Chapter 74
Chapter 74
tace"Wallahi maganar ki gaskiya ce Allah ya kyauta." Nace "Ni Abunda yake damuna Abu daya ne aurana da Jahid wallahi yanzu abun tsoro yake bani ina jin tsoron abunda zanje in Tarar."! Insha Allahu alkairi zaki yadda ke dai ki cigaba da yin addu'a.'a" nace "Nagode Munnu." Da Wannan hirarar muka isa gida. ******* Amjad zaune a harami ya d'aga hannunwan sa sama sai kwararo addu'a yake, yana zubar da hawaye ni kaina ya mugun bani tausayi, ya kai Rabin awa cikin wannan halin kana ya shafa addu'ar ya mike a nutse ya dauki daddumar sa da glass d'insa dake aje a gefe ya nufi mazaunin sa, ko da ya isa ba zauna ba toilet ya nufa cikin kuzari yati wanka ya fito fes dashi kasamcewar ana zafi bai shafa mai ba, sai ya shafe jikinsa da turare ya sanya wasu ubansu parkinsan ash coulor hade da wata hula mai kamar net fara tasa da ita, takalmi mai gidan yatsa yayi amfani dashi ya d'aura tsaddan a gogon shi, kana ya manna farin tabarau din shi a fuskarshi, sai ya kara wani uban kyau, kasancewar ya Tara kasumba bai yi aski ba, sai abin ya bada sha'awa Amjadu ya saje da larabawan saudia domun duk kwakwar mutum bazai tab'a cewa ba balarabe bane ga yanayin fatarsa lufluf domin har tafi ta wani balaraben goge wa fuskarsa babu walwala a dauki wayoyin shi hade da wata k'aramar haka irin ta matafiya, kulle dakin yayi da key ya sauka k'asa. Amjad ya nufin koma wa gida Cikin iyalinsa bayan yaje dakin Allah yayi addu'a ga iyayen sa dashi kansa da sauran alumar musulmi. Yana jirgi ya kira su Rambo ya Sanar musu gashinan kan hanya take suka wuce airport domin tarar sa, Granny ya kira a waya ya fada mata, tace"Amma kayi mana bazata! Mai kake so a girka ma." ? Murmushi yayi yace." Granny kuyi min Dambu da zogale." Dariya tasa tana fadin "Kasamu k'ato Allah ya kawo ka Lafiya." Kashe wayar tayi tana kiran Iyami. Tace" maza a shirya dambu mai kyau ga k'ato nan kam hanya." Iyami tace"Wallahi baby ce take kuka har yanzu taki hak'ura kawai tana wasa sai ta fashe da kuka." Dariya granny tasa tace"Tana tuno uwarta ne, jeki dauko min ita kije kiyi aikin ki." Da sauri Iyami ta dauko baby dake kuka har da majina. Granny ta mik'a hannu tana son ta karbe ta ta make kafad'a wai baza ta zo ba, dariya tayi tana fadin"Kaga ja'ira dole kuwa komai kukan ki kiyi shiru Ubanki na kan hanya. Tace iyami aje ta kije kiyi aikin ki." Iyami ta ajeta a kasan gurin ta nufi kicin da sauri. Lokacin baby ta tsandare da kuka, babu shiri granny ta dauke ta ta Goya Tana zagaye parlor da ita, Tunda ya doso kofar parlor yake jin kukan sweetheart dinshi yaji ranshi ya sosu da sauri ya shiga ciki hade da sallama k'asa_kasa granny ta amsa tana masa barka da zuwa, mamaki yake yi ganin baby a bayan granny a goye amma taba kuka, wayoyinsa ya zube kan teble din gaban shi ya fara kokarin daukar babyn da Granny take kokarin kwance ta, yace." Wai mai akayi mata ne take kuka tun kafin na shigo nake jiyo ihun ta." Granny tace"Sheganta ka ce kawai wallahi tun da taje gurun uwarta tayi kwana biyu Shikkenan ta dawo mana da rigima Don da kyar ma ta yarda da iyami, nu kuwa sai nayi da gaske nake daukar ta." Ya gane inda maganar Granny ta dosa, zama yayi cikin kujera yana goge mata fuska da hakincin sa, yace"Granny