Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 3

Chapter 3

Babban Yaro Book 2 Complete Hausa Novel 1,224 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

da saurin baki kuma bata kaurara murya tana da zaki don haka Ku cikin mata dubu ta shiga zai iya gane muryar ta. Wani kiran na kara kwala wa Mimi tare da fad'in"Mimi wai ki ba kya ji ne, Habibin ki ne fa kiyi sauri kar ta katse........ Muryar matar Naji tana fad'in" D'iyar arziki sanun ki kinji Ubangiji Allah yayi miki albarka nagode mutuka zaki auri jikana duk da lalurar da take damun sa....ko da yake naji yace." Kema baki da lafiya, kuyi hakurin insha Allahu zamu shiga mu futa Dom......Kafin ta karasa naji yo muryar sa Yana fad'in"Nifa ba cewa nayi ki wani jawabi ba, cewa nayi Ku gaisa da My wife dina kin tsaya wani zance."!! Ji nayi tace" Matsa ka bani guri don Allah , ai wannan yarinyar ta isa a jinin na mata saboda tayi jahadi.... Dariyar shi na jiyo Yana fadin"Sai kiyi ai."" Ta cigaba da cewa"Allah yayi miki albarka kinji ko." A hankali nace" Ameeen amma bani bace budurwar tashi tana band'aki ni Sunana Asma'u ita kuma Mimi in ta futo za'a..ban k'arasa ba Mimi ta shigo dakin. Nace." Yawwa ga Mimi nan. wayar na mik'a mata na futa daga d'akin. Kwata_kwata ban fuskanci komai ba Dan gane da maganganun da matar take,cikin zuciyata dai nake cewa"K'ila sunyi wata hira ne shi da Mimi tace mishi bata da lafiya, tom ni dai a iya sanina Mimi bata da wata cuta wacce bamu San da ita ba, asalima Mimi bata fiye yin ciwo ba, sai shekara-shekara take zazzab'in nan Wanda ake fama dashi. Cikin zuciyata Naji tausayin ta, kuma nayi alk'awarin sai na tambaye wane ciwo ne yake damunta Wanda har ta kasa fad'ar shi a gida ta tafi waje tana yad'awa... Tsintsaya na dauka na hau share-share dama Umma bata nan taje suna sai mu kadai a gidan. Ta futo daga d'akin sai kace wata Mara gaskiya, kallonta nayi, ni yanzu tausayi take bani ganin yanda ta hada kanta da babban aiki. Sam yanzu na daina jin haushin ta, nace" Kun gama ne " zama tayi kusa dani tare da fadin "Eh, Ashe kakarsa ce wai take so mu gaisa shine ya kira ni." Cike da nazari nake kallonta nace"Mimi wane irin lalura ce dake da har kika kasa fad'ar ta a gida, kika fad'awa saurayi Wanda baki da tabbacin zai aure ki."? Yanda na tsare ta da ido ina tuhumar ta sai ka rantse da Allah uwarta ce ni ko yayarta. Cike da mamaki take kallona tace." Ban gane abunda kike nufi ba."? K'wafa nayi cike da takaici nace"dama baza ki gane ba, naji wannan matar tana fad'in"Zata je ta nemo miki magani dake dashi kuma kinyi jahadi tunda zaki aure shi." Ranta a d'an b'ace ta kalle ni tace"Kinga Asma'u ya zaki tasa ni a gaba kina min wata tambaya kamar wata uwata, ni babu wata magana da mukayi dashi. " Nace" Ok k'arya nayi kenan."!? Tab'e baki tayi tace"ke kika sani kuma" a hasale nace"To ki kiyaye wallahi duk inda kike tunanin wannan guy ya wuce gurin, naga soyayya ta rufe miki ido kina nema ki futa waje ki tona mana asirin gida, duk lalurar da ke damun ki nasan kika fad'awa Umma zata yi miki magani iya iyawar ta, ke da kanki Kin san kafin tayi min Abu tayi miki sau dubu me zai sa ki watsa mata k'asa a ido kije ki zauna kiyi tunani da kyau kafin kowa yasan abunda yake damun ki ita yafi kamata ta sani, amma..........Kinga Asma'u.!'" Mimi ta fada tare