Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 33

Chapter 33

Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel 1,204 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

mata don ganin wajen aiki zata tafi, azaton shi yau dai zata zauna ta kula da d'anta domin lafiya tafi kud'i, mai makon ma ta dafo wani abu da tasan mara lafiya zai buk'ata ta kawo musu sai tazo musu k'iyau miyau. Sai takardu a hannu sai kace wadda zata kadance kundin ilimin duniya, shi yasan duk wannan aikin da take yi d'anta ya fishing daraja a matsayinta na 'ya mace bata da abinda yafi d'anta mahimmanci a wajenta. Ta dubi agogo "Zan wuce wajen aiki su momy suna zuwa da abinci munyi waya da Safiyya," ko kallon ta bai yi ba "basu da hakkin bani abinci wannan aikinki ne ba nasu ba kuma baki damu ba zaki tafi uzurinki, akwai ranar k'in dillanci, shiyasa wasu 'ya'yan sam basa tausayin iyayensu kuma ba komai ke janyowa ba sai irin wad'annan abubuwan, baka san wahalar d'an daka haifa ba, shi zaiji k'anka bayan ke ba haka iyayenmu suka yi miki ba," ta d'aga mishi hannu cikin hayayyak'owa "bafa tsoranka nake ji ba da zaka dinga fad'amin abinda kaga dama, ka fad'amin ayar da tace don ka aure ni na ciyar dakai cewa akayi a ciyar dani, kuma ni haka tsarina yake bazan canza ba," "ke kuma akace kimin biyayya don ki samu aljanna to idan na nemo abinda Zan ciyar dake yana cikin biyayyar aure ki dafa min, to don haka ki kiyaye yimin ihu aka kinsan ni ba sa'anki bane sannan a k'ark'ashi na kike kin gane koh?" A fusace ta fita, ya cije leb'e wato yayi shi kad'ai ita bazata saurareshi ba. Duk iyalan gidan sunzo momy, daddy yake yana gari da Faruq su Saudat suna makaranta shiyasa basu zo ba, suna zuwa Faheem yace zaije ya d'an kintsa a gida, momy tayi mamaki da Faheem yace mata wai Kausar ta tafi aiki. Da yamma ya kasa jurewa ya nemo number Aysha, ringing biyu ta d'auka bayan sun gaisa tace "Dan Allah yaya kayi hakuri ina tafe an jima zan shigo ya jikin boy d'in nawa?" "Karki samu damuwa da sauk'i sosai," "to harna ji dad'i Allah ya k'ara sauki, yauwa yaya don Allah ina son ganin Hibbah zamu d'an tattauna akan maganar Jabeer wallahi ya dameni yana so a yi auren nan kasan wajen aikin mu d'aya," Gaba d'aya ji yayi wani abu mai Kama da bugun guduma a tsakar kansa, ransa babu dad'i yayi ajiyar zuciya wani abu na nuk'urk'usar zuciyar sa, "yaya kana jina dai ko?" "Hmmm ina sauraronki, bata nan taje gida ne kwana biyu bata dawo ba bansani ba ko lafiya, bani address d'in gidan nasu," "Oh to Allah yasa lafiya don nima ban nemeta ba kwana biyu, ai gidan Alhaji sani ne gidan nasu fa," "Alhaji sani dai wanda na sani?" Faheem ya tambaya "eh shine yaya," sukayi sallam. Sai ya samu kansa da............ *by* *Mamyn Najmah* [10/26, 9:24 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *RAYUWA* page3⃣4⃣ *NA* *MAMYN NAJMAH* 🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION* D.B.W.A *DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA* ```Tabital pulaaku group ina kuke? Wannan wannan page d'in d'ungurungun nakune, Allah ya barmu tare cikin so da k'aunar junanmu.