Chapter 51
Chapter 51
ne, shine zaku zumar mun da mutumci, ni d'an maula ne."!? Ya fada da wata irin tsawa.! Mamaki ya kamani jin wata irin magana tana futowa daga bakinsa, dama alkairi yana koma wa sharri ? Me ya kawo maula cikin taimako na tabbata Mujahid bada wata NIYYA ya taimake Mimi ba sai dai hakkin makota ka. Shashshekar kukan Mimi muka ji nida granny sai hakuri take bashi shi kuma yana kara fusata sai hayaniya yake mata cike da rashin tausayi. Cike da b'acin rai granny ta mike tana fadin"Wannan rashin hakuri dame yayi kama? Daga zuwan ka, ka fara fad'a ki tausayi babu, wato kai duk irin abun da akai maka na taimako baka gani." Dakin ta bude ta shiga tana cigaba da fad'an ta. Mimi tace"Don Allah kayi hakuri wallahi ba laifi na bane." Da sauri yace." Dama nasan ba laifin ki bane nasan me zuga ki, duk abunda kike yi tunda da kunne na naji." Granny tace"Kai ko daga dawo wa zaka soma tashin hankali ka duba halin da take ci ki mana, kila da bama gidan dukan ta zaka yi ko."? Ranshi a bace Yace. " granny a gaban ki ake shigo min da namiji gida bananan,duk da cewa makoci na ne, amma shigowar shi cikin gidana bashi da wani amfani mutukar bani na kawo shi ba, kuma nasan dalilin da yake kawo shi gidana,kune kuke ganin taimako ne yake kawo shi ni za'a rainawa hankali."! Ya k'arashe maganar sa cikin hayaniya. Duk ina jinsa, a zuciya ta nace"Ikon Allah daga taimako ya koma tashin hankali, mik'ewa nayi da sauri na nufi bedroom din Mimi domin in fara had'a kayana zama bai ganni ba. Granny rarrashin Mimi take sosai ganin yanda take wani irin haki! Ya tsorata sosai, ta zauna kusa da ita tana fadin "Kiyi hakuri ki daina kuka shi namiji ba'ayi masa haka, kinga yanzu kin nuna masa langon ki." Ita dai Mimi hawaye kawai take sharewa tana mamakin jarabar mijin nata . Shi kam Amjad tuni ya bar dakin. Ko da ya futo yaso ya samu Asma'u a zaune ya wanke ta tas sai yaga bata gurin, k'wafa yayi a fili yace."Zamu hadu dake kema." Parlor ya zauna hade da Dora kafa daya kan daya ya k'urawa TV ido sai faman huci yake. Futowa nayi daga bedroom din bayan na gama hada kayana,kawai na ganshi zaune da har zan koma ciki kawai na dake sosai Nazo na gifta shi zan nufi kicin, k'afar shi ya sanya ya tad'o tata cike da mugunta Taga-taga nayi zan fad'i da sauri na rike hannun kujera, sai ya sanya hannunsa guda da k'arfi ya buge min hannuna na fad'a jikinsa kaina ya daki k'irjinsa. Kafin inyi wani yunkuri ya ture ni daga jikinsa hade da Jan tsaki, yana min wani irin kallo. Kamar zan fashe da kuka na mike tsaye hade da d'aukar dankwalina da ya cire na d'aura. Murya na rawa nace"Allah ya Isa wallahi." Zuba min ido yayi yana kallona. K'irjina nayi saurin kalla ganin shi yake kallo, saman breast dina duk sun futo dama kaida ne hakan. Tsaki naja nace"Iskanci a cikin gidan aure Allah ya raba mu da irin auran wannan mazan." Kicin din na wuce da sauri ina hard'ewa nasan kallona yake yi. Dauke kansa yayi bayan shigowar ta har yanzu ya rasa wane irin hukunci zai yi ma yarinyar . Tsayuwa nayi tsakiyar kicin din ina tunanin abunda ya kawo ni, minti biyu na tuna Mimi nake so inyi wa miyar ogon da hanta, kullum nake mata taci da bread ko gurasa domin su kadai take iya ci,sai wainar