da D'aga min hannu a fusace ! Ta mik'e tsaye. "Gwara ki nuna min cewar a gidanku nake zaune,Asma'u gwara kiyi min gori saboda ina zaune a karkashin inuwar Ku, amma ina so ki San wani Abu kin San dai nima ba daga sama na fad'o ba ina da Iyaye ina da dangi masu rufin asiri Ubana yana Raye a duniya sai dai kice ba a gari yake ba, tom insha Allah Allahu zan bar muku gida Asma'u kada wataran ki ce sai na biya Ku kud'in hidimar da iyayen ki suka yi min tun ina jaririya hakan ma na gode." Dugu ta shige dakinmu tana kuka!!! Jikina ne yayi sanyi Mimi daga magana zata yi min wata fassara ta daban, tunda muke da Mimi mu kwana mu tashi guri guda bamu tab'a fad'a na cacar baki ba,ko mu fadawa junanmu munanan kalamai, nice dama mafad'aciya in taga na hau sai ta sauko ko ta maida abun wasa,Mimi bata tab'a gaba dani idan inayi ma dariya take min, tayi min magana har in gaji in sauko. Mik'ewa nayi na bita dakin namu na tsaya bakin k'ofar shiga, ina kallonta tana ta had'a kaya tana kuka, Babu yabo babu fallasa nace" Mimi daga magana zaki yi min wata fassara ta daban, har kike had'a kayan ki, Mimi kina da wani gidan ne bayan wannan? Baki da Uwa da ta wuce Umma kuma baki da 'yan uwa sama damu, idan abunda na fad'a ya b'ata miki rai Allah ya baki hakuri." Nafada ina shigowa d'akin..... Akwatin da take had'a kayan na d'auke ina fad'in"So kike yau Yaya Aminu ya kusa kashe ni a gidanan kenan? Ko so kike Umma ta tsine min.? Kiyi hakuri bazan k'ara yi miki magana irin wannan ba." Mimi mai saukin kai da saukin hali tace." Kin kasa fahimta ta ne Asma'u amma na fada miki babu wata magana da mukayi dashi wai bani da lafiya, idan bani da lafiya sai kin Riga kowa sani tunda tare dake muke kwana muke tashi a daki daya." Domim a zauna lafiya nace"Nagane yanzu mybe shima yana tsokanar kakar tashi ne." Ta goge hawayen ta tare da fadin " ni ma nafi tunanin haka." Akwatin na d'auke na mai da ita inda take, nace"Tashi mu shiga kicin kar Umma ta dawo kin ga magariba ta kusa." Mik'ewa tayi muka futa daga d'akin. ****** *Amjadu* tun lokacin da Granny ta mik'o masa wayarsa bayan sunyi sallama da Mimi yake tunani Muryar yarinyar da yaji ta tayar masa da wani azabbanan fleengs sosai daurewa kawai yake amma yau yana ganin dole ya ragewa kansa damuwa saboda yadda yake jin mararasa na kullewa alamun sparm ya taru sosai. Lumshe idonsa yayi hade da Dan Mike k'afafun sa, jira yake gari yayi duhu a idar da sallahr Magariba yaje ya ragewa kansa damuwa. Domin had'uwar su ta d'azu ta tayar masa da sha'awa kausasan kalaman da tayi amfani dasu ne suka d'auke masa sha'awar ta a lokacin, tayi mugun b'ata masa rai. Granny ta mike tana fadin"kar dai kayi bacci nan da lokaci k'ankani zaka ji kiran sallahr magariba, shiru yayi mata bai ce komai ba, ita kuma ta shige kicin..... Nan massalacin jikin gidan yayi sallahr shi a gurguje ya dawo gidan ko zama bai yi ba, yace." Zan tafi ni." Granny tace"ga abunci can Iyami tana jera maka a daining ya kamata kaje kaci tukkuna. Girgiza kansa yayi yana d'an Sosa kunnen shi da key yace." Na koshi kinsa n bana cin Abu me nauyi da daddare damuna yake." Tab'e baki tayi, yace.' Gobe zan tafi chana kiyi min addu'a." Tace"Allah ya tsare min kai gaba da baya sai ka dawo." "Ammen suma ameen si ba

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});