Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 23

Chapter 23

Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

daidaita miki shi zan d'auki babban mataki akanki, ke kuma Kausar saboda zubda girma har dake ake yiwa yarinyar nan rashin mutunci ko? Ku cigaba," Kausar tayi k'asa da kai Safiyya tace "kiyi hakuri momy," harararta momy tayi tare da yin ciki. Safiyya ta kalli Kausar, Kausar tace "Safiyya dafa matsala kalli yadda momy take mana fad'a kan waccan banzar," Safiyya tace "hmm ai sainayi maganinta," Saudat ce tayi sallama ta k'araso kusa dasu ta xube a kujera tace "wash Allah wallahi na gaji, Safiyya kun jima da dawowa kenan," Ta fad'a tana kallon Safiyya, Safiyya tace "eh tun kafin Aunty su huce muka tawo," Saudat tace "kuna nan a zaune tunda kuka dawo?" D'aga mata kai Safiyya tayi tace "eh mene kike tambaya?" Saudat tad'an kishingid'a tace "kunga shigowar Hibbah? Tun d'azu da aka tashi muketa nemanta amma bamu ganta ba," harararta Kausar tayi tace "Saudat wannan wane irin maganar banzane, kinga munyi miki kama da masu gadi ne daza kizo kina tambayar mu wata banzar 'yar aiki," Saudat taji haushin furucin Kausar dama kuma ba shiri suke ba, Saudat tace "kinga dai aunty Kausar bada ke nake ba kiyi hakuri kiyi min shiru," Safiyya ta kalleta tace "ai gara ita ta tanka miki ni kina tunanin zan tanka miki ne yarinyar da a kanta momy tayi min fad'a, kuma ki fad'a mata tunda tasa momy tayi min fad'a sai tayi data sanin zuwanta gidan nan" Saudat ta buga tsaki tare da mik'ewa ta kalli Safiyya tace "aikin banza don momy tayi miki fad'a saiki huce a kanta? To bismillah," ta kalli Kausar data d'ora k'afa d'aya kan d'aya tana karka d'awa, Saudat tace "a shawarce da zaki daina biyewa wannan daya fiye miki, kinfi kowa sanin halinta matarda ko gidanta bataso aje shine kike mak'ale da ita, duk soyayyar da zata miki a gaban su momy ne kina zuwa gidanta zakiga bambanci ," tana gama fad'in haka ta hau stairs, binta da ido sukayi musamman ma Kausar tayi mamakin Saudat, kuma ta kasa cewa komai, suka kalli juna Safiyya a ranta ta yarda da kalaman Saudat don kafin aunty tayi aure saida tazo tana fad'awa momy. Ita kuwa Saudat d'akin aunty ta nufa donta duba ko Hibbah ta dawo, shiga d'akin tayi da sallama ta k'arasa kusa da Hibbah tana murmushi tace "shine kika gudo koh? Mukaje can muna ta nemanki." Hibbah tayi dariya tace"wallahi gani nayi wannan mutumin yana neman takurani ne shiyasa," Saudat ta d'an matso kusa da ita tace "Hibbah baki fahimci Ya Jabeer bane yana da halaye masu kyau ki tsaya ki fahimce sa," Hibbah ta d'an kalleta tace "kinga Saudat nifa bacci nake ji ki rabu Dani da halin mazan nan duk Wanda yazo wajenki buk'atarsa d'aya ce ya nemi jikin ki," "a'a Hibbah karki yanke hukunci" Saudat tayi saurin katseta, Hibbah tayi murmushi tare da mik'ewa ba tace komai ba ta nufi toilet ta d'an watsa ruwa ta d'auro alwala sukayi sallama da Saudat, tayi addu'o'in ta ta kwanta. Kamar yadda ta saba tashi haka yauma ta tashi, ta d'auro alwala ta zo tana ta nafilfili tana rok'on allah ya k'ara mata juriya da hakurin zama da Kausar, tana nan zaune har akayi assalamu ta tashi ta gabatar da sallah, ta d'auko Qur'anin aunty ta shiga karantawa, bayan ta idar ta d'ora da azkar har gari yayi haske sannan ta ajiye ta sauko k'asa ta nufi kitchen. Hadiza ta gani tana kiciniyar had'a breakfast, ta gaisheta suka shiga had'awa tare. Suna ta hira har suka gama suka kai dinning Hibbah ta jere