Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 46

Chapter 46

A Tsakanin Soyayya Book 1 Complete Hausa Novel – Aliyu’s Romantic Journey Begins 1,203 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

shi suka bama Ammi ahankali tadaure tadago kwayoyin idanunta dasuka sha kwalli ta daura akan Dady, wani irin lumshe ido yayi kafin yabude su ahankali ya kalleta murya chan kasa yace "godiya nake yallabiyata" sallama Aneesa tayi ta tsaya abakin kofa tana jiran abata izinin shigowa, ahankali Ammi tace "shigo" shigowa tayi dauke da best tray dinsu mai kyau da maltina mai sanyi ke kai sai kulan tuwo da miyan kuka dayaji wake da kifi da dan bowl dake dauke da ruwan wanke hannu sai goran ruwan Eva maidan sanyi Baffa yasiyo maltinan da ruwa, karasowa tayi ta ijiye tray tace "Abba ga abincin ka nan, Ammi na tadafa ai zaka cinye ko" da sauri yana kallon fuskan Aneesan yana mata murmushi yana masifar son yarinyar yace "kwarai kuwa, tunda Ammi ki tadafa ai dole na cinye harda side kwano" murmushi sosai Aneesa tayi tadan saci kallon Ammi data watsa mata harara tamike tafita daga dakin takoma wurin su Baffa. Kallon Ammi Baffa yayi cikeda so ahankali yace "nagode da karamci, musamman kikamin girki dole na cinye abincin hasken idaniyata" murmushi Ammi tayi tasa hannu zata jawo tray dan serving nashi yace "zanci anjima kadan, yanzu lokacin kine bana cin abinci ba" murmushi Ammi tayi tama rasa mezatace itadai wanan mutum na kashe mata zuciya da kalamai. Gyara zama Dady yayi yana facing Ammi dake wasa da yatsun ta yanda Aneesa keyi, ahankali yace "ina kaunar ki sosai Rukayya sabida ina ganin kaina aduk lokacin dana ganki, ayau nazo wurinki dauke da batu biyu danake so namiki masu mahimmanci" shiru Ammi tayi ta baci dukkan natsuwan ta sabida yanda taga yanatsu shima alamun maganan dazai mata mai ma'ana ne, dan ajiyar zuciya yayi yace "Rukayya banso mugina rayuwan mu kan karya kokuma yaudara, Inaso mugina rayuwan aure na amana da tsantsan kauna da jinkai, maganan farko dazan miki shine kome zaki gani agidana badaga wurina ba wurin matana kiyakuri bazan miki karyaba matana sai ahankali, sai ahankali kome zasu miki baruwanki dasu ba zaman su kikeba zamana kike, banso kiyi koyi da dabi'oisu, sonake nakara aure konadinga samin kwanciyan hankali daga wurinki" yay dan shiru kafin ahankali yace "sai magana tabiyu, marayan d'ana Aliyu shekaran shi ashirin da tara yanzu, mahaifiyar shi tarasu tun kafin yadan tasa, inaso kihada shi dashi da Aneesa kirike minsu amana Rukayya, matayena basa sonshi ko kadan abinci inba ina gidan nanba nace akaimai ba'a kaima, baida hayaniya ko kadan zaki ganshi, baida fada, baima cika magana ba, Komi nashi inaso yadawo wurinki, nabaki shi Rukayya kece mahaifiyar shi zuciyata ta yarda sanan ta aminta dake, kirike minshi amana kinji Rukayya hope ban hadaki da aiki babba ba?" dan murmushi Ammi tayi tace "ko kadan, d'a nakowa ne, baka hadani da aiki ba, nakuma gode da matsayin daka bani namaka alkawari zan kula dashi amana, bqzaka taba samuna da zalunci ko ha'intar shiba, na karba, na karbi Aliyu da hannu bibbiyu, Allah ya shige mana gaba" "Ameen" Dady yace yana wani irin jin son Ammi aranshi. Shiru duk sukayi suna kallon juna Ammi ce tafara breaking kallon ta nunamai tray tace "abincin ka zai huci kaci dan Allah" murmushi Dady yayi yace "ina zan iyacin abinci batare danasan ranan da zan mallaki Rukayya amatasayin matata ba uwar yarana guda biyu Aliyu da Aneesa" wani irin cute smile Ammi tayi batare data kalleshi ba, cikin wani irin murya Dady yace "idanuna na maradin wanan sassanyar kallon naki mai sanyayamin rai gimbiya" dagokai Ammi tayi ta kallai, ahankali yace "yaushe zaki bari na mallakeki kidawo mallakina?" ahankali