Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 29

Chapter 29

Babban Yaro Book 2 Complete Hausa Novel 1,205 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ko ns aure ki zuciyar ki na can gurin wani bazan samu kulawar da nake so ba." Wasa-wasa har k'arfe goma na dare Mimi bata farfado ba, likita ya duba ta sosai ya tabbatar tana Raye kawai tayi dogon suma ne, nan ya rarrashin Aminu da ya tada hankalinsa a kan hakan. Da kyar Aminu ya futo daga d'akin sai yaji duk ya samu sauki ma domin halin da yaga Mimi a ciki ya tsora tashi babu shakka zai iya SADAUKAR da soyayyarsa a kanta domin ta rayu. Wannan shine sahihin so.da wannan tunanin ya futo. Ya Tarar da tashin hankali a waje Inda Umma ta kasa nutsuwa ta tare wata narse tana share hawaye tana rokonta wai ta fada mata idan Mimi ta mutu shikkenan sai su hak'ura saboda d'azu da Dr ya futo Lokacin su Kawu Yunusa nan yake tambayar sa,lafiyar Aminu yace masa ya dawo dai-dai Ita Mimin ce bata dawo normal ba shine hankalin ta ya tashi . Aminu yazo ya rike ta zuciyarsa nayi masa rad'ad'i da zugi ga wani irin jiri yana d'ibar muryarsa a shake yace." Kiyi hakuri Mimi lafiyar lau bata mutu ba, yanzu daga gurin ta nake." Umma ta rike hannunsa tana kallonsa cike da tausayi ta bude baki zata yi magana ya katse ta ta hanyar fadin "Umma na hak'ura da Mimi idan shine samun kwanciyar hankalinta na hak'ura ta auri Wanda take so. Umma ta rungume shi tana share hawayen ta tace." Aminu Allah yayi maka albarka Ubangiji Allah ya zab'a maka mafi alkairi a rayuwar ka, nagode da wannan karmanci da kayi min yarona ka fidda ni daga zargin mutane." Rungume ta yayi tare da tausar zuciyar ta, Ni da aunt Hauwa muka kama ta muka zaunar da ita jikinta sai bari yake. A hankali Ya Aminu yace." Ni zan je gida in kwanta in huta jiri nake ji." Aunt Hauwa tace." Idan kana ganin babu matsala shikkenan. " gyada kansa yayi kawai ya bar gurin yanda yake tafiya zaka San ba shi da cikkakiyar Lafiya. Tun lokacin da Ya Aminu ya fad'i cewar ya janye maganar auran sa da Mimi naji wani irin sanyi a zuciyata tayi wasai duk wani bacin rai da fargabar da nake ciki naji babu shi. Umma ma na lura ta sauya ta saki jikinta Munanan zaune har sha biyu babu Wanda yake kokarin kwanciya ko gyangyadi muna sauraren futaw Dr wata narse ce ta futo daga d'akin da Mimi take Fuskata babu yabo babu fallasa tace." Wacece "Asma'u a cikin Ku."? Da sauri nace" Nice." Tace." Kizo maralafiyar nan da kuka kawo na Neman ki. Hamdala Umma tayi tare da fadin"Ta farfado kenan." ? Narse tace "Eh kusan awa biyu da farfadowar ta shine Yanzu tace." Wai a kira mata Asma'u." Umma tace." Maza jeki kiji kome ye ko kara kwantar mata da hankali." Da sauri na bi bayan nurse din. Mimi na zaune ta jingina da jikin gado kanta a kasa tana wasa da hannunta kamar wata sokuwa ko kuma sabon shigar hauka duk ta sauya, cike da tausayin ta na zauna kusa da ita tare da fadin"Mimi gani menene."? D'ago kanta tayi hawaye na bin kuncin ta, ta rike hannunwa tamau!! Bakinta na rawa tace." Habbity ya zanyi da rayuwa ta ne."!!!!? Ba kasaifai take kira na da wannan sunan ba, sai muna cikin damuwa da ni da ita. Hannunta na rike sosai nace." Mimi ba dai *Amjadu* ba."