Chapter 76
Chapter 76
ita tadafa abinci doesn't mean ita tasaka poison, banda haka ba itakadai ne agidan nanba sanan kowa anan can enter bangaren Aliyu" cikeda rashin kunya da rashin mutunci Maman su Rauda tace "me kake nufi Alhaji Aneesa bazata iya kisa ba to mune kenan zamu iya? Sonkai kiri kiri sabida yar gaban goshin kace, mukake zargi kenan mune zamu iya ko, nagadai akwai CCTV agidan aje aduba mana hakanan nifa na tsani zargi koba hakaba Amina" da sauri sukace hakane wlh, officer ne ya kalli Dady yace "Sir akwai CCTV agidan nanne?" gyadamai kai Dady yayi yace "akwai a compound dinan, banda haka akwai CCTV a bangaren Aliyu dashi kanshi baisani dashi ba, CCTV tareda kwan lantarkin dakinshi yake, nasaka ne sabida nasan matayena sun tsaneshi zasu iya komi akanshi saisa nasaka?" da sauri officer yace "ina zamuga footage din" "muje yana secret room dina" ya kalli matan yace "kar wacce ta tafi daki kujiramu anan" hanyar flat din Mama Dady yayi da Officer, wani irin murmushi Mama tayi zuciyata tai sanyi dama takira CCTV ne sabida tasa aduba, Dady yazaci shi kadai ysan password din shiga dakin baisani batun yauba tasan. Dakin Mama sukayi sukai sama, agaban wani daki ya tsaya da handle din kenan kaman waya ga boturan dannawa, password din yasaka saiga dakin yabudu computers ne wurin shiga adakin, straight computer bangaren Aliyu Dady yanuna musu, officer ya zauna gaban computer yay rewinding back har zuwa footage din jiya, rewinding sosai yayi har zuwa daidai inda Aneesa tazo part dinshi ahankali yace "got it" tsayawa Dady yay akanshi ya shiga kallo kirjinshi na bugawa shigowa part din tayi rike da tray ta kalli ko ina kaman tana neman wani abu kafin suga tai tafiya da sauri ta shiga falon ta sauke tray din kan center table tana kalle kalle, sai sukaga ta chusa hannunta agefen zaninta basuga metayi ba sundaiga tafito da kwaya daya ta jefa a mug saikuma tadauko daya ta dagargaza kaman yanda ake dagargaza magi da hannu ta barbaza kan saman pancake ta kakkabe hannunta tadauka da sauri tai hanyar bedroom dinshi tabude kofa ta shiga dayake babu CCTV a bedroom dinshi basusan meya faru ba sundaiga chan tafito daga dakin aguje, baya Dady yayi zai fadi tsabagen yanda heartbeat dinshi yay weak polisawan suka tareshi suna salati wani irin fincike kanshi Dady yayi yafita daga dakin da mugun zuciya. Tundaga yanda Ammi taga fuskarshi gabanta ya shiga faduwa ta shiga ambaton Allah, dawani irin zuciya Dady ke dumfaro su harya karaso inda suke tsaye hannu yasa yawani irin fizgo Aneesa dake tsaye kusada Ammi jikinta na rawa Dady baiyi wata wataba ya daga hannu ya watsa mata lafiyayyen mari "tass!" runste ido Ammi tayi dan har kashinta taji marin da Dady ya dauke Aneesa dashi, fashewa da kuka sosai Aneesa tayi tsabagen tsoro tamika hannunta tana kokarin kamo Ammi tace "wayyo Allah na Ammi, Ammi, Ammi, Ammi n...." zuba mata wani marin Dady yayi akaro na biyu da saita yasa tai shiru tai gum tama kasa magana sai dubu datake gani a idanunta cikin ihu da daga murya Dady ya jijjigata yace "me Aliyu yamiki? Meya miki kikeso kiashi lahira? Ubanwa yasaki kikashe min d'a??" yakara daga hannu zaikai mata mari na uku Ammi ta kirashi. "Alhaji" dago kai yayi ya kalli Ammi idanunta sunyi jajir suna shirin tsiyayar da hawaye, cikin raunin zuciya Ammi tace "kayakuri Alhaji ka kwantar da zuciyan ka abi komi ahankali, Aneesa bazata iya kisa ba, nasan abinda na haifa" cikin wani irin fushi Dady yace "nine makaryaci ko, kina zaton shiri nama yarki? Okay