Chapter 54
Chapter 54
da kanta Inna ta mik'e "bara a kawo muku ruwa ko?" "A'a ki barshi mun gode" Faheem yayi saurin dakatar da ita donshi ko me za'a yi masa bazai iya cin wani abun daya fito daga hannun lami ba. Abba yace "wajen mai gidan muka zo gashi ance baya nan zai iya kaiwa zuwa yaushe kafin ya dawo?" Inna ta kuma washe baki "ayya ai yanzu zaku ganshi ya dawo ba jimawa zaiyi ba" Abba ya jinjina kai "to shikenan bara mu jira sa" Hibbah sai b'oye kai take kamar munafuka, su kuwa su momy dasu Saudat su Aunty duk mamakin inna sukeyi yadda take ta wani washe baki kamar gonar auduga. Suna nan zaune har wajen k'arfe hud'u saura malam bai dawo ba duk sun k'osa ya dawo musamman Daddy, Faheem ya kalli inna dake ta son jansu da hira "anya kuwa zai dawo yanzu ga la'asae har ta gabato ko dai muje mu dawo ne?" "Eh to ko zakuje ku dawo d'in amma idan sak'one Ku bayar a ajiye masa" duk suka kalleta da mamaki, ita kuwa ko a jikinta ta mik'e ta d'auko wata bak'ar buta wadda rabon da a wanketa har anmanta ta d'ebo ruwa a ciki ta kawo musu "ga ruwan alwala naga lokacin sallah yayi" Faheem ya mik'e "a'a mun gode muna da ruwa a mota" ta dube shi ta d'an b'ata rai ya fara bata haushi "au k'yamarmu kake yi 'yan k'auye ba mutane bane?" Daddy shima ya tashi yana bawa inna hakuri "kiyi hakuri baiwar Allah ba k'yamarki yake yiba, bara muje zuwa anjima zamu dawo" ta kalli su momy da suka kasa ma magana don matar mamaki take basu "ku tashi mu k'arasa can in anjima ma dawo." Suka mik'e zasu tafi Hibbah sai b'oyewa take a bayan su Saudat ita kuma Umma mamaki ne tab ya cikata ya akai Inna bata ganeta ba meta canza. Har k'ofar zaure inna tayo musu rakiya sai surutu take yi musu sudai basu kulata ba sukayi gaba. Ta koma cikin gidan tana ta d'auki ta dubi Rahmatu "ke yanzu haka ake tarbar bak'i musamman ma wad'annan 'yan birni dasu kina ganinsu kinsan kud'i ya zauna musu ai ko baza su shaba sai ki kawo musu ruwan, ni wannan d'an gayun ne yafi bani haushi sai wani iyayi yake yimi" sai kuma ta washe baki "Kai Allah mun gode maka may be sunzo tafita ne da malam can birnin shikenan zamu bar zaman k'auye" ta saki gud'a. Su Daddy kuwa suna fita suka ce su sallah zasu fara yi su matan su shiga gidan su Umma idan yaso su daga baya zasu shigo. Haka kuwa akayi Umma tayi musu jagorancin shiga cikin gidan suka shiga da sallama lokacin gwaggo tana sallah bata amsa musu ba. Umma ta shigar dasu d'akin gwaggo ta shimfid'a musu tabarma suka zauna ta dubesu da murmushi a saman fuskarta "Hibbah tashi kije ki amso musu ruwan alwala mun mance ba'a amso ba" momy tayi saurin tare ta "a'a idan akwai a nan zuba mana muyi dashi" "zaku iya kuwa amfani dashi karya ja muku matsala tunda ba sabawa kukayi ba?" Mamy ta mik'e "nuna min inda ruwan yake ni na d'iba don naga kamar kina tsoro ne" "a'a bara na d'ebo muku" Umma ta tashi ta d'auko butocin gwaggo sababbi guda uku ta zuba musu ruwan a ciki, momy da mamy da kuma Aunty suka d'auka. Suna fita gwaggo ta idar da sallar ta dubesu "sannunku da zuwa kunsha tafiya ya hanya?" "Yauwa alhamdulillah" "kunzo lafiya?" "lafiya lau mun same Ku lafiya?" Nan suka shiga gaggai sawa, Nawaz da Hisham suka gaishe ta. Hibbah ta kalli gwaggo cikin shagwaba "wai gwaggo yanzu don