [11/28, 7:55 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO* *MALLAKAR_ BINTA UMAR* *LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI* *66* Mujahid ya cigaba da rarrashin Momyn sa har sai da tayi shiru tukkuna ya kalleta a nutsu yace."Momy wai ina kika ga Asma'u da har tayi miki rashin kunya nifa abun nan ya bani mamaki."! Cikin fusata Momy tace"Naga kamar kana shakka ne Jahid har kana titsiyeni ka tambaye ni, to gidansu nasa aka kaini domin in gargade ta ta fita harkar ka domin naga mayu ne kana zaune da matar ka ta kirki ka je ka kwasowa kanka kaska shine fa ta yi mana wankin babban bargo nida Hajiya Fatima." Mujahid yayi kasa da dansa cikin mamaki jin wai momy gidansu Asma'u taje to in hakane Ashe itace ta jawowa kanta raina yasan halin Momyn sa da zubda girma mybe taje tayi wulakancin da ta saba ne. Tace "Saboda haka in dai nice mahaifiyar ka ban yarda k auri yarinyar ba, shida shiru yayi mata har sanda ta kare fad'an ta yayi mata sallama ya tafi gida. To ko da yaje gida ma matarshi kasa gane kansa tayi dama 'yan kwanakin nan haka yake mata duk ya sauya kwayenta nace mata dama idan namiji zai kara aure canza hali yake, ita dai tunda ta hada masa abunci sai ta shige d'akinta domin ta lura kamar zamanta a kusa dashu baya so. Jahid kuwa ba wani ci abunci da yawa ba, ta kwanta duguwar kujera yana tunanin ala'amri lokacin yi wayar su nayi ya kirata. Lokacin ina zaune ina yin game a wayata naga kiransa dama na tsammaci haka, Muka gaisa kamar yanda muka saba kana ya d'ora da maganar shi kamar haka" Asma'u wai da gaske Momyna tazo gidanmu."? Nace"Babu wai Mujahid Momynka tazo gidanmu. " shiru yayi na minti biyu yace."Ki fada mun gaskiyar Abunda ya faru." Nace"Jahid Momyn ka tazo tayi mana cin mutumci sosai takai har sai

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});