Ammi tace "duk randa kakeso Yallabai" washe baki Dady yayi yace "yau Wednesday ko" gyadamai kai Ammi tayi, murmushi yayi yace "ran jumma'a nakeso adaura auren bayan antaso daga masallaci inyaso zan iya kara miki ko kwana biyu ne ko sati daya kigama shiryawan ku na mata saiki tare ko Gimbiya" dan murmushi Ammi tayi tace "hakan ma yayi, Allah yasamana albarka aciki" dan lumshe ido Dady yayi yabude yace "ina kaunar ki sosai Rukayya," yy maganan ahankali yana kallon Ammi kaman yana jiran tacemai wani abu murmushi sosai Ammi tayi tamika hannunta tadauko kulan abincin ta ijiye kusada shi tana kokarin budewa ahankali tace "ina kaunar ka nima Yallabai tun ranan dana fara ganinka" numfashin Dady yakusa daukewa da sauri yace "wayyo Allah na ban ruwa Rukayya zuciyata ta dadada dayawa, dole in kora da ruwa" murmushi sosai Ammi tayi tana girgiza kai tadauko ruwan tabude ta mikamai tana kallonshi kafa ruwan yayi abaki ya asha yana kallonta kafin ahankali ya mika mata goran, karba tayi tace "kaci abinci to" faraci yayi ba karamin dadi abincin yamai ba tass yaci ye tuwon hakan yama Ammi dadi ba kadan ba, ya wanke hannu yana share baki sanan ya kalli agogo goma saura tashi yayi yace "bari intafi, amma fara bani izinin tafiya tukunna" murmushi Ammi tayi tace "nabaka" "tom saida safe" gyadamai kai tayi tace "Allah ya kaika lafiya, nagode" har bakin kofa taraka shi yatafi su Baffa suka rakashi waje Aneesa ta shigo tareda rungume Ammi tana murna, yarane suka shiga shigo da jakunkunan na kayan kwalama daga baya kuma saiga su Baffa abinci tanasu suka ci suma suna mata maganan ran jumma'a za'a daura auren wai inji Alhaji. Karan shigowan sako dataji yasa tabude. _na manta ban gayamiki ina tsananin kaunar ki kafin natafi ba, ina miki Son so, ki kulamin da kanki gimbiyata, Allah yamiki albarka, saida safe_ _Alhaji Muhammad Ibrahim_ Murmushi Ammi tayi ta ijiye wayan bata taba sanin zata karason waniba, bama tasan Yaya akai Dady ya sace mata zuciya ba kodan sabida yanda yakeson Aneesa ne? Kokuma sabida yanda Aneesa keson shine? Kokuma da iya maganan shi da halin taimakon shine? All she knows is tanason each and every single shade of him. _duk wacce takaranta bata biyaba itada Allah, duk maison book dinan ta tuntubeni ta 07012181461 watsapp_ _masu fitarwa dama ku watstsatsu ne, saika kuka watsawa, ban yafemukuba kuma, rubabbu kawai_ [4/5, 8:09 AM] Hijabi_muslimah🙌: _*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_ _IN BETWEEN THE LOVE_ ❤ _Lies another love_❤ _✍🏿M Shakur_ 3️⃣1️⃣ Gida suka karasa bayan sun tsaya sunyi sallan isha'i, thank God Momma bata falo dakinsu ya wuce direct dan ko kadan bazai iya tsayawa mata magana ba, ko takalmi bai cireba yafada kan gado yaja bargo yarufe tundaga kanshi har zuwa kafafunshi, inda ace zai biyema zuciyan shi kuka kawai zaitayi batare dayasan mezaiyi ya sanyayamai raiba, he's so soo maddd, so angry, ya tsani yaga Aneesa dawani tanamai magana jiyake kaman zai fadi yamutu, baima san tayaya zaiyi describing yanda zuciyan shi kemai zafiba idan ya ganta dawani, jiyake kaman ana daddatse mai zuciya da babban wuka, wani irin wahalallen bacci ne yay awon gaba dashi yana cikin tunani. Abdul ne yabude kofar dakin ya shigo zaimai magana yaga har yay bacci ya dunkule agado looking so innocent ko kayan jikinshi ma bai cireba yana sauke ajiyan zuciya daddaya, ahankali yazauna abakin gadon yana kallonshi yana tunani yaushe har soyayyan barkono yakama shi haka? Rashin amsan tambayan shi yasa shima duk yunwan da yakeji yaji takoma ciki ya kwanta gefen Aliyun shima batare daya cire kayaba nan wani shegen bacci yay awon gaba dashi. Momma dake kitchen dasuka shigo ne tafito Ihsan

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});