? Shiru tayi min hawaye na zuba a idonta. Murmushi nayi me ciwo nace." Kamar kin aure shi kin gama an gama komai manya ma sun shiga maganar Ya Aminu kuma ya janye maganar auran ki, Yace ki auri Wanda kike so." Na k'arashe maganar fuskata dauke da murmushi na karfin hali. Hannuna dake damk'e da nata ta matsaye sosai tana gyda kanta,bata CE min komai ba, minti biyu tsakani nace." Kuma d'azu yazo duba ki lokacin kina bacci ya dad'e ma tare da dr duk wasu hidima shine yayi, nima na amunce ya aure mu tare ki kwantar da hankalin ki." Cikin nauyin baki tace"Nagode Habibty 'yar uwata ta kaina hak'ika kin cika 'yar halak Nagode Asma'u na rasa wata irin zuciya ce dani narasa wace iri ce ni, ki yafe min zuciya ta tafi karfina bazan iya sarrafa ta ba." Murmushi nayi hade da rike hannunta nace "Ba laifin ki bane Mimi sharrin so ne kawai kowa ma haka tana iya faruwa dashi, kuma kinsan kowa da irin zuciyarsa wani yana da dauriya wani kuma bashi da ita, hakanan wani yana iya sarrafa zuciyar sa, wani kuma zuciyarsa tafi k'arfi sa, kamar ke kenan, hummm!! Yanzu dai magana ta wuce insha Allahu baki da miji sai Amjadu zakiyi rayuwa inuwa guda dashi." Wata irin ajiyar zuciya ta sauke tare da sakin wani irin murmushi Wanda dashi gwara kuka tace." Asma'u na Dade da sanin cewar *Jad* baya sona nice nake haukana a kanshi, ke yake so inda ke kuma baya gaban ki!! Ki bani shawarar Ya za'ayi na jawo hankalin sa kaina. " Murmushi nayi ina mamakin Mimi da so ya rufewa ido ashe har suna ta sanya masa wai *Jad* humm!! Sunan kuwa yayi min dad'i. Domin in kara kwantar mata da hankali nace" Mimi ke kike abunki kar ki damu ni nasan da an d'aura aure zai so ki kamar ya mutu zai so ki fiye da yanda Ya Aminu yake son ki, Mimi kina da kyau kina da kira mai d'aukar hankali gaki fara alkyabar mata, babu namjin da zai kauda kansa daga kanki ki kwantar da hankalin ke dai." Murmushi tayi hade da sunkuyar da kanta har yanzu hannuna guda na rike da nata.nace "Kinga wayar ki ma a hannuna Bari in kira miki shi Ku gaisa ko."? Bata ce min komai ba, na fara kiran numbar shi, bugu daya ya dauka muryar shi da alamun bacci yace." *HUSNAH."!* Sai da naji wani irin yarrrr! A jikina jin yanda ya ambaci sunana da ba kowa ne yake kira na dashi ba, ga muryar tayi low sosai kamar me mura. Ajiyar zuciya na sauke babu yabo babu fallasa nace"Ga Mimi za kuyi magana. " Shiru naji yayi nace ."Hello." Gyaran muryar shi na ji yace." Owk bata wayar." Mimi na mik'awa wayar da murmushi a fuskata, hannunta na rawa ta karb'i wayar tayi sallama da dusashashiyar muryar ta. Ina jinsa yana amsa mata a sake, yace." Ya jikin naki Momyna."? Tace." Jiki da sauki." Yace." Alhmdullahi ki kwantar da hankalin ki kinji ko duk abunda kike tunanin bazai yi wu ba to zai yi yuwu da izinin Allah idan Allah ya kaddara ke din matata ce Sai ki ga munyi aure, ki daina tashin hankalin ki, Tare da yardar 'yar Uwar ki ni na amunce zan aure Ku a tare ina fatan alkairi a kan haka, daga k'arshe nake ce wa dake ki godewa 'yar Uwar ki, domin tabbas ta sadaukar da nata farin cikin a kanki da samun fi gaban ki hade da lafiyar ki. Momyna hak'ika kin sa'ar 'yar uwa me kyawun zuciya." Ya karasa maganar tasa cikin nutsuwa. Ba Mimi ba ni kaina kalaman sa sun yi min dadi kuma naji dadin yabon da yayi min abunda bai tab'a faruwa ba ni dashi, bai

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});