Chapter 35
Chapter 35
ki zab'a min miji Wanda kike so Amjadu na bar wa Mimi ." Umma tace." Asma'u kina jin abunda Kawun Ku yake fada ko akan ki kina jin irin cin mutumcin da yake min ko.? Nace" Umma duk naji kiyi hakuri ki kyalesu dama ba yau suka saba miki cin mutum ci. Ni nasan yanda zanyi insha Allahu Mimi bata da miji sai Amjadu ki kwantar da hankalin ki." Hannun d'iyar tata ta rike tare da fad'in"Ubangiji Allah yayi miki albarka Asma'u Yanda kike min biyyaya Allah ya baki 'yaya masu biyayya kema, yanda kike ceci rai ubangiji Allah yasa Annabi ya cece ki kema." Wasu zafafan hawaye na hau sharewa lokaci guda tausayin kaina ya kama ni, wani irin hali na shiga a lokacin ta inda naji gwara min mutuwa da rayuwa Allah-Allah nake naga Mimi a gidan Amjadu ko ma samu hankalin mu ya kwanta, Alluma ajirin fi musibati wa aklifni kairan minha itace addu'ar Dana ke ta maimatawa a zuciyata tare da Innalillahi wa inna ilahi raji'un, lokaci guda naji zuciyata tayi sanyi na kalli Umma tare da fadin"Don Allah Umma kar a kara tayar da maganar nan domin I Dan Mimi taji to wani tashin hankalin ne, Umma kija kunnen Ya Aminu a kan hakan." Umma tace"Nima abun ya soma damuna Asma'u Insha Allah zan ja kunnen sa, ke dai Allah yayi miki albarka insha Allahu yanda kika sanya ni farin ciki kema 'yayan ki zasu sanya ki." Bacci ne ya soma fizgar sa kad'an-kad'an yaji ringing din wayar sa, cikin kunnen sa, dalili airpic din dake manne a kunnen sa, a hankali ya dauki wayar dake saman k'irjinsa yana dubawa. Mik'ewa yayi da sauri ganin numbar da ta kirashi. Ba tare da ya cire airpix din ba ya latsa wayar tare da fadin"Salamu alaikum." Murya Asma'u yaji sama-sama ta amsa da wa'alaikasalm. " gabansa ya fad'i sosai lumshe idonsa yayi hade da cije leb'anshi fargabar abunda zaiji daga bakin ta yake." Kai tsaye yaji tace"Barka da yamma." A hankali yace." Barka ya kike Husnah."!! "Lafiya.'! Tafad'a babu wani sassauci ta cigaba da cewa " Yanzu Kawu Yunusa ya bar gidanmu bayan ya Sanar damu sak'on ka." "Owk" shine abunda Yace yaja bakinsa yayi shiru yana sauraran ta. Ta cigaba da cewa" Allah ya kadddara ni ba matar ka bace, ina yi maka fatan alkairi idan son da kake min na gaskiya ne, to a madadina da aka zab'a akan Mimi ni na hak'ura ka mai da maganar auranmu kan 'yar Uwata domin ceto rayuwar ta.". Wani irin gumi ne yake tsayaya daga jikinsa bakinsa yayi wani irin daci ya soma Jin zazzab'i na shigar shi, jin abunda take cewa, amma da yake NAMIJIN duniya ne, muryarsa a tsaye yace." Meye hujjar ki ta fad'ar haka, shin nine bakya so ko kuma akwai wata manufa taki."? Cike da dakiyar zuciya tace." Eh duk biyun ne bawai bana sonka ba ne, Mimi tafi ni sonka bayan haka kuma kayi mata alk'awarin aure ka yaudare ta da kalaman ka hade da zakin bakin ka, kayi kwance kwance ka lasa mata Zuma a baki daga baya kuma kace ka fasa auran ta, shin baka tunanin halin da zata shifa ko kuma kana so mu rasa ta, son da Mimi take maka zai iya kashe ta."! Wani irin yammm!! Yake ji a jikinsa tsigar jikinsa tana Mik'ewa jin abunda yarinyar take fada, a kausashe yace." Shine Hujjar ki."