Chapter 66
Chapter 66
sauri na mik'a mishi wayar nace "Bari in dauko wayar tawa ka tura min wsp din don Baby Aysha amma da na daina yi." Dariya yake min har na futa daga motar. A tsakaice dai sai da Jahid ya bude min wsp dina da na rufe tun bayan rasuwar Mimi ya tura min dukanin. Hotonan baby Aysha, yace" kullum zai dinga d'aukar ta sabbin pictures Yana turo min sosai naji dadin haka na saki jikina sosai muka yi shirarmu nan yace insha Allahu a karshen wata yake so ya turo magabatan sa gurin Kawu Yunusa nace"Allah yasa nan mukayi sallama dashi ya tafi. Ko da Umma taga hoton baby Aysha tayi ta mamaki sosai sai taji sha'awar ganin yarinyar a zahiri tace." To tunda ya hamu ita ni zanje da kaina in duba ta ai hakan ba laifi bane." Umma da kin kyaleshi dai komai abunda baby Dole ta nemi dangin uwarta wallahi." Umma tace"Ai baza'ayi haka ba, domin bamu San munufar sa tayin haka ba, to koma dai menene abar shi da d'iyar shi yayi yanda yake so da ita." Shiru nayi ina raya wani Abu a raina Abunci naci nayi wa Umma sallama, kai tsaye dakinmu na nufa, na tube kayan jikina wata duguwar Riga na sanya a jikina mai uban kyau da tsada duk cikin kayan Mimi suke, hula na sanya a kaina na kwanta kan katifa, hade da rufe k'afafuna hotan baby na tsurawa ido ina murmushi nima wallahi na damu inga yarinyar a zuciya ta. Wsp na shiga na d'ora pic dinta kan df na, wsp din dake amfani a waya ta mai Gb ne ya nuna min Amjad na online wata zuciyar tace kiyi masa magana kawai tunda gashi a onile da sauri na shiga gurin shi naga ya sauka akai. Yanzu Df shi na kamo da sauri ina dubawa, pic dinshi ne da baby Aysha ya d'aga ta sama yana dariya hat tada dimple dinshi sai da ya futo saboda dariya itama babyn dariya take naji sun bani sha'awa, zuciya ta tace min "Shi yana Cikin jin dad'i har da dariya gashi ga 'yar shi hummm! Ai in da mutumci Amjad bamu cancanci haka daga gurin shi ba, message na tura masa kamar haka _" Duk d'an halak baya bance alkairi kuma tilas! Ace da mijin iya baba, duk talaucin mu, baby na tabbata sai ta neme mu, domin mune dai dangin uwarta."_ Tura masa nayi na kashe data ta, tsawon mintuna ashirin, na k'ara bud'e datar, ina dubawa naga har ya gani, sai naji wata fad'uwar gaba, messenges na cigaba da dubawa ina sauraron amsar sa, shiru kusan minti talatin kuma duk dubawar da zanyi sai inga yana online, bakin ciki da takaici suka ishe ni, abunda na tsana a rayuwa ta shariya guy nan yaga sakona zai wulakanta ni, lallai ya sanja sabbin halaye, ji nayi wasu zafafan hawaye na nema su kufce min. Kira ne ya shigo wayar tawa ina dubawa naga shine..... *26/11/2019* [11/27, 4:45 PM] BintuUmarAbbale: *BABBAN YARO* *MALLAKAR_ BINTA UMAR* *LITTAFIN MALLAKINA NE KUN BIYA KUDIN KARATU NE KAWAI DUK WACCA TASAN ZATA CI MIN AMANA TA FUTAR MIN DA LITTAFINA TO TUN WURI TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA, GASKIYA DAYA CE, HAKA MA AMANA DAYA CE DUK WANDA YACI TA SAI TA CI SHI* *65* Cikin fad'uwar gaba na mik'e zaune sosai ina k'ara duba wayar tabbas shine ya kira ni. Cikin zuciyata nace to me zai ce min lallai ma, kin d'agawa nayi har ra katse wani kiran ya k'ara shigowa ina kallon wayar nan ma ta katse band'aga ba, sai da