naji shairi namata a CCTV baya shairi ko to muje kigani" ya finciki Aneesa dahar lokacin bata gani sosai yay flat din Mama Ammi tabisu da sauri su Rauda dake kuka sosai da sauran matan Dady ma suka bisu har dakin cameran, shiga dakin Dady yayi rikeda Aneesa kaman wacce tai sata sauran matan ma da Ammi ma ta shigo cikin tsananin fushi Dady yace "play d footage back officer" dan bude idanu Aneesa tayi ta kafe computer da ido, wani irin faduwa gaban Ammi keyi lokacin da sukaga Aneesa ta jefa kwayar a mug da lokacin data dagargaza daya ta zuba akan pancake dakin yadau salati Mama tace "ga irinta nan ai, aure aure yau munga ranan aure aure, ka aurosu karufa mata asiri ka kawota gidanan da ita da agolan yarta, kahada yarta da namu gashinan suke son kashemaka d'a muda muke gidan nan shekara da shekaru ko kurjewa bamu tabasa Aliyu yayi ba amma gasunan dududu satinsu nawa a gidan just sati biyu da kwana daya" tajuya ta kalli Ammi tana mata tafi a fuska tace "to Allah yatona asirin ku, Allah yatona asirin ku kinyi amfani da yarki ta kashe Aliyu an kamaku, Allah saiya sakama Aliyu, butulu kawai murders, Aliyu daya dauke ku a matsayin uwa, andaiji kunya anji kunya, wlh hukuma ce zata rabamu daku, mutumin daya miki komi yafi fitaki kanmu harda siyamiki mota ne zaki kashema da" Dady jiyayi kirjinshi na tafarfasa kan maganganun Mama dan kaman tana sosamai inda kemai ciwone, cikin fushi Dady yajijjiga Aneesa dake kuka sosai yace "me dana yamiki Aneesa zaki kasheahi tell me the truth" fashewa da kuka sosai tayi tace "Abba wlh wlh, na rantse maka da girman Allah bani bane wlh, wlh kuw......" wani irin mari Dady ya kifa mata abaki saijini cikin ihu yace "stop lying! Stop lying kifadamin gaskiya, Maman ki tasa ki kashemin Aliyu kowane?" da sauri ta girgixa kai muryanta harbaya fita da kyau tsabagen kuka tace "wlh Abba banine ba, banine ba na rantse maka da girman Allah" cikin wani irin fushi ganin yanda take karya bayan ankamata dumu dumu yasa Dady yarufe ta da duka baji bagani tun Aneesa na ihu tana kiran Ammi hartazo takasa ihu ganin yana neman sumar da ita yasa officer da yaranshi suka rikeshi, yaciro ankwa daga aljihu yakama hannun Aneesa yasamata yace "with all the evidence damuka samu a kanki malama Aneesa, you are under arrest for attempt murder of Aliyu Muhammad Ibrahim you have the right to remain silent anything you say will be used against you" yajuya ya kalli Ammi dake kallon Aneesan dako numfashi bata iyayi yace "ki gayama yarki tafadi gaskiyan duk inda tasamo wanan poison din inba hakaba gidan yari ne makomarta" yaja Aneesan kaman yanajan kare sukai hanyar fita daga dakin Ammi ta tsaya still tana ma Dady wani irin kallo, duk fita akayi daga dakin akabi su officer dan aga inda zasuyi da Aneesa yarage daga Ammi sai Dady adakin, ko kallonta Dady baiyiba azuciye yazo zaibi tagefenta yawuce takama hannunshi tarike lumshe ido Dady yayi Allah kadai yasan iyason dayake ma Ammi dan tabashin nan datayi har brain dinshi yaji, kasa juyowa yayi hakan yasa ahankali Ammi ta zagayo ta gabanshi tasan Dady nacikin tashin hankali, ya acikin matsala saisa dudda uban dukan dayama Aneesa still tamai uzuri batason ko kadan taga bakinshi, ahankali tana kallon fuskan shi tai kneeling akasa ta hade hannayenta ta danne zuciyata sosai dan bata so ta karaya she needs to be strong and fight this battle for her daughter a yanzu Aneesa batada kowa sai ita she's all alone, Murya chan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78