Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 47

Chapter 47

A Tsakanin Soyayya Book 1 Complete Hausa Novel – Aliyu’s Romantic Journey Begins 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

dake biyeda ita tafito itama, Ihsan ta kalla tace "jeki kiramin su suzo suci abinci" sama Ihsan tayi bata wani jimaba ta sauko tana dariya tace "Momma duk sunyi bacci ko takalma basu cireba" girgiza kai Momma tayi tace "Aliyu da Abdul ai saidai Allah ya shirya domin kam duk kanwar ja ce" ta gyara zama tana kokarin daukan remote dake kan dayan kujeran tace "jekici abincin ki Ihsan". Sai wuraren shadaya sanan Aneesa tabaro wurin Baffa dasuka wuce dakin zaure dasuke kwana itakuma tadawo daki, kulle kofa tayi dan tasan Ammi ta riga ta kwanta, dakin Ammi ta wuce straight Ammi na zaune kan gado tana linke kayan data cire, kallo daya tama Aneesan ta dauke kai, murmushi Aneesa tayi takarasa kan gadon ta zauna kusada Ammin, kayan ta karba takarasa linkewa ta tashi tai wajen sip din Ammi, sip din tabude tana kokarin maida kayan ciki tace "Ammi kinason Abban? Naga su Baffa sunce jibi ne bikin" tana maganan tana jera kayan a sip, jin Ammi ba tace komiba yasa ta juyo ta kalleta, hada ido sukayi da Ammi dake kallonta, washe baki tayi takaraso ta zauna kusada Ammi tareda daura hanunta kan cinyar Ammi tace "eh Ammi, bakice komiba" dan murmushi Ammi tayi tace "kina sonshi to Aneesa, ba dole na yarda ba" washe baki tasake yi tace "nagode Ammi na, Ammi kinga ko nizan miki lallen biki, in miki kwalliya dakomi ko Ammi" tabe baki Ammi tayi tace "nine zanyi wani lalle saikace bikin yar yarinya" kaman Aneesa zatai kuka tace "wlh nisaina miki, Ammi na mai shegen kyau kinji" tabe baki Ammi tayi tace "naji to, Allah kaimu da rai da lafiya" Ameen Aneesa tace haka tacika Ammi da surutu har Ammi tagaji tace mata tamata shiru kota maketa, gabaki daya tama manta da batun wani Aliyu daya bata mata rai dazu, bamata so ta tuna ko kadan, mamanta is getting married so she's super excited. _masu iya magana sunce rana bata karya, saidai uwar diya taji........_ Yau dubannin jama'a wayanda suka halarci sallan jumma'a a babban central mosque in Suleja, wanda ya kunshi mutane da dama daga ciki harda abokanen Dady na wajen aiki da kasuwance, Aliyu, Abdul, dakuma Baban Abdul (mijin Momma), shi kanshi Dady dayaci wata fitinannan shadda wacce taci sunanta shadda, dakuma su Baffa da fuskokin su ke dauke da annuri, limami ya daura aure tsakanin Alhaji Muhammad Ibrahim da kuma Rukayya Hamisu, inda su Baffa da mutane da dama suka shaida sai murna ake ana hayaniya, sosai Aliyu ke murmushi he's trying his best yaboye damuwan shi dan baiso Dady yagane, today is a happy day for Dady baiso yaga any sign of something a tattare dashi ya shiga damuwa, yanada matsala daya addabi zuciyan shi ainun rabonshi da Aneesa tun ranan nan, yakira layin ta taki dagawa daga bayama kashe wayan tayi gabaki daya, gajiya ma Yayi da amsa gaisuwan mutane ganin kanshi yafara masifan ciwo ya kalli Abdul dake kusada shi shima yana sanye cikin shadda fara kaman tashi yace "am going home" da sauri Abdul yace "me haka? Kasan Dady zai nemeka ko" yatsine fuska yayi yace "stay kai, am having headache, inya tambayeni kacemai naje gida" yana yin maganan yay tafiya yana kallon Dady dake washe baki kaman anmai kyautan makka yana gaisawa da mutane, yawuce ya shiga mota yaja zuwa chan Abuja dan yasan koyaje gidan momma dake nan Suleja dakwai hayaniya kuma baison hayaniya ko kadan, yana danna mota cikin gidan Maman su Rauda na fitowa daga motar ta datai