Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 71

Chapter 71

Babban Yaro Book 2 Complete Hausa Novel 1,209 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

bayar ba, ba dai a kan 'yar kake min wannan hayaniyar ba Tom sha kurumin ka baby Aysha na gurina yanzu ma ta farka daga bacci na bata ruwa tasha, ka cigaba da kirana mayya a kanta wallahi dad'i nake ji, maganar da wa nake waya bai dame ka ba, mutum na son yayi bacci an dame shi."!! Kashe wayar nayi gaba ki d'ayan ta, wani irin sanyi naji cikin zuciyata na mayar masa da Martani Nasan yau da kyar in zai iya bacci. Aikuwa sakato yayi da waya a hannu yana kallon abun kamar almara baby Aysha na hannun Asma'u wato duk kauce kaucen sa yarinyar nan sai da taje ta dauko mata sweetheart, yasan halin Asma'u farin sani bata munafurci yasan da gaske take, shifa yanzu babu wacce yake jin haushi sai granny domin yana ganin itace ta bada fuskar a dauko masa 'yar sa, da kyar bacci ya dauke shi yana tunanin maganganun da Asma'u ta dankara masa. Abunda yafi tsaya masa a ransa shine tunanin da wa take waya, yasan dai idan da 'yar uwarta mace take waya baza su kai kusan a wa guda ba, wata zuciyar tace masa ko Mujahid ne? Take ya yardar wa zuciyar sa shi din ne....... Cike da tunani. Ta da mafarkin sweetheart d'insa yayi bacci. Ko da safe ma da ya tashi babu kuzari a jikinsa har abokansa suka gane, nan yace musu baya jin dad'i ne kawai, yini yayi a kwance yana kewar gwalantun baby kuma yayi alk'awarin bazai k'ara kiranta a waya ba balle ta kara fada masa magana shifa Yanzu neman hanyar da zai yi nesa da ita yake saboda alak'arsu da Mujahid. Da safe da kyar baby Aysha ta yarda da Umma lokacin da zan tafi skull ma sai Goya ta Umma tayi ta shige da ita daki don kar taga futata ko gilmawa ta ta gani zata fara zillo idan kuwa ban dauketa ba sai ta sanya kuka. Koda muka had'u da Munnu a skull cewa tayi wai kunyar Umma take ji baza ta iya zuwa ta dauki baby ba, sai nace ta bari zan kawo ta insha Allahu. Bayan sallahr la'asar na fito tsaf dani baby na bayan Umma a goye ta sauko ta, ina kokarin sab'ata a kafad'a Umma tace"Ki Goya ta akwai sanyi- sanyi hadarin nan ya zama sanyi, towel din na karba na Goya ta sosai na saki hijab kana nayi wa Umma sallama, gidan su Munnu na nufa kai tsaye. ***** Ummansu Munnu tayi farin ciki sosai ta karb'i baby ta goya ta tam a bayan ta har sai da tayi bacci ta tashi sannan ta sakko da ita, tace " Ya kamata a gwada bata abunci fa." Dariya nayi nace"Ta isa cin abunci yanzu."? Tace"Bari ki gani." Wake ta Mirza ta sanya mata a baki Aikuwa baby ta lamushe ni da Munnu muka dinga dariya, Ummansu Munnu tace"Yaran yanzu da wayon su ake haifar su, gashi dai daga laluba mata wake ta lamushe, haka Ummansu Munnu tayi mata kusan sau biyar sannan ta k'yaleta ta bata ruwa, kuma Allah ya taimaka bata yi kuka ba, sai bayan magariba Babansu Munnu ya dawo gida, ya dauki baby Aysha yayi mata addu'a hade da sanya mata albarka yayi mata addu'a sosai da sosai kana ya sanya k'aramin yaron shi yaje kanti yayi mata siyayya sosai kalolin biscuits iri-iri Ummansu Munnu tayi ta dariya tana fad'in "Irin wannan siyayar akai wa kishiyata alhalin gani a zaune ba'a min ba, dadin abun dai cin abunci ma ni na koya mata." Baban