Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 52

Chapter 52

A Tsakanin Soyayya Book 1 Complete Hausa Novel – Aliyu’s Romantic Journey Begins 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

tabude kofa suka shigo itada Ammi dake sanye da hijabi har kasa sai Aneesa, itama sanye da hijabin ta har kasa tana gefen Ammin ta har wajen kujera Momma takawo Ammi da Dady yabi da kallo tace "ga kujera ki zauna" zama Ammi tayi ahankali tadan dago kanta ta kalli Dady dake kallonta cikeda natsuwa da tsantsan girmamawa tace "ina yini Alhaji, barka da dare" har wani irin lumshe ido Dady yayi da Ammi ta gaidashi muryanta na ratsa kowani bangare najikinshi, kafin ma yabata amsa ta juya ta kalli sauran matan dan kallo daya ta musu tagane matayen Dady ne tace "ina yinin mu" zama Aneesa tayi gefen kafar Ammi tace "ina yini Abba" murmushi sosai Abba yayi yace "lafiya lau daughter na, ya gajiya" cikeda kunya tana kare fuskarta da hijabi dan dakin da mutane da yawa tace "Alhamdulillah" sanan ta kalli matayen da Ammin ta ta gaida basu amsa ba tace "ina yini" dan gajeren tsaki maman Rauda taja, har ranshi Dady yaji tsakin baice komiba yasan dama bazasu amsaba ya kalli Momma data tsaya kallon komi yace "sun wuce?" "eh sun wuce yaya, nima natafi saida safe" "nagode" hannu Rauda tadagama Momma tana murmushi tace "Momma saida safe ki gaidamin da Ihsan" murmushi Momma tayi tace "zataji Rauda" tabude kofa tafice. Ajiyan zuciya Dady ya sauke kafin ya gyara zama yabude taro da addu'a sanan ya kalli yaranshi dake zaune kan carpet din yace "yarana" atare suka amsa dukan su "na'am Dady" murmushi yayi sosai yace "na kiraku nanne sabida na nuna muku new Mummy dinku, sunanta Mummy Aliyu kokuma kuce Mummy Aneesa" duk murmushi yaran sukayi suna kallon fuskar Ammi dake kasa banda Hajar datai kini kini da rai, ganin yanda suke murmushi Dady yace "ga Aneesa nan, y'atace itama sanan yar uwarku ce, Inaso kuhada kai kuso juna banda fada kunaji" da sauri duk suka gyadama Dady kai, murmushi Dady yayi shi yasan Allah has blessed him da yara nagari but iyayen su ke batamishi su, ahankali yace "kutashi kuje ku gaida new Mum dinku" da sauri suka tashi har ana rige rigen zuwa murmushi Ammi tayi ta rungume su tana shafa kansu sai gashe da ita suke. "Mummy Aliyu ina yini, Mummy Aliyu good evening" haka suketa gaidata, Rauda ma tazo tana murmushi tace "sannu da zuwa Mummy" murmushi Ammi tayi ta shafa fuskarta tace "nagode y'ata" Hajar ma tasowa tayi ba yabo ba fallasa tace "ina yini Mummy Aliyu" lafiya lau Ammi ta amsata ganin yanda ta gaidata da kyar sanan duk suka koma suka zazzauna, murmushi Dady yayi ya kalli Ammi yace "dukan su yarana ne, su goma sha tara ne Rukayya" ya kalli yaran yace "to duk kutashi kutafi ku kwanta zanyi magana da iyayen ku" tashi sukayi ahankali harda Aneesa da Rauda tamiko mata hannu dan tun dazu data shigo take kallonta tagane ta ita Aneesa bamata ganeta ba har yanzu dan ranan dataganta tai buzu buzu, murmushi Aneesa tayi Dady na dan dariya yaji yakara son Rauda suka fita daga dakin Mama nabin bayan Rauda da harara suka rufo kofan. _how to subscribe_ _zaki turo 300 ta account number na 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment ta watsap number na 07012181461 sainai adding dinki a group din a tsakanin soyyayya_ _duk wacce takaranta batare data biyaba Allah ya isa_ Gyara zama Dady yayi zaiyi magana Amarya tace "ansa y'ay'an mu sun gaidata amma ba'a saka yarta tagaidamu ba tun yanzu anfara son kai" da hannu Dady yanuna ta cikin kakkausar murya yace "Zainab ki shiga taitayin ki