fulawa, gurara sa, Mujahid ne yake jigilar kawo mata, in bashi ba, Umma ta aiko mata. Cikin sauri na fara had'a abun bukata, Allah-Allah nake in gama in bar gidan. Ina tsaka da Yanka hanta ya fad'o kicin din. Saboda tsoro saura kadan in yanke hannuna. Jarumta na aro na daure fuska ta tamau.! Cikin yanayin tafiyar shi ya k'araso inda nake tsaye. Ya kalleni shekeke tare da fad'in "Mara kunya Nazo ki maimata min zagin da kika yi min." Cike da mamaki nake kallon shi, zallahr fitina na hango a kwayar idon shi, shiru nayi masa na cigaba da abunda nake yi. Fuzgo ni yayi da sauri bisa tsautsayi knife din hannuna ta yanke ni, a Dan ya tsaya. Da sauri na aje ta ina yarfar da hannun Cikin azabar zafi, sai cije bakina nake. Gurin yarfar da hannun nawa duk na bata mishi kayan jikinsa. Ko a jikinsa, zare min ido yayi yace." Wane d'an iskan ne, yace ki shigo min da saurayin ki gidana." K'walla ce take kokarin zubo min, ga zafin da nake ciki ga jarabar sa. Shiru nayi ina kallonsa, yace." Zaki daina kallona ko sai na tsone miki ido! Nace"Wane shegen ne yasa ki shigo min da wancan banzan gida, ko an fada miki kowa ma irin ki ne."! Murya ta na rawa nace"Kullum baka da zance sai gida-gida dai gida-gida wai meye a cikin gidan ne? Da har kake ihu! Ina ce duk gida sunan shi gida mutukar za'a shiga a kwanta a cikinsa, sannan za'ayi kashi da futsari a cikinsa, ko da ko gidan bunu ne Wanda aka yi da karare sunan shi, gida kuma bashi da maraba da Wannan da kake magana a kan sa."! Mari! Ya kai mata a fusace! Yace." Ni kike kokarin fad'awa magana Cikin gidana, na fad'a gidana idan kinyi zuciya kar ki kara zuwa balantana kiyi min shirme dama rashin zuciya ne, tuntuni na fad'a miki bana son ganin k'afar ki a gidana ko. Ba haka ba."!? Ya fada cikin sigar rashin mutumci. Cikin mugun takaicin sa nace"Tabbas gida gidan ka ne, kuma dole inzo gidan nan,tunda 'yar uwata na cikin sa, da bata cikin gidan kai kanka kasan babu abunda zai had'a ni da kai." Tsaki yaja ya nuna ni da Dan ya tsaya "Wallahi wannan ne na farko da k'arshe a gurin ki ko da wasa kar ki kara shigo min da wani banza cikin gidana." Cikin sigar kuntatawa nace"Mutum da kake magana akan shi ni yafi min daraja a kan ka, so ina mutukar jin ciwo idan ka zage shi." A kufule yace." Owk don Allah kiyi gangancin sake shigo min dashi gida, Wallahi ke dashi sai na daure Ku! Duk iskancin da zakiyi kije kiyi shi a waje ya fi miki sauk'i ba sai kin kawo min gardi gida ba."!! Wani irin kallo nayi masa sai naga duk ya wani burkuce sai hura hanci yake! Nasan na kular dashi Nace"Allah sarki My Jahid hummm yanda ka dauke shi shi ba haka yake ba, a tunani na kai zaka yi shaidar shi, tunda ka rigani sanin sa, wallahi tunda nake dashi ko gyalena bai tab'a rikewa ba, balle har ta ja shi ga tab'a jikina."! A hasale! Yace." Me kike nufi."? Shiru nayi mishi ina kokarin barin gurin. Jawo ni yayi da sauri ya matse jikin bango, muka fara kallon juna ni dashi. Murya ta na rawa nace"Kasan da wannan abun da kake aikata wa haramun ne ko? Idan da Kayi min iskanci son ranka yanzu ka tab'a ni ka tab'a haram! Kana auran 'yar uwata." Sam! Baya cikin hayyacin sa, idonsa na can wuyan ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78