nifa bana ganin laifin kowa sai naki ke da kika dauke ta kika basu." Cike da jin haushi yayi maganar. Granny tace"To ka dawo ko zaka fara iyayin naka to me kake nufi iyayenta sunzo su dauke ta sai in hanasu ni kam ban iya wannan k'ek'e da k'ek'en ba irin naka." Baice komai ba ya sanye leb'anshi na k'asa bakin ta, kamar yanda yake mata tana jin jira, aikuwa ta kama tsotsa yarinyar bata manta ba. Kallon ta yake yana jin wani irin tausayin ta cikin zuciyarsa duk sanda zai kalleta sai ya tuna masa da Wife dinshi Mimi ko da yaje Saudia duk Rabin addu'ar shi tata ce. Baby Aysha ta fara lumshe ido kalaman bacco still leb'anshi take tsotsa kad'an kad'an har bacci ya rinjayeta ta saki. Ajiyar zuciya ya sauke ya rungume ta tsam a jikinsa tare da fad'in"Iyami ta gyara mata gurin kwanciya tayi bacci."! Granny ta bude baki zata kwalawa Iyami kira kamar yanda ta saba. Da sauri ya d'aga mata hannu yana yamutse fuska da ido ya nuna mata baby wai kar ta tashe ta. Tsaki granny yaja ta mike daga gurin. Da kanta taje ta gyara mata gurin kwanciya ta dawo zata karb'i ta kamar kurma haka ya zama Mik'ewa yayi ba tare da ya bata babyn ba ya nufi bedroom d'insa da Yarinyar granny tayi sakaro da baki, tana fad'in"On ni naga iyayi da feleke a ka dawo din zaka fara nuna mana iyakarmu ni da Iyami komai mukayi bamu iya ba hummm! Allah ya sawak'e maka." Ni da Munnu ne zaune a Uwar dakin aunty Hauwa ta sanya muku tsuguna cikin wani dogon bokitin na k'arfe inda ta sanya wata k'aramar tukunyar k'asa da garwashin wuta had'e da wani mugun turare da wasu saiwowi masu wani irin kamshi, kullemu tayi a dakin har da Dan mukkuli, tsaki babu irin wannan banyi ba, a ganina ni budurwa CE ba bazawara ba, mai zasa aunty Hauwa ta dinga azabtar damu da turaran matsi kawai garin Neman gira a rasa ido, tunda akace saura kwana goma sha hudu d'aurin auranmu aunty hauwa ta sanya mu a gaba, domin har munnu ma da take surukar ta tace ita bata dauke ta a matsayin suruka ba, k'anwar tace duk abunda zata min zata yi mata, kuma bayan haka Si Dan uwanta take gyarawa Munnu tun tana jin kunya ta daina ji domin yau kwananmu uku a gidan aunt Hauwa tana yi mana izaya iri-iri, magani kullum ta dama da nono mai Dan iskan bauri da wani irin k'amshi kai hawa ka taje sai mun shanye tasa, wallahi ina daga tsigar jikina na Mik'ewa saboda yanayin dandanon sa a bakina babu dad'i bauri yaji zak'i d'aci duka, ranar dai da taba ni zubarwa nayi Munnu kuwa saboda kunya sai ta shanye tasa ta aje kofin ni kuwa kullum rigima muke da ita kan hakan. Yanzu ma Mik'ewa nayi da sauri jin wani Abu na zuba daga k'asa na, zani na nasaki na mai da pant dina. Munnu tace"Ya kika tashi ne." Cikin b'acin rai nace"Munnu ke in zaki zauna zauna ki cigaba da azabtar da kanki kina budurwa ace wani Dole sai kin matse mtssss to wace irin katsewa kuma ake buk'ata. " munnu tace "Don Allah ki koma ki zauna Wallahi tunda kikaga ta dage akanmu hakan yana da amfani." Tsaki naja nace"Sai kiyi ke ni dai na gaji." Kofa na nufa ina bugawa hade da kiran sunan aunt hauwa nace"kizo ki bude min zan shiga band'aki. " bude min tayi taba fadin kiyi sauri ki fito kar maganin ya sane so nske ya bi jikin Ku sosai."
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78