last warning" yay maganan babu alamun wasa atattare dashi hakan yasa kowaccen su tahadiye abinda ke ranta, Dady yayi shiru yana kallonsu kafin cikin fushi yace "data shigo ta gaida ku kun amsata ne? Anyway kubi ahankali inba hakaba zanyi mummunan saba muku" dan shiru yayi trying to calm kanshi down kafin ahankali yakira Ammi. "Rukayya" ahankali Ammi tadago kanta tace "na'am Alhaji" nuna su Mama yayi yace "ga matana nan, Kareema itace uwargida, sai Amina mai binta, sai Zainab" ya nuna amaryan shi yace "itace ta uku, inaso ki basu girman su banson neman fada da hayaniya, kwana bibbiyu ne ake amsan girki, ba'a girki General girki agidana ko wacce tana girkinta daban dan banson tashin hankali da korafi, duk randa nake dakin ki saikiyi dani, ko wacce ina samata abinci a dakinta idan wani abu yakare ba'a riga an kawoba akwai General store anan tsakar gida zaki iya dubawa in akwai abinda kike bukata saiki dauka, inaso ki zama mace mara hayaniya mara fada da kowa, ki kare mutunci kanki dana mijinki kome aka miki kifada min kafin kidau hukunci kinji Rukayya" gyadamai kai Ammi tayi tace "in sha Allah zan kiyaye duk abinda kace Alhaji, Allah yatayani yakuma yimin jagora" murmushi yayi yana kallonta yace "Ameen" sanan ya kalli sauran matan shi yace "ga yar kanwar kunan sunanta Rukayya nabaku ita amana, ku hada kanku kuyi bautan aure, ku kwantar min da hankali ku hada kan yarana, banda fada da hayaniya, Allah yamuku albarka dukanku, idan damai magana zata iyayi" da sauri Amarya tana kumbure kumbure tace "yanzu kwana nawa zakayi a wurin ta kafin kadawo wurin mu?" dan murmushi Dady yayi ganin yanda kishi ke cinta yace "kwana uku in sha Allah" Maman su Rauda cikin daure fuska tace "wanan yarinyan kuma fa damuka gani?" cikin daure fuska Dady yace "y'ata ce itama, sunan ta Fateema ana kiranta da Aneesa, dawata maganan ne?" Amina matar Dady ta biyu ne tace "badai makarantan da y'ayan mu suke zaka sata badai ko" cikin kakkausar murya Dady yace "Aneesah y'ata ce bakida ikon da zaki fadamin how da kuma tayaya zanbi da yarana, duk inda nasata wanan ba matsalan ki bace tunda dai bada kudin ki nake biyan kudin makarantan ba" zata kara magana Dady yadaga musu hannu alamun suyi shiru kafin yanuna musu hanyar kofa yace "zaku iya tafiya" tashi sukayi fuuu suka fice suka bugo kofar, ahankali Dady yatashi daga kan kujeran yakoma kan kujeran da Ammi ke zaune hannu yasa yadago fuskarta murmushi ta sakan mai mai taushi ajiyan zuciya ya sauke yace "am sorry Rukayya, kiyakuri dakome matana zasuce I know kalaman su have hurt you kiyakuri kinji" murmushi Ammi tayi ta kama hanun Dady tana shafawa ahankali tace "karka sake ban hakuri ko daya ban damuba, hasalima godiya zanma, thank you for standing as a father to Aneesa agaban kowa Abu Aneesa" murmushi Dady yayi yace "ni mahaifinta ne so don't ever thank me akan anything dazanma y'ata Ummu Aliyu" ahankali Ammi ta rungume shi tana murmushi, bayanta ya shafa murya chan kasa yace "Aneesa ta iya kwana ita kadai?" gyadamai kai Ammi tayi murya chan kasa tace "eh" murmushi Dady yayi yace "tashi to muje mumata saida safe" murmushi Ammi tayi tace "to Allah ja zamanin Maigidana" tashi Dady yayi yana murmushi yadaga ta yana rike da hannu ta suka fito daga part dinshi sukai part din Ammi Aneesa bata falo hakan yasa sukai sama atare itada Dady suka shiga dakin Aneesa harta kwanta tafara gyangyadi tarufe da bargo dan karfin AC yamata yawa yanda ta dukunkune yasa Dady yace "lafiya Aneesa ko zazzabin ne" da sauri tace "Abba sanyi

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});