Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 14

Chapter 14

Babban Yaro Book 2 Complete Hausa Novel 1,216 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ya hallice shi a haka. " Gyada kansa yayi tare da fad'in"Wannan ke yake damu, kiyi abunda na umarce ki kafin in Riga goma." Cikin daga murya ya fad'i maganar. Jin nayi shiru ne yasa ya damk'i gashin kaina hade da ja da mugun k'arfi !! Ihu! Na kurma ina fad'in"Zan y......Fuzgar gashin Yayi da k'arfi yace." Oya! Ce ne *Amjadu* kayi hakuri sau goma sha biyu nake so ki fada." Rintse idona nayi ina cije bakina na fara fad'ar *Amjadu kayi hakuri bazan k'ara ba.!"* sai fa na fad'i haka sau goma sha biyu kamar yanda ya umarce ni. Babu sauk'i a muryarsa yace." Duk naga shirme da kika rafka naga irin rashin mutumcin da kika tsula a gurin party ku , to ki sani ma Sam! Bakiyi wani kyau ba, kullum kina kiran kanki da Me aji mace mai daraja to duk baki amsa wannan sunan ba, *Momyna* ita za'a kira da wannan sunan." Shiru yayi na minti biyu ya cigaba da cewa "Momyna ita yafi dacewar na aura a tsakanin Ku, to kuma sai d'azu wanki Aminu yake rokona kan in hada in aure Ku gaba d'aya, cewar kin tayar da hankalin ki, ke ni kadai kike so, hake ko ba haka bane."? Kallonsa nayi cike da mamaki anya Ya Aminu zai fada masa haka.? Wata zuciyar tace" Tsaf Ya Aminu zai iya fada masa haka saboda daman ba shiri kuke dashi ba." A d'age na kalleshi ina ya mutse fuskata nace"Sai dai Mimi don da ita kuka fi dacewa amma ni ko maza sun k'are bana jin zan aure ka gwara in k'are rayuwata a haka." Miskilin murmushi yayi bai ce komai ba ya sake ni, hijabina na dauka ina kokarin sanyawa naga ya tada motar nace"Ina zaka kaini."? Ko kallo ban ishe shi ba, ya figi motar da gudu.! Da sauri na sanya hannu guda na rike sitiyarin motar murya ta na rawa nace"Ka mayar dani gida don girman Allah." Ko kallona bai yi ba, ya cigaba da fafura gudu, kuka sosai na sanya tsoro ya shige ni ganin fuskarsa murtuk!! Nace"Wai me nayi maka ne kake kokarin wulakantani ? Ita Mimi meya sa baka yi mata abunda kake min. " Shiru babu Amsa, yanzu tsoron gida nake da tsoron dukan da Yaya Aminu zai yi min. Hannunsa na rike tamau! Ina rokanshi motar ta fara gargada! A fusace! Ya fuzge hannuna had'e da yarfa min mari." Cike da mamaki na dafe kuncina ina kallonsa... Da Jan ido ya kalle ni tare da fad'in"Ki shiga hankalin ki." Shiru nayi tsoro yana shigata. Gudu yake sosai kan kwalta, naga mun wuce Jambulo wajan gidan shi ya mik'e titin BUK bakina na rawa nace"Kayi hakuri." Hankalinsa na kan driving ki kallona bai yi ba. Rimin Gata muka shiga sosai, yayi parking dai-dai wani k'aton gidan mai Haske ko ina jama'a na ta shiga da motocin su Suna shan mai. Da sauri naga wani mai aikacin ya nufo mu jikinsa sanye da Uniporm orange da tambarin sunan mai gidan mai yana k'araso wa na ga jikinsa rigarsa an sanya *A&A Amjadu Mai nasara feturolium* nace Ashe har gidan mai ne dashi, cikin turanci naji suna maganar Sam ban fuskanci komai ba na dai ga mutumin ya juya ya tafi da sauri! Minti biyar sai ga mutumin shida wani, sai da suka k'araso sannan naso na gane wanene. Gaba na ne ya fad'i ganin Abokin Shamsu wato Abba gana, yayi tsuru-tsuru, Bude kofar motar Yayi hade da umar tarsa ya shiga Abba gana ya shiga motar ba tare da gaddama ba. Shi kuma ma'aikacin ya koma gurin akinshi Juyo wa yayi yana kallonsa, muryarsa babu wasa yace." Malam meye sunan ka? Kuma meye ya kawo ka wannan jahar."