Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 2

Chapter 2

Babban Yaro Book 2 Complete Hausa Novel 1,216 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

'yan kasuwa wad'anda suka ci suka ts dakai marasa tausayin na k'asa dasu Wanda Kansu kawai suka sani. Masu bakin ciki ga duk wani Dan kasuwa da ya sauke farashin kayansa, a cewar su talaka ba abun tausayi bane. Su biyar ne a dakin meeting din gidan gomnati wato government house suna tattaunawa game da yanda zasu b'ulluwa Amjadu domin dukaninsu saurari jawabin sa, na yau, hankalin su yayi masifar tashi sosai jin wai har company biyu ya bude a kasashen waje bayan company shi nan Lallai ya zama dole su San yadda za'ayi su rusa shi. Alhaji Sunusi mai leshi ne Yace. " Ni ina gani kawai mu hada baki da ma'aikatan sa mu Sakar masu KUDI Sosai mu fada musu bukatar mu. Cewar muna so su sanya algus da mugunta a ko wace irin adduga da zasu sarrafa, a company ta inda duk kayan da za'a futar a company su zama marasa k'wari da karko kunga daga nan Jama'a zasu gane sai su fara guduwa." Mai citta ya gyara zama hade da sakin murmushin mugunta yace." Wannan shawarar taka tayi kyau kuma itace abar d'auka dole zamu San yadda mukayi mu jone da ma'aikatan nasa idan muka jik'asu da kudi kome ye zasu yi ko ya kuka gani."? Duk suka yi na'am da haka, nan taro ya watse ko wannen su cike da farin ciki. ***** Tana zaune a parlor kamar ko da yaushe me aikin ta Iyami na zaune a gefanta tana bata labarin garin su, yayi sallama ya shigo parlor, Iyami dattijiwa mai kirki ta dinga yi masa sannu da zuwa had'e da tsokanar sa, zama yayi cikin kujera yana gaishe ta, ta amsa da fuska a sake, da sauri ta nufi kicin domin ta kawo masa abunci. Granny ta kalle shi babu yabo babu fallasa tace"K'ato me k'irar damu dawa kana tafiya gotai-gotai da kai babu iyali kai ko kunya baka ji, ka kai munzali amma ka tsaya shirme." B'ata fuskarsa yayi yace. " zan can kenan daga zuwa sai maganar aure wai a kanki nake ne." Granny tace." Yo ni in a kaina kake ai da tuni ka kashe ni. Dube ka don Allah kamar zaka ji babu jiki a murd'e ai kai kam matarka zata fad'awa 'yan garinsu." Gyara zaman sa yayi yana dariya kasa-kasa yasan halin kakar tasa da sakin magana ko wace iri ce ita babu ruwan ta, kafin yace wani Abu yaji tace" ka fad'amin in baka da lafiya sai in baza ma nema maka magani ko kauyen su Iyami muka je nasan za'a samo maka maganin k'arfi, ina amfanin girman jiki da k'wanji babu fus!! Uhum? Irin Ku ne matayen Ku suke shan takaici a zahiri dai gaku maza a bad'ini kuwa sai takaici." Ta k'arashe maganar ta tsakanin ta da Allah. Gyara zamansa yayi da k'awataccan murmushi a fuskar sa yace." E dama na kasa fad'a miki bani da lafiya don Allah ki shiga k'auyika ki nemo min maganin k'arfi kinji."!! Granny ta kalleshi da hankalinta a tashe tace"Yanzu kai k'ato da kana fama da wannan lalurar ka zauna sai dai kaci ka sha ka nemi kudi? Au! Ko da naji shiyasa ko wace mace aka kawo maka sai kace bata yi maka ba, tom yanzu yaya kake ji a jikinka shin kana sha'awar mace sa'i da lokaci ko A'a."