kayan, Hadiza dama ta ware nasu daban ta koma sukaci sunata hira. Sama Hibbah ta koma tayi wanka ta shirya cikin wani material Orange tayi masifar kyau ta gyara fuskarta, wayarta ta d'auka tanata game har wajen sha d'aya sannan taji motsin 'yan gidan. Tana zaune wajen sha biyu Hisham ya turo k'ofa ya shigo, ya k'araso gaban Hibbah yace ""aunty Hibbah kizo inji daddy'n Nawaz," ji tayi gabanta ya fad'i duk da bata sanshi ba, mayafinta ta d'auka tasan tafiya zasuyi k'irjinta na bugawa ta fita. A parlor'n k'asa taga 'yan gidan a zazzaune harda su momy ita da mamy amma banda aunty Kausar da alama tana tare da mijin nata ko kuma tun jiya ta huce ta gaishe da su, momy tace "yauwa kije yana waje yana jiranki, ki kula da kanki Hibbah ki d'auke kanki akan duk abinda za'a yi miki, can yana da bambanci da nan kinji?" D'aga mata kai Hibbah tayi k'aunar momy na kuma shiga ranta, tace "na gode momy allah ya saka da alkhari," momy tace "ameen Hibbah," mamy ta kalli su Safiyya tace "ku tashi Ku rakata mana," Saudat ce ta fara mik'ewa taja hannun Hibbah suka fita, ita kuwa Safiyya dama danna wayarta take yi data fito ma cigaba tayi da abinta. A mota suka tarar dashi motar a bud'e shi kuma ya zuro kafarsa d'aya waje yanayiwa Nawaz wasa, suka k'araso wajen inda yake suka gaishe shi ya amsa tare da d'agowa ya kalleta, ji tayi gabanta yayi wata muguwar fad'uwa ganinsa tayi kamar Faruq komai nashi irin na Faruq bambancinsa da Faruq kawai girmane amma hatta maganarsu ma iri d'aya ce. Ya kalli Nawaz yace "boy shiga mota mu tafi gida," yaron d'an kyakykyawa yace "to daddy," ya kalli su Saudat yace "Aunty Saudat wace wannan?" Saudat tayi murmushi tace "sunanta aunty Hibbah," ya kalli Hibbah yace "aunty Hibbah," Hibbah ta kalleshi tana murmushi. Ya kuma kallon Saudat yace "aunty Saudat aunty Hibbah tana murmushi don na Kira sunanta," Faheem ne ya katseshi da cewa "Nawaz ka shiga mota mu tafi mana," da sauri yaron ya juya ya bud'e motar tare da shiga yana yiwa su Hibbah murmushi, Saudat ma ta bud'ewa Hibbah gidan baya ta shiga sukayi sallama, Faheem ya tashi motar suka huce. Safiyya na ganin sun tafi ta komawarta gida dama ita Danna wayarta take. A mota Nawaz sai surutu yake tayi shi kad'ai, yace "daddy aunty Hibbah gidan mu zamu da ita?" Faheem dayake tuk'i yace "eh Nawaz ita zata dinga zama tare da kai idan ka dawo daga school, tayi maka wanka ta koya maka homework ta dafa mana abinci," Nawaz jin ya ambaci homework yasaki ihun murna "yeeeh daddy nima na samu aunty," ya juyo yana kallon Hibbah yace "aunty Hibbah har unguwa zaki dinga zuwa dani momy na bata zuwa unguwa dani wai nayi girma, ai banyi girma ba ko aunty?" Hibbah ta d'aga masa kai tana murmushi tace "eh Nawaz zan dinga zuwa dakai," lokaci d'aya taji k'aunar yaron ta shiga ranta, shi kuwa Nawaz cigaba yayi da wasanshi har suka k'araso gidan Mai gadi ya bud'e gate d'in gidan yana yiwa Faheem sannu dazuwa. A parking lot ya ajiye motar suka fito, Faheem yayi gaba shi kuma Nawaz ya zo ya rik'e hannun Hibbah suka parlor yana ta yi mata surutu. Suna shiga suka tararda Faheem a parlor yana k'ok'arin kunna TV, bai kallesu ba ya kunna TV ya dawo ya zauna yana kallon labarai, a k'asa Hibbah ta zauna Nawaz yana kan cinyarta, Faheem yad'an kalleta kad'an ya kawar da kansa yace "Hibbah sunanki ko?" Hibbah ta d'aga kai "eh" yace "Hibbah aikin ki a gidan nan shine girki,

Table of Contents

Chapters

63 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});