Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 27

Chapter 27

Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel 1,199 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

da lullub'e kanta da mayafin rigar, ta shafa powder da lipstick ta feshe jikinta da daddad'an turarukan da aunty ta bata, ta rik'e hannun Nawaz d'an kad'afi duk inda ta cire k'afa ya maida sawunshi, shiyasa suke kuma shak'uwa. Yana zaune cikin motar ya kasa d'auke idanunsa daga kanta ashe duk ganin da yake mata bai gama ganin baiwar da Allah yayi mata ba, tayi masa kyau shi dai yana k'aunarta a ransa, tak'i goguwa a zuciyarsa wani d'an sataccen murmushi tayi masa, ikon allah sai yaji ta tafi dashi gaba d'aya. Ya fito ya jingina da motar komanta ya burgeshi ya rik'o hannun Nawaz yana kallon kyakykyawan yaron, a kunyace ta gaisheshi don itama d'in yau ta k'are masa kallo. Bak'ine kyakykyawa wato irin black beauty d'in nan hancinsa dogo har baka shi ya dad'a fito da sigar kyansa ga shiga da tsari, yana sanye da wani laushashshan boyel yayi matuk'ar kyau ga nutsuwa da allah ya bashi. Ya kalleta da murmushi a fuskