Chapter 19
Chapter 19
kallonsa ba daga k'arshe ma tashi nayi na bar gurin naje na tsiri ninkin kaya ina tunin yanda Allah ya dauka kashi a duniya 'yan da yake da kyauta da son talaka da yanda yake da farin jinin jama'a, yanda yake da ibada, amma yana aikata sabon Allah domin zina mugun aikine Wanda Allah ya hana shi, kawai sai na tsinci kaina da yi masa addu'ar shiriya naji wani irin tausayin shi, babu uwa babu uba ga makiya da d'umbun masoya gaba da baya, Allah ne kadai yasan abunda zai zama nan gaba, a fili nace"Ubangiji Allah ya kare ka daga sharrin ma su sharri Allah ya shirye ka shirin addinin musulunci yasa ka daina aikata zina." ****** Yau sati guda kenan da faruwar al'amarin Wanda yayi dai-dai da kwanaki goma da afkuwar al'amarin Auran mu komai ya dai-dai ta, tun ranar da ya kira wayar Mimi na kashe ban kara kunnawa ba sai yau, sun kawo wuta na jona ta a chaji. Mimi ta shigo dakin jikinta babu k'wari ta zube kan katifa. Binta nayi da kallo. Nace"Mimi kinga yanda kika rame kuwa."? Shuru tayi min Nace"Wallahi Ki yiwa kanki fada ni yanzu kin daina bani tausayi haushi kike bani wallahi, wai Amjadu shi kadai ne namiji a duniyar nan." Shiru dai tayi min bata ce min komai ba. Tsaki naja na futa daga dakin. *** Tun lokacin da ya kira wayar yaji an kashe bai Kara kira ba yasan Mimi baza ta kashe masa waya ba. Tabbas Asma'u ce shiyasa bai kara kira ba. Yana zaune gefan bed da wayar a hannunsa numbar ya kira sai yaji ta shiga har ta katse ba a dauka ba, kira ya kara yi a karo na biyu nan ma ta katse ba a dauka ba, a je wayar yayi hade da Jan tsaki a fili yace." Mata masu aji kenan." Mik'ewa yayi ya futa parlor. Mimi na kwance a dakin lokacin da yake kiran wayar tarin da take ne ya hanata d'aukar wayar har ta katse. Cikin wani irin mugun tari da galabaita ta mike zaune hade da dafe k'irjinta tana cigaba da tarin sosai wa [11/8, 6:21 PM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO* *Mallakar_BINTA UMAR* *LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD'IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.* *45* Ni da Umma muka shigo dakin da sauri! Mimi na durkushe ta rike k'irjinta tana ta tari. Da sauri Umma taje ta rike ta ni kuma ns dauko ruwa hade da fasawa na dago kanta ina bata, k'arfin tarin ya hanata ta karb'i ruwan. Umma tace"Maza kije ki dauko gishiri a kicin. Cikin tashin hankali na nufi kicin din na dauko ledar gishiri Umma ta dangwala a hannuta ta sanyawa Mimi a baki tana Dan bubbuga bayanta hade da yi mata sannu. Mimi idonta ya rufe sosai take tari! Da haki tare da hawaye. Ni da Umma duk mun shiga tashin hankali. Nace"Wallahi Umma jiya da daddare haka ta dinga yi da kyar tayi bacci." Umma tace"Ikon Allah watak'ila busawar sanyin nan ne,. Nace"Ina jin hakane " cikin ikon Allah tarin ya lafa sai dai haki da take yi. Umma ta rungume ta a jikinta tana yi mata sannu Ya Aminu ne ya shigo dakin ya tsaya bakin kofa fuskarsa s daure yake tambayar menene? Umma tace"Mimi ce babu Lafiya in anjima ka siyo mata maganin tare saboda dare." Wani irin kallo yake wa Mimi daga bisani kuma ya tab'e bakinsa Yace. " Umma ki rabu dasu duk karya ne,nasan wannan'yar iskar ce take zugata." Umma ta bata fuska tare da fadin"bana son wannan halin naka Aminu ina ruwan Asma'u anan.? Futa yayi daga dakin ransa a bace. Nace"Umma shifa bazai taba ganewa ba tunda ya samu ya kubuta Mimi CE abun tausayi.' Shiru Umma tayi min, sai da taga Mimi tayi bacci sannan ta gyara mata kwanciya ta futa daga dakin jikinta duk babu k'wari. Kallon Mimi nake gwanin tausayi duk ta rame tayi Dan wuya k'irjinta sai sama yake yana kasa alamun tana jin jiki. Jikina babu k'wari na kwanta kusa da ita ina tunani Ringing din wayar naji wacce take jone a chaji na mike da sauri hade da dauka Babu sauk'i a murya ta nayi sallama Ajiyar zuciyarsa naji a hankali yace." Ya kike mata masu aji."!! Sama nayi da murya ta nace." Ina nan kallo kamar tsumma a randa, amma kasan da cewar zuciyar da ka yaudara da sunan so kake azabtar da ita tana cikin gararin rayuwa tana cikin halin ha'ulai kullum bata da sukun hawayen idonta ya kasa daina zuba....... Katse ni yayi kafin in karasa magana ta yace." Wannan wace irin banzar magana kike min kina yi kina daga murya kamar kina yi da sa'an ki, kiyi min magana yanda zan fahimci me kike nufi ." Haushi maganar shi ta bani saboda haka nace "Da Hausa nake maka magana ba da harshe nasara ba, nace" D'aya zuciyar daka yaudara tana cikin halin ha'ulai da damuwa saboda haka in ta shiga mugun hali to kai ne sila." Lokaci guda ya fahimci inda maganar ta ta dosa. Babu ya bo babu fallasa yace." Bani Momyna mu gaisa. " A hasale nace"Ya ina yi maka magana daban kana yi min wata maganar, Mimi dai na bacci Wanda muka samu ya dauke ta da kyar don haka bazan tashe ta." Na k'arashe maganar tawa a kufule! Wannan karon akwai sassauci a muryarsa yace." Nace kiyi min bayani dallah-dallah yanda zan fahimta ni har yanzu ban gane abunda kike nufi ba." Nace"Mimi na kwance babu lafiya tana jin jiki saboda sonka shine Abunda nake nufi. Ina jinsa yayi murmushi cikin nutsuwa yace." To waye mai laifi tsakanin ni da ita da iyayen Ku."? Da sauri nace "Kar ka sake ka zage mu ko kafad'i bak'ar magana kan iyayen mu." 'Yar dariya naji Yayi yace." 'Yan matana kenan, dags magana zan zage iyayen Ku cewa nayi waye mai laifi sai ki bani amsa ta." A fusace! Nace "Kai kasani." Yace."OK naji bani Momyna muyi magana. " "Kasan Allah bazan tashe ta ba wai me ma zaka fada mata ne bayan ka yaudare ta." 'Yar dariya yayi tare da fadin"Ina ruwan ki? Ke dai nace ki bani ita." Shiru yayi sai kuma ya cigaba da cewa"Kina maganar na yaudare ta, nifa ita nace s kawo wa kud'in aure akayi mistake aka kawo miki, bayan nan Kuma maganar Aminu ta futo, ai ni ne ma zan ce an yaudare ni an bani wacce bana ra'ayi." Tsaki! Naja na kashe wayar ganin yana nema ya Mai da mutane mahaukata. Ganin magariba ta kusa ne yasa na tashi Mimi domin baccin magariba babu kyau. Lokacin Ya Aminu har ya kawo magunguna dasu Lemo da ayaba sai kai wa yake yana kawo wa, in muka hada ido ya buga min harara. Muna idar da sallah na sanya Mimi a gaba taci abunci sannan na bata magunguna sai ta kwanta. Nida Umma muna addu'ar Allah yasa kar tarin ya kara sark'e ta. K'arfe Tara dai-dai naji ringing waya tsaki nayi Dan nasan wanene. Dauka nayi hade da sallama ba tare da ya amsa min ba yace." Ki futo yanzu ina jiran
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78