Chapter 59
Chapter 59
daina ba, ita kuwa Hibbah duk kunyar Faheem take ji shiyasa ma ta kasa sakewa a haka har dai suka yi bacci. Inna lami kuwa sunkai wajen 3hours a ciki ita da boka kafin............. *by* *Mamyn Najmah* [10/26, 9:27 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *RAYUWA* page5⃣3⃣ *NA* *MAMYN NAJMAH* 🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA* ```watpad@mamyn_najmah2222``` Kafin su fito ya had'a musu wasu k'ullika ya bata "ga wannan ki barbad'a a wajen da kika tabbatar zata tsallaka daga yanzu da kika amsa karya awa d'aya baki yi amfani dashi ba sannan da kinje gida ki barbad'a tana tsallakewa da mintuna biyar ki share, karki karya k'a'ida ko guda d'aya idan aka samu matsala d'aya a cikin mu zai mutu ko ni na mutu ko ke ki mutu" babu ko d'ar a zuciyar Inna lami ta amsa suna k'ok'arin zube masa k'ud'i y katse su "wannan aikin naku yana da had'ari ku bari sai aiki yayi kyau sai ku kawo" nan suka tashi sukayi godiya suka tafi. Suna tafiya suna ta hira a kan maganin da bokan ya basu, sunzo tsallaka wani d'an k'aramin titin da zai sadasu da k'auyen katsalle da yake titi guda d'aya ne sai ji kake k'uuuuuuuuuu wata k'atuwar dab tayi shoki da su delu ma'ana tayi sama dasu a take suka zube a wajen. Can gidan kuwa ana kiraye kirayen sallah dukkanninsu suka tashi mazan suka nufi masallaci yayin da matan sukayi a gida bayan sun idar kuma suka shiga tattare gidan don Daddy yace yau zasu koma gida, suna shirin d'ora girki sai gashi gwaggo ta aiko musu da breakfast mai rai da lafiya. Nan suka amsa tare da godiya aka zauna aka nad'i girkin gwaggo bayan sun gama kuma sukayi wanka Ana ta shirin komawa birni. Ita dai Hibbah bata so komawarsu ba taso zuwa gidan Abu kodan suka juna ta kuma fad'a mata abinda yake faruwa tasan abu zata tayata murna. Haka ba don tana so ba suka gama shiryawa suka nufi gidan gwaggo don d'aukota su tafi sannan su yiwa malam sallama, da suka je ma itama ta shirya suka kuma yiwa malam godiya suna shirin fita saiga Abu ta shigo ta gaishe dasu momy sannan ta rumgume Hibbah tana murnar ganinta ita ma Hibbah cikin d'auki da murna ta rumgume Abun, Abu tace "na tayaki murna Hibbah naji dad'in wannan al'amari ashe dama rabon kiga dangi ne ya kaiki birni" Hibbah ta kuma k'amk'ameta sai dai taji bata rumgume Abu sosai ba don wani abu ya tokare tsakaninsu Hibbah ta d'an saketa ta d'an matsar da ita daga jikinta tana son ganin mene abun da ya hanasu had'a jiki sosai. Ido Hibbah ta zaro da mamaki tana kallon Abu tayi k'asa da murya tace "Abu me nake gani ciki?" Abu ta d'an buge kafad'art "ni har kin bani tsoro wallahi ji nake wani abun ne, to cikin bashi bane ribar aure" Hibbah ta rik'e baki tana mamaki wai Abu ceda ciki kenan itama dole ne ta k'unshi nata?" Ta girgiza Kai Anya kuwa zan iya? Abu ta dafata "tunanin me kike yi?" "Ba komai waya fad'a miki nazo garin nan?" Hibbah ta tambaye ta "Abban Amina ne ya fad'a min" kallon ta Hibbah tayi da mamaki "waye kuma Abban Amina?" Abu tace "au a shefa baki santa ba, 'yar da na Haifa ce ta rasu" "au wai kina nufin wannan cikin bashi ne na farko ba? Tab kina k'ok'ari" "k'ok'arin me?" "K'ok'arin d'aukar wannan cikin" dariya ma Hibbah ta Bawa Abu tace "kema zaki d'aukane" Saudat dake gefensu tana jin duk abinda suke cewa tace "tab har na