? Abba yace." Sunana Abba Gana ni mutumin mai duguri ne, yau sati na biyu a jahar kano, Nazo Neman kudi." Gyada kansa yayi murya a cunkushe yace." Kasan wannan yarinyar."? Naji gabana ya buga damm!!! Shiru Abbah yayi, tsawa ya buga masa tare da fadin" Answer me." Baki na rawa Abba yace." Banga fuskarta ba Yallab'ai." Cikin wata irin kyara da hantara yace." Ki juya masa fuskar ki ya kalle ki."!!!! Da sauri na juya muka hada ido da Abbah Wanda tun ranar party mu bamu sake had'uwa dashi ba. Da sauri Abba yace." Na Santa sosai Yallab'ai. " "Good."! Yafad'a yana jin jina kansa. Bakina na rawa nace" A ina ka sanni da har kake cewa kayi min farin San.....ban k'arasa ba, ya gwab'e min bakina da gwiwar hannusa. Dafe bakina nayi ina kallonsa hawaye na zubo min. Kallona yake shima fuskar sa babu sauk'i. Minfi minti biyu a haka sannan ya juya da kaurarriyar murya yace." Abba kana son ta ko."? Abba yace." K'warai kuwa Yallab'ai. " Gyada kansa yayi yace."Zaka aure ta ni zan tsaya maka a kan komai zan baka gida akin yi da duk abun bukata." Abba ya dinga godiya tsakanin sa da Allah, yace." Kana iya tafiya"Abba ya fara kokarin bude motar sai kuma ya daka ta tare da juyo wa Cikin sauri yace." Yallab'ai nagode k'warai da wannan karamcin naka, hak'ika idan ana samun mutane irin Ku to da talakwa sunji dadin su, amma ka yafe min hak'ika yanzu na kara tabbatar da cewar Asma'u matar manya CE, nagode da karamcin ka, Asma'u da kai ta dace Yallab'ai. " Wani kallo Amjadu ya watsa masa yace." Bayan kun gama wasan soyayyar da ita zaka ce dani ta dace. Tab'e bakinsa yayi yana girgiza kansa yace." Ni nafi k'arfin socond hand, kawai idan baka so in bawa wani." Abbah yayi shiru yana tunani daga bisani yace." To Yallab'ai duk yanda kayi dai-dai ne." 'Yar dariya yayi yace." Yanzu kayi magana guy kaje kawai ka fara shiri." Simi-simi Abbah ya bar gurin yana mamakin meye manufar sa kan haka, yarinyar da yayi-yayi ta bashi numbar waya tak'i yau ita za a bashi, shi ba Yaro bane yana kallon tsantsar so hade da kishi a idon sa, addu'a yake Allah yasa kar ya auna shi garinsu dama jarabar fad'an da ake ne yasa ya biyo Shamsu tunda dukanin su iyayen su sun mutu. Kunna motar yayi muka fara tafiya. Da gefan ido ya kalleni tare da fad'in"Ko kiyi min shiru ko kuma in sauke ki anan." Cikin kuka nace"Allah kad'ai na mik'a masa kuka na akan ka, ka zame min bala'i ka shiga rayuwa ta, me na tsare maka a duniyar nan, da kake kokarin tozar ta ni." Cikin zafin zuciya yace." Kika tozarta kanki dai! Ni gata nake so nayi miki saboda na lura da yanda bagalar ki take, kar ki dauko abun kunya domin baki da juriya, nace zan rufa miki asiri in aure ki kin ce bakya so, tom naje gurin sauranyin naki da Kuka gama rungume-rumgume dashi zan taimake Ku, shine kike min kuka harda hada ni da Allah, me kike so ayi miki."? Murya ta a shak'e nace"Idan na dauko abun kunya meye damuwar ka? Na farko dai dani da kai bamu had'a dangartakar komai ba, babu wata alak'a a tsakanimu,saboda haka baka da damuwa da wannan....ka tse ni yayi ta hanyar fadin"Sai kace ba musulumi ba, wato kina so Allah ya kama ni kenan ? Idan kika je kika dauko zunubi

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});