!? Granny ta tsarashi da tambaya hankalinta duk ya tashi. Kamar gaske yace." Kwata-kwata bana jin sha'awar mata, amma ina ganin a haka zanyi auran da kike so nayi." Tace" innalillahi u ni 'yasu! Amma yaron nan kaso kacuci kanta.....Iyami Iyami Iyami.!" Ta dinga kwala wa mai akinta kira. Yace." Nifa ba cewa nayi kiyi min taron dangi ba, uhumm ke kad'ai na fad'awa damuwa ta." Hararasa tayi tace"Naji kana maganar zaka yi aure a haka Uwar me zaka tsinanawa matar taka, abunci da madara kawai zaka bata bukatar ta kuma waye zai biya mata."! Cike da tuhuma tayi masa tambayar." Dariya yake sosai yace." Ai Irina zan auro kinga bani da matsala ." "To baka isa ba ehe! Nima ai ina son 'yan yara, a gaba, ni kawai zaka cuta.'!!! Tsakanin ta da Allah take maganar, Iyami ta shigo parlor da sauri take fadin" Hjy kira kike ko."? Granny tace"Iyami zama bai kama mu ba, k'ato babu lafiya." Iyami ta kalleshi cikin rawar baki tace"Mai gida babu lafiya Ashe? Allah ya kawo sauk'i.'" Yace." Ameen Iyami ai tace"Zata shiga ta futa ta samo min magani." Iyami tace"Hjy meye yake damun Shi ne." Granny tace"Iyami je ki cigaba da aikin ki zamuyi maganar idan anjima." Iyami ta mike da jiki a sanyaye. Kallo ya bita dashi yana kumshe dariya. Ita kuwa granny surutai kawai take masa tare da yi masa fad'a ya zauna cuta yaci k'arfin sa, saboda yana so ya zama lusarin namiji. Aikuwa tana tsaka da fad'an ta taga an hasko shi a TV tashar CTV kano mutane kewaye dashi yana jawabi. Tace." Duba ka gani k'ato dubi yanda Allah yayi maka kwarjini da daukaka ta jama'a kudi duk kana da su. OO ni! 'Yar nan Allah kar ka jarrabe mu da abunda baza mu iya ba." Granny ta fashe da kuka sosai! Cike da mamaki yake kallonta, ganin da gaske kukan take yasa ya rungume ta a jikinsa yana rarrashinta tayi shiru yasan ko ya fad'a mata da wasa yake ba yarda zata yi ba ganin yadda duk ta tada hankalinta yasa yace." Granny kiyi hakuri ki daina kuka don Allah zan yi aure in haihu, ina ganin ma yanda nake jin k'arfi a jikina in dinga bada k'wayayen 'yan biyu ko uku , ki kwantar da hankalin kinji kiyi shiru kiji wani."Shiru granny tayi tana share hawaye tsakanin ta da Allah. Wayarsa ya ciro daga aljuhu yace." Bari in kira miki ita Ku gaisa." Tace"wacece kuma"? A hankali yace "My wifi mana." "Meye wifi."? Ta tambaye shi dariya yasa yace." Matata mana."? Sakin fuska tayi tace" 'yar albarka ta yarda zata aure ka da lalurar ka ko.'? Gyad'a kansa yayi kamar gaske, yana laluban numbar Mimi, sai da ya kira sau uku ba a d'auka ba, shi da in yayi kira sau d'aya baya sake wa, yau gashi yayi uku, yana shirin yin na hud'u. Mimi na band'aki a lokacin ta kuma b'oye wayar bayan katifar mu, ina shigo wa naji ringing din waya, dube-dube nake sam ban ganta ba, in da nafi jin karar tayi yawa nan na nufa na janye pillow da ta kare wayar dashi, ina dauka kiran yana katsewa, wayar na rik'e a hannuna ina dubawa cike da mamaki! Tabbas wayarsa ce, ga k'amshin sa nan jikin wayar domin hanci na ya Riga ya gama sanin k'amshin sa. Wani kiran ne ya shigo kamar kar in dauka sai kuma wata zuciyar tace"dauki kije abunda zai je da Mimi, dannawa nayi na bud'e speaker sosai na aje ta kan kati far. Muryar sa naji yo yana fad'in"Ungo wayar gatanan Ku gaisa, kafin in an kara Naji muryar mace, macen ma ba yarinya ba, dattijuwa me kamali. Motsin Mimi naji a tsakar gida, da sauri na k'wala mata kira ina fadin"Mimi kizo an kira wayar ki."!!!!!!! Granny da shi kanshi uban gayyar suka yi sak! Yayi wa muryar ta farin sani saboda tana

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});