hango Hibbah da k'aton ciki nan kina tafiya da k'yar" ta kuwa kwashe da dariya. Hibbah ta harareta bata ce komai ba, Saudat ta cigaba "kinga dama Daddy yace nan da sati biyu zaki tare kinga kenan nan da wata tara zamu so suna" Abu ta kalli Hibbah da mamaki "au Hibbah kinyi aure kema?" Da Sauri ta katseta "k'arya fa take yi" Saudat tayi zaraf "wallahi da gaske nake sanadin auren ne ma yasa muka zo garin nan kuma ki tambayi su gwaggo" "na yarda ma wallahi, to ke Hibbah ai ba'a b'oye abin alkhari" ita dai Hibbah bata ce komai ba sai hararar Saudat da take yi. Suna nan zaune sukaji sallama babban mutum ne wai baba yake nema, baba ya tashi ya fita abinda ya gani ne ya sashi juyowa gida da sauri ya shigo duk a hargitse kallon mamaki su Abba duk suke masa suna tambayar lafiya? Yama kasa magana waje kawai yake nuna musu ganin ya kasa magana yasa suka mik'e suka fita don ganin abinda ya rikita baba. Inna lillahi kawai suke kira duk sun firgita da abinda suka gani, Inna lami ce da delu a kwance a k'ofar gidan inna k'afafunta sun cire fit babu hannaye ga idanunta ba duk bata gani sai surutai take yi "wallahi Hibbah saina ga k'arshenki dama saida boka halakakke yace karna sake na bari ki dawo k'auyen nan idan kika dawo akwai mummunan al'amari da zai faru kuma na gargad'eki karki dawo amma sai da kika dawo gashi nan munje wajen bokan mun tadda shi yana ci da wuta don haka kema sai na k'onaki" sai kuma tasa wata muguwar dariyar da ta tsorata su duka wajen ga 'yan k'auyen duk sun zagayeta. Sai da tayi mai isarta sannan ta tsagaita dariyar "na tsaneki Hibbah bazan iya barinki kiji dad'in rayuwa ba shiyasa muka tafi wajen wani bokan yayi amfani dani ya bani wasu k'ullika yace ina komawa gida na barbad'a miki kar na huce awa d'aya ban barbad'a ba, kuma idan na barbad'a miki kina tsallakewa na share kar yayi mintuna biyar ban share ba idan ba haka ba ni ko shi d'aya a cikinmu zai mutu, mun tawo akan hanyar mu ta dawowa mota ta bigemu........" Sai kuma tasa wata muguwar dariya can kuma tasa kuka kamar yarinya wai ciwo jikinta yake mata "wayyo malam jikina ciwo" sai ta kuma sa dariya "malam kaima nice nayi maka asiri don karka koma garinku saboda inasonka bayan nayi maka asiri ne na fad'awa baba shine ya aura maka ni. Kuma nice na rabaka da Aysha da Hibbah nasa ka tsanesu nayiwa Aysha sharrin zina nasa ka rabu da ita Hibbah ma nice na tura mata kwarto d'akintaaaaa!" Sai ta kuma fashewa da da dariya. Gaba d'aya jikinsu yayi sanyi sai kallonta suke yi hauka take sosai tana ta fad'in abinda ta aikata, delu kuwa dake can gefe ko numfashi bata yi da alama ma ta mutu. Rahmatu da Hibbah sun had'a Kai sai kuka suke yi Rahmatu wani zugi take ji a zuciyarta ace mahaifiyarka na aikata shirka yanzu kuma ta haukace a wajen bin bokayen nata gashi ba hannaye ba k'afafu ba idanu wannan kad'ai ya ishi masu yi isara. Mijin delu dake gefe ya dubi baba "malam Mukhtar kaga *RAYUWA* ko kaga aikin bin bukaye ko wallahi nayi danasanin kasancewarta mata a wajena Allah ya isa tsakani na dake delu bazan yafe miki ba" daddy yayi saurin kace shi "a'a malam ba'ayi haka ba ba'a bin mamaci da mummunar addu'a kayi mata fatan rahmar ubanjgiji kawai" mijin delu ya gyad'a kai zuciyarsa na k'una yace "Allah yayi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63