``` Sai ya samu kansa da kasa samun nutsuwa sai yaje gidansu Hibbah don gaskiya yana so yaga Hibbah, dayake har lokacin momy na nan sai yace mata yana zuwa ya zari key ya fita, direct gidan Alhaji Sani ya nufa, Alhaji Sani ya tare shi suka shiga cikin parlor babu kowa cikin mutumci suka gaisa sosai Alhaji yana tambayarsa ya iyali, suka d'anyi shiru na wasu 'yan dak'ik'u Alhaji yana mamakin zuwan Faheem gidan sa ko Alhaji ne ya turosa ya kasa jurewa yace "Faheem Alhajin ne ya turo ka?" "A'a dama ina sone mu gaisa da Umma tana nan ne?" Alhaji yayi murmushi "to to naji dad'i bara nayi mata magana tana d'aki," Alhaji ya mik'e ya shiga d'aya daga cikin d'akunan cikin parlor'n, jim kad'an sai ga su sun fito shi da umman, Alhaji sukayi sallama da Faheem don shi fita zaiyi. Faheem ya zamo daga kujerar da yake zaune ya durk'usa har k'asa ya gaishe da Umma ta tambaye shi Kausar da Nawaz (ta tab'a ganinsa ne a hoto da Aysha ta nuna mata shi). Yace "wallahi kinga ma shiya taso ni nazo don baijin dad'i ne, kuma ya damu da Hibbah don ciwon da sauk'i akan damuwar," Umma tayi murmushi "Allah sarki bamu sani ba ai da anje an dubo shi Allah ya Bashi lafiya, bawan Allah haka so yake gamuwar jini, badai abinda zamuce muku sai fatan alkhari, Allah ya biya da aljannah," yayi Jim wani abu ya tab'o zuciyarsa yaji dad'in kalaman Umma, yana son ta tashiga ransa sai yaji don me bazai fad'a mata damuwarsa ba damin a maganarta ya fahimci bata da masaniya akan abinda ya faru har Hibbah tayo musu yaji. A nutse ya fad'awa Umma komai abinda ya kasance har yajin da Hibbah tayi musu na tawowa ba tare da saninsa ba, Umma ta kad'a kai "ikon Allah wallahi bansani ba ni nan b'oye min tayi bata fad'a min ba cemin tayi kunyi tafiya ne ni kuma nasan bata iya k'arya ba kuma Allah bai nufa munyi maganar da Alhaji ba, kai amma banji dad'i ba kuma bata kyauta ba. Ita d'in me tafi k'arfin ayi mata fad'a ne idan tayi badai dai ba ka tsawatar mata wannan shine tarbiya, wato tasan idan ta fad'a zanyi mata fad'a shiyasa b'oye tak'i fad'a min, don Allah kayi hakuri," Faheem sai yaji wani iri kamar Umma da girmanta da k'amarta ta dinga Bashi hakuri "a'a Umma babu komai wallahi," wadda take yiwa Umma share share ce tazo d'aukar abu Umma tace ta turo mata Hibbah, sai gata kuwa tana ganinshi tayi turus, zuciyarta tana bugawa kamar zata tarwatse ko a mafarki bata tab'a tsammanin shi ba, ta zube "ina yini Daddy," ya dubeta ya had'e fuska "bazan amsa ba Hibbah tunda nayi fad'a kikayi fushi har kika tawowarki gida bako sallama, kin bani girma kenan? Gashinan kinsa yaronki rashin lafiya yana asiiti kin kyauta kenan?" Ta dubeshi a razane hantarta har ta kad'a ta had'iyi miyau dak'ar idanunta sun cicciko hawaye, Nawaz Allah sarki dama tasan za'a rina bata yi masa adalci ba, ita ma tana nan har d'an zazzab'i tayi shak'uwarsu tayi yawa ita da Nawaz, Allah sarki sak taji tausayin yaron da k'aunarsa na kuma shiga ranta. To yaya zatayi idan ba ta barwa Faheem gidansa ba don yayi mata hannunka mail sanda. Umma kuwa ta rufe ta da fad'a "ni ban san sanda kika koyi k'arya ba halin hofi Hibbah don me baza'a fad'a miki kinyi ba dai dai ba kinfi k'arfi a tank'wara kine, to ki shiga hankalinki idan ka rasa mafad'i a duniya ka shiga uku, wad'annan mutanen sunan k'aunarki mutunan da suka d'aukekan tamkar d'an uwa na jini suke d'awainiya dakai, tun wuri ki sauya tunani ni ban goyi da bayan ki raina na gana da ke ba d'an halak baya manta alkhari, wallahi kar na kumaji kinyi irin wannan shirmen kuma ki d'auki kayanki ki koma, ki bashi hakuri yanzu," Zuciyarta tayi rauni jinkinta yayi sanyi ganin ran Umma ya b'aci sosai gashi tana ta yi mata fad'a abinda bata tab'a yi mata ba, da k'yar muryarta

Table of Contents

Chapters

63 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});