ya kira sau uku nak'i dagawa sannan ya hak'ura, kwanciya nayi ina sak'e-sak'e a zuciya ta, data ta kara kunnawa aikuwa sak'on shi na farko hannuna na rawa na shiga ina dubawa. Ga Abunda yace. _"Maganar ki gaskiya ne 'yan mata, Sweetheart bata da wani dangi sai ku domin kune iyayen ta, Abunda na kasa fahimta a maganar da kika ce duk D'an halal ba ya mance alkairi, shin wane alkairi kuka yi min da har na manta? Bayan nan kuma ina so in k'ara jaddada miki cewar Aysha d'iya tace domin nine k'ashin bayan Samar da ita, dukanin Ku baku da iko akanta, ni nake da iko akan kaya ta, so bana son damuwa don Allah daga yau sai yau karki kara yi min magana makamamciyar wannan, ina fatan kin fahimta? Kin turo min Jahid kan bukatar ki, to baki isa ba indai nine uban Aysha bazan tab'a Bari ki raine ta ba ballanta ki koya mata munanan d'abi'un ki, tabbas yanzu na tabbatar da cewa a baya nayi wauta da nake kokarin rabuwa da mace tagari a kanki , na tabbata Mimi alkairi ce a rayuwa ta, kuma duk macan da zan aura sai dai tabi bayanta wallahi,a halin da ake ciki yanzu soyayyar ta ta cika min zuciyata duk da bata Raye, ta inda nake yi wa mata kallon maza ciki kuwa har dake, saboda haka ki kiyaye fad'a min magana ko wace iri ce,ni Amjadu AbulAbbas ma nasara na shafe ki a babin rayuwa ta."_ ~AMJD ABUL ABBAS~ Wani irin gumi ne yake tsiyaya a jikina take wasu zafaffan hawaye suka kece min, Dana San wad'annan mugayen maganganun guy nan zai fad'a mun da ban mishi magana ba, hannuna na karkarwa nake bashi amsa..... Da sauri na tura masa, na kashe data hade da jefar da wayar kan Katifa na rungume filo ina tik'ar kuka harda sharb'e majina,wato ni guy nan yake nunawa iyaka ta kan abunda Mimi ta tafi ta bari gashi Ubangji ya zuba min kauna da son baby Aysha a cikin raina, nafi awa guda ina kuka k'asa kasa don kar Umma taji fa kyar na rarrashi kaina tare da alk'awarin cewar bazan kara shiga harkar shi ba har a bada..Data na k'ara kunnuwa ina tunanin zanga sak'on shi domin nasan na fad'a masa bak'aken maganganu Wanda suka fi nashi abun mamaki, ko da na duba sai naga yayi bloking d'ina, sak'on Dana tura masa Yanan yanda yake, ajiye wayar nayi ina da na sanin bud'e whatsp din inda nasan wannan bakin cikin zan riske, da kyar bacci ya dauke ni mai cike da mafarkin baby Aysha da Mahaifiyar ta. Ko dana tashi da safe sukuku na tashi jikina duk babu kuzari har Umma ta fahimci wan Abu amma bata ce min komai ba, saboda tana tunanin a jizanci ne irin na d'an Adam, sallama nayi mata na tafi makaranta. To ko A skull din ma kasa b'oyewa Munnu nayi sai da na fad'a mata komai kuma na nuna mata text din da ya turo min, Munnu ta dinga mamaki tsabar haushi da takaici yasa ta dinga zaginsa hotonan baby take dubawa sosai tana fad'in"Wallahi karya yake in Ku ya rabaku da ita mu bai isaba sai munje mu daukota Wallahi munganta ai wannan rashin imani ne ace kamar jinin Mimi sai dai mu ganta a hoto gaskiya bai isa ba."!! Yanda Munnu take masifa sai ya bani dariya nace"Munnu ni da zaki bi ta tawa da mun hak'ura wallahi duk son ki da baby baki kaini ba, amma na hak'ura na bar masa kayan sa kamar yanda ya fad'a d'in, nasan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78