parking, wani natsiyacin kallo tama motarshi ko damuwa baiyi a yabude yafito yay side dinshi batare dayama inda take second look ba ballema yasan wats she's up to, kwafa Maman su Rauda tayi tace "inhar ban koyama Aliyu hankali ba aduniyan nan basunana Kareema ba wanan alkawari ne namaka, wlh kuwa" tai kwafa tawuce dakinta. Bude part dinshi yayi ya shiga yaji ko ina na kamshin turaren wuta lumshe ido yayi yabude dan yana mugun son kamshi kuma yasan aikin Rauda ne hakan yamaida kofar yarufe yya hanyar bedroom dinshi, kaya yarage ya shiga wanka koyaji dadin jikinshi, baiwani jimaba yafito yana yatsine fuska sanye da bathrobe yafada kan gado tareda daukan wayanshi yana kallon number Aneesa yanaso yakira but yasan koya kira bazata dauka ba, ahankali bacci yay awon gaba dashi. _Bangaren su Ammi, Suleja_ Yau jumma'a tun kafin a daura auren wuraren karfe takwas nasafe Momma da kawayenta suka kawo akwati guda goma inda saiti bakwai na Ammi ne dake cike da hadaddun kaya da an dinka wasu wasu kuma ba'a dinka ba saiti uku kuma na Aneesa ne da aka cikamata da kaya na yamma ta harda dogunayen riga Aneesa harda kuka, few kawayen Ammi na anguwan ne suka tarbesu itakuma Ammi taki fitowa har suka tafi anata guda daga baya aka daura hadadden abinci dan tun jiya Dady ya turo da motan kawo abinci Aneesa tama Ammi hadadden lalle bana wasaba ta shirya Ammi cikin wani lace mai kyau sky blue da fari ta rungume Ammi yafi sau dari sabida yanda Ammi tai kyau sanan takawo wani farin babban mayafi ta yafama Ammi, Ammi sai amsan gaisuwa take tana murmushi ka ganta itada Aneesa zaka zaci y'a da kanwa ne, Aneesa itama wani farin lace tasaka mai ratsin pink shima dadin ne yaaaimata takai aka dinka mata tai kyau telan dudda bai aunata ba amma chip chip yamata yafito da shape dinta sosai bana wasaba sai murna take ko ita ke aure albarka. Wajajen karfe uku anguwan ya cika da maza da mawaka ana wake Dady, Baffa ne ya shigo ya leko ya kira Aneesa dake tsakar gida tana nan tai chan tama kasa zama waje daya da gudu tai wajen Baffa a zaure, baki Baffa yarike yace "wai wai wai, masha Allahu, ashe haka yar tawa keda kyau aida kyar naganeki wanan kyau haka" wani irin cute smile tayi cike da zumudi tace "Baffa an daura? Yanzu Abba yadawo mijin Ammi na?" tafada cikeda wani irin murna gyadamata kai Baffa yayi yace "kinsan mezakimin yanzu anjima zamuyi hira, yanzu jeki kawomin maman ki nan dakin mu ta zauna kifito, sabon baban ki keson yimata magana" da sauri Aneesa tace to Baffa tajuya da sauri takoma cikin gida Baffa yakoma waje ko minti daya ba'a yiba shida Dady suka shigo zauren tareda Baffa dakin su Baffa yabude ma Dady yace "shiga ka zauna na aika Aneesa takirata, cikin gidan mata sun cika abinka da gidan sha'ani" shiga ciki Dady yayi ya zauna yana murmushi yanadan girgiza kafa yawani irin kosa yaga Ammi ta shigo. Har gaban kofar dakin Aneesa takawo Ammi dake wani irin jin kunya sosai sanan tawuce takoma cikin gida da gudu, bin bayanta da kallo Ammi tayi tana sauke ajiyan zuciya kafin ahankali tasa hannu tabude kofar dakin ta shiga ciki ahankali da sallama, mikewa tsaye Dady yayi yana yana gyara babban riganshi dayasha lafiyayyen aiki yana kallon Ammi, kasa jure kallon daya ke mata Ammi tayi hakan yasa ta saukar da nata kan kasa, ahankali tashigo tana taku daidai anatse har gabanshi kafin ta tsugunna ahankali zata gaidashi da sauri yawani irin riketa batare daya bari ta tsugunna ba yadago ta tashi tsaye tayi tana kallon

Table of Contents

Chapters

78 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});