Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 23

Chapter 23

Babban Yaro Book 2 Complete Hausa Novel 1,214 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

gidan da kallo, shiga nayi na barshi tsaye a gurin. Mamaki yake sosai yanzu dama acikin wannan gidan Asma'u take rayuwa? Duka girman gidan bai kai b'angaran mai gadin gidan shi girma ba, gyada kansa yake yana duba 'yan gujub-gujub din gidajen dake layin namu a cikin zuciyarsa yake fadin talaka na ganin rayuwa me zai hana baza'ayi zazzab'in maleria ba kwataci duk sun bi hanya sauro da kudaje da bola ko ina. Tsaye na ganshi jikin bango hannunsa nan nade a k'irjinsa nace"Shigo to" Gaba nayi yana bina a baya Umma na zaune gefen sabuwar tabarmar da ta shimfid'a masa tana sanye da farin hijab fuska a sake take amsa sallamarsa. Cikin ladabi naga ya tsaya bakin kofar ya cire hadd'adan takalimsa karfashi sanye da wata lafiyayyar safa ya karasa kan tabarmar . Umma fad'i take"Sannu da zuwa yaron arziki Mara ba lale. Zama yayi kanshi a kasa yace." Barka da yamma Umma na same Ku Lafiya."? Umma tace"Lafiya Lou Alhmdullahi ya kokarin ka da fama da jama'a. "? Yace." Alhmdullahi wallahi ya me jiki kuma."?.Tace" Jiki yayi sauk'i ai bs wani tsanani Yayi ba Asma'u ta ta soka." Murmushi yayi tare da fadin"Dama yau nayi niyar in shigo mu gaisa sai kuma take fadamin Momyna babu lafiya." Umma tace"Wallahi kuwa tari take amma da sauk'i dai tunda Aminu ya siyo mata magani Tasha ta samu tayi bacci." Yace." Tou Alhamdullahi Allah ya kara sauk'i. " Yanda suke hira da Umma sai abun ya bani mamaki kamar Wanda suka shekara da sanin juna Umma sai shi masa albarka take da fadin"Muna ganin taimakon talakawa da kake yi a garinan muna jin dad'i Ubangiji Allah ya tsare ka ya kare ka daga sharrin masu sharri. " yaji dadin adduoin da Umma take masa ga yanayin yanda yake amsawa Mimi dake kwance a daki tana bacci kamar a mafarkin taji muryar shi firgigt ta tashi ta zauna k'irjinta yayi mata nauyi sosai rarrafowa tayi ta futo tsakar gida tana dafa bango Nice na fara ganinta ganin kamar tana kokarin fad'uwa ya sanya naje da sauri na rike ta muka karasa kusa dasu Umma Tace." Yauwa ai gata nan ma ta tashi sannu Mimi." Zaunar da ita nayi kusa da shi, na matsa gefe Amjad mamaki ramar Mimi yake duk da yake dare ne kuma tsakar gidan babu wadataccan haske sai da ya fahimci tana jin jiki. A hankali yace." Momyna ya jikin ki? Ashe haka Abu yayi tsanani. " Cikin sanyayyr murya tace." Jiki da sauk'i ." gyada kansa yayi tare da kallon Umma yace." Kunje asibiti da ita kuwa."? Kafin Umma tace Wani Abu Yaya Aminu ya shigo gidan. Gabansa ne ya fad'i ganin Mutumin dake zaune ga gidan jininsa Mimi kenan a zaune a kusa dashi, lokaci guda ya b'ata fuskarsa hade da yin kicin-kicin da ita sama-sama suka gaisa dashi Yana mamakin me ya kawo shi, zama yayi gefen rijiya yana sauraran maganar da suke yi da Umma. Umma tace." Ba muje asibiti ba amma dai gobe in Allah ya kaimu za muje a duba ta sosai." Gyada kansa yayi shiru na minti biyu yace." Gobe idan Allah ya kaimu zan turo dravar sai a kaita asibtin malam Aminu a duba ba ta sosai." Umma tace"Allah yayi albarka ai da ka bari ma, sai muje asibitin Murtala ." Hannu ya zura aljihu ya futo da kudi masu yawa ya zube gaban Umma ya mike tare da fadin" Zan wuce Allah ya bata Lafiya ." Umma tace"Harda wahala kuma ai da ka barshi." Shiru yayi ya mik'awa Aminu hannu suyi sallama. Rai babu dad'i Aminu ya mik'a masa nasa hannun sukayi musabaha. Takalmin shi ya sanya Umma sai godiya take masa futa yayi cikin sauri Umma ta kalleni tare da fadin" Kije ki raka shi mana kinye tsaye." Bayansa nabi da sauri.. Yayi nisa sosai don Haka sai da na k'ara sauri. Na tadda shi. Yana kokarin bude mota na same shi Yace." Amma nayi mamakin ramar Mimi,Abunda kika fada gaskiya ne."