su Munnu yace." Da kin sani Baki koya mata ba ai." Mudai dariya kurrum muke musu, hira muke da Munnu sosai wacce ta dauke min hankalina sai da Ummansu Munnu ta leko dakin tana fad'in "Asma'u ko anan zaki kwana ne ga hadari nan yana had'owa." Agogo na kallah da sauri naga tara shaura da sauri na mike INA fad'in "A'a wallahi Yanzu zan tafi." Baby na dauke wacce ta Dade da yin bacci na Goya ta da sauri na zura hijab na fito wani bakin hadari na gani a gabas Nace"Munnu Allah ya kiyaye ni da dukan ruwa." Tace "ameen dai amma ni shawara ta ki bari sai gobe kawai kya tafi." Ko kallonta banyi ba nayi hanyar futa ina sallama da Ummansu dake Uwar daki. Ina futowa titi aka fara wata irin iska mai k'arfi abubuwan hawa sai gudu suke akan titi duk yawanci motocin gida ne da kyar na samu a d'an sahu Wanda ya rage mutum d'aya a ciki na shiga aikuwa kamar almara ruwa ya kece kamar da bakin kwarya,ni da nake gefe ruwa ya fara duka na, kafin kice me na jike jagab, ta karewa nayi ina tsoran kar ruwa ya taba baby sai ta fara motsi tana k'ananun kuka, gaba na ya fad'i jijjigata nake yi INA so tayi shiru yarinya kamar wacce ake zugawa ga feshin ruwa sai dukan fuskata yake, kamar zanyi kuka nace "Don Allah kayi sauri babyna na Kuka."! Mai dai-dai ta yace." Hajiya ai ina ganin parking ma zanyi saboda ban San iya inda ruwan zai tsaya ba, domin karfinsa yayi yawa sai ya tsagaita sai mu tafi." Kafin ince komai ya tsayar da 'Dan sahunsa, nace"Na shiga uku ni Asma'u nayi da na sani tawowa da na hak'ura na zauna na kwana gidansu Munnu zai fi min, tausayin baby nake ji jin yadda take sakin ajiyar zuciya tana baya sai kyarmar sanyi jikinta yake yi, ni da ita duk mun jike matan dake a dai dai ta na kalla naga sai hirarasu suke yi babu abunda ya dame su, su kadai ne single babu wacce take da yaro Karami balle tayi fargaba. Sai da aka dauki 30minutes ana ruwa mai k'arfi sannan ya tsagaita sai wata irin iskar sanyi ta soma kadawa, a lokacin naji Baby ya fara atishawa sakkota nayi ina duba jikinta, naga jagab duk da dabarun da nayi mata sai da ta Nike hatta da gashin kanta, kuka take so tayi ta kasa sai sakin atishawa take, hawaye na fara sharewa kana na rungume ta tsam! A jikina Ina fadin"Duk nice na jawo miki babyna."! Jagab! Muka shiga gida muna d'igar ruwa Umma na gani cikin ruwa ta dinga min fada "Shin baza ki bari gobe idan Allah ya kaimu kya dawo ba, ko kuwa gidan su Munnu din bak'on ki ne.? Ko tausayin k'aramar yarinya bakya ji sai kinje kin kwaso mata mura da da tari ko." Fada sosai Umma take min, ni kam hankalina na gurin baby wacce take ta motsi majina har ta fara zurara a hancin ta, kayan jikinta na cire mata da sauri na sanya mata Pampers na sanya mata kayan sanyi masu kauri kudindine ta nayi. Umma tace"Bani itanan mu gani." Mik'a mata ita nayi, ina tsaye da jikakkun kaya ban damu da In cire su ba, duk da nima hakan take kamar baby kwata kwata bana son dukan ruwan sama Shikkenan zazzab'i da mura zai kama ni. Robb Umma ta dinga Mirza mata k'irjinta da bayan kunnen ta, da tafin kafarta sannan ta Goya ta. Futa nayi jikina duk babu kwari, har yanzu da ragowar ruwa kadan kadan yake sauka d'akinta na shiga na kwabe kayan jikina pant

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});