Allah wai baki gane ni ba?" Gwaggo ta tsaya kallonta tana mamaki fara tattafa hannu tana salati "Hibbah Kece? Alhamdulillah Allah kaine abin godiya Hibbah dama ashe zan kuma ganinki?" "To ba gashii kin ganni ba, ni fa ba mun b'ata da wannan tsohuwar tunda bata ganeni ba" Hibbah ta fad'a cike da shagwaba "ayya Hibbah ba haka bane ni ban tab'a tunanin zan kuma ganinki ba, na d'auka tunda lami tace karki kuma dawowa bazaki dawo d'in ba." "To ba gashi yanzu na dawo ba ina Abu?" "Gaskiya naji dad'i da zuwan nan naki, Abu tuni tayi aure Hibbah har da 'ya'yan biyu ma" Hibbah ta zaro ido "gwaggo Abu ce ta haihu har yara biyu?" "Eh mana Hibbah kema da kina nan da yanzu da naki, wad'annan su waye? Ko a wajensu kike aikin?" Gwaggo ta tambaye ta. Gyad'a Kai tayi "eh gwaggo a gidansu nake aiki sune suka inganta min rayuwa suka tallafa min suka ni a makaranta sun d'auke ni tamkar 'yarsu" "Allah mai iko mun gode da wannan kulawar da kuka yi mata Allah ya saka da alkhari ya k'ara bud'i mun gode" Kausar tayi murmushi "babu komai gwaggo" su mamy suka shigo suka gaggaisa da gwaggo suma gwaggo tayi musu godiya. Su Hibbah suka tashi don zuwa suyi alwala Saudat ta kalli Hibbah tana murmushi tace "Hibbah banji kincewa gwaggo kinyi aure ba" Hibbah ta harareta gwaggo ta rik'e baki "au Hibbah kema kinyi aure shine ba'a fad'a mana ba" "gwaggo k'arya take fa" Saudat tasa dariya "wallahi gwaggo tayi aure amma bata tare ba, munzo wajen baba ne" Hibbah ta kai mata duka tare da fita ta d'auki buta Nawaz ya biyota wai shima alwalar zaiyi. Su Safiyya ma suka fito Saudat tana ta yiwa Hibbah dariya, suka yi alwala suka koma d'akin. Bayan sun idar da sallah su momy suka shiga hira da gwaggo kamar sunsan juna anan suke fad'a mata tsakanin su da Hibbah kuma sun tabbatar mata da cewa Hibbah da gaske tana da aure d'an uwanta ma take aure amma bata tare ba, gwaggo ta bayyana murnarta sosai suna cikin hira Daddy ya kira layin momy ya fad'a musu sun dawo. Momy ta fad'awa su Umma taje ta shigo dasu, gwaggo ta fito da manyan tabarmi aka shimfid'a a k'ofar d'akin su Daddy suka shigo a tare da malam (mijin gwaggo) suka gaggaisa dasu gwaggo, sukayi musu godiya da kuma yi musu murnar ganin d'an uwansu da sukayi. Bayan sun gama gaggaisawa gyara zama ya fad'a musu abinda ya kawo su ya d'ora da cewa "to shine muka zo don mu tabbatar amma ita Umman Hibbah tace wai ba ita bace ita a nan aka haifeta kuma wai iyayenta basu mutu ba suna raye" malam da gwaggo suka yi shiru kamar ruwa ya cinyesu babu wanda ya iya magana, malam yayi k'asa da kai yana tunanin dole yau ya bayyanawa Aysha cewa ba sune mahaifanta na asaliba don ranar wanka ba'a b'uyan cibi. A hankali ya d'ago kai ya kalli duk su Abba da suka maida hankulansu a kansa ya dubi Umma yace "tabbas Aysha ba mune asalin mahaifanki ba" a razane Umma take kallon sa da alamomin tabbaya k'unshe a fuskarta. Malam ya cigaba "bamu muka haife ki ba kuma da dukkan alamu wad'annan mutanen sune 'yan uwanki da mukayi ta nema bamu samu ba, yau zan baki labarin yadda akayi muka same ki" "Ranar wata juma'a da yamma na dawo daga gona na hango ki kinata............... *by* *Mamyn Najmah* [10/26, 9:27 PM] Maman Najma
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63