? 'K'warai kuwa Mimi na sonka sosai kai kuma kana yaudarar ta." Shiru yayi yana tunani tabbas abunda Asma'u ta fada gaskiya ne baya jin dai-dai da kwayar zarrah na son Mimi a zuciyar sa, yana yi mata so ne kawai irin na musulunci sai kuma sunan mahaifiyar sa da take dashi. Ajiyar zuciya ya sauke tare da fadin"Allah ya bata Lafiya, Nasan ni babu laifina anan gaskiyar magana ko Yanzu aka ce an bani ita zan aure ta darajar son da data ke min." [11/10, 8:25 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO* *Mallakar_BINTA UMAR* *LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.* *47* Shiru nayi masa domin na rasa abunda zance dashi ni kaina al'amarin Mimi yana bani tsoro Mota ya bude ya shiga tare da fadin"Ni zan tafi zan kira waya insha Allahu. " Matsawa nayi daga jikin motar ba tare da nace masa komai ba ya ja ya tafi na lura jikinsa duk yayi sanyi. Ina koma wa gida na tarar da Ya Aminu ya tasa Umma a gaba sai faman bala'i yake mata Ina shiga ya hau d'ura min ashar wai me yasa na gayyato Amjadu gida wallahi komai kulafucin sa ba zai bar mishi Mimi ba. Masifa yake kamar zai dake ni Umma tace"Kar ka sake ka doke ta Aminu Sam Asma'u bata da laifi Kaine dai idonka ya rufe, ka ke ganin da laifin ta anan.". Kan Mimi ya dawo cikin hargowa yace." Wallahi Mimi ko mutuwa zaki baza ki aure shi ba sai dai idan ki Mutu ni dashi mu rasa amma ina ji ina gani bazan bar masa ke ba." Yana gama maganar shi ya fuce daga gidan a fusace.! Mimi ta fashe da kuka tari ya sark'e ta, aikuwa ta dinga yi bubu ji babu gani, Umma ta jawo ta jikinta ta rungume ta sosai tana danne mata kirjinta hankalinta duk ya tashi Da sauri tace"Asma'u d'ebo ta murhu a shafa mata ko Allah zai sanya ya Tsaya tari. Da gudu na nufi kicin na d'ebo toka Umma ta bude rigar Mimi ta shafa mata. Kamar kara ingizata ake ta cigaba da tari!!! Nace." Ina maganin a dauko a kara bata." Da kyar Umma tace"Dauko a daki." Dakin na shiga da sauri na dauko maganin, abunda na gani yayi mutukar gigita ni da bani tsoro wani irin jini bak'ikkirin na gani daga bakin Mimi yana zubowa jikin Umma, Da sauri na jefar da kwalbar maganin nayi kanta INA salati. Umma kuwa kuka ta fashe dashi tana tare jinin da hannunta. Baki na rawa nace"Umma jini ne ko."? Tace." Asma'u maza duba waje ki gani Aminu nan ki kirashi mu tafi asibiti abun ya zama babba." Da gudu na futa ko talkami babu. Mimi ta galabaita iya galabaita tari take sosai jini na zuba daga bakinta idanunta sunyi jajazur dashi sai daga hannu take. Ni da Aminu muka shigo gidan hankalumu ya tashe. Yana ganin Abunda yake faruwa ya gigice tare da fadin"Innalillahi wainnailahi raji'un. " futa yayi da sauri ya dauko mota. D'aukar ta yayi kacokan ya futa da ita da saurin Nida Muka rufa masa baya zuwa yanzu na

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});