! ? "Eh shine Hujja ta." Ta fada babu wasa a cikin maganar ta." Ajiyar zuciya ya sauke minti uku tsakani yace."Shikkenan tunda haka kika Zab'a mana ni dake muyi rayuwa na karb'i Mimi a matsayin mata kamar yanda kika bukata, Allah ya sa haka shi yafi alkairi.". Da sauri nace"Ameen auran Mimi alkairi ne a gare ka insha Allahu." Kashe wayarsa yayi ba tare da yace min komai ba. Lokacin naji damuwar da ke cikin raina ta ragu burina kawai inga Mimi gidan Amjadu mu huta da wannan masifar, duk abunda ya faru tsakanina dashi na Sanar da Umma ita ma taji dadin yanda ya amunce lokaci guda. Hannusa ya sanya ya dafe kansa dashi lokaci guda kansa ya shiga Sara masa wani irin bakin ciki da damuwa sun taro sun tsaya masa a mak'ogwaro da kyar yake had'iyar yau!! Sosai yake jin bakin ciki da takaicin zafafen maganganun da yarinyar ta watsa masa lallai inda ranka kasha kallo wai shine yau 'ya mace take furta cewa bata son sa baki da baki yarinyar ma k'arama irin Asma'u. *14/November/2019* [11/15, 10:20 AM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO* *MALLAKAR_ BINTA UMAR* *LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI* *52* Yana zaune a gurin hannunsa saman goshin sa granny da Iyami me aikinta suka shigo parlor Iyami ta nufi daining tana gyara gurin, ita kuma Granny ta k'araso kusa dashi da sauri ganin yanda yake cije bakinsa yasa ta dafa kafadar sa, tare da fadin"Kar ka sake ka sanya damuwa cikin zuciyar ka har ta haifar maka da wani ciwon ni dai a ra'ayi na nafi so ka auri 'yar bak'ar yarinyar a cikin su biyun naga kamar tana da kunya da hankali." Ta k'arashe maganar ta a tausashe. Da kyar ya iya bude bakinsa yace." Tace bata sona Granny. " Zama tayi kusa dashi cike da mamaki tace" Amma Wannan anyi 'yar banza ta samu namiji me zafi da kwarjini kamar tace bata so, in banda ma Matsalar ka nasan ko mata dozin aka aje maka zaka iya dasu, amma wannan yarinyar ta bani haushi wallahi. " Kwanciya ya gyara hade da lumshe idonsa shi kadai yasan abunda yake damun zuciyar sa. Granny kuwa mita take tayi tace"Tun farko sai da nace maka kaje ka nemi auran Hafsatu ka kiji kaga ni ai abunda nake guje maka." A hankali yace." Granny magana ta wuce a halin yanzu insha Allah jibi za'a d'aura min aure da Ma ko wacece na yadda haka Allah ya shirya min." Tace"Tunda dai kayi niyyar auran mata biyu mai zai hana ka hada da Hafsatu nasan in kayi magana baza su ki ba." Jajayen idonsa ya bude ya sauke su a kanta, fuskar shi a murtuke yace." Ki k'yaleni da wani zance Inji da guda d'ayan ma ni da ba cikkakiyar Lafiya ba." Hararasa tayi tace"Au! Ashe munafurci ne yasa kace zaka hada mata biyu hummm! Kai dai ka sani ma kanka." Shiru yayi cikin zuciyar sa Yace ." Granny in batayi wasa ba zai sauke fushinsa akan ta yanzu juya mata baya yayi ta gaji da mitar ta tashi daga gurin. Wayoyinsa duk kashe su Yayi domin baya bukatar damu a halin da yake ciki ji yake zuciyarsa tana iya bugawa ta tarwatse. Sai daf da magari ba ya tashi daga kwanciyar da Yayi kai tsaye masjid ya nufa yayi sallolinshi tare da addu'ar Neman zabin Allah ya futo daga massalaci Jama'a na ta mik'o masa gaisuwa Amjadu bashi da wulakanci sosai ya tsaya ya gaisa da mutane, cikin ikon Allah yana shiga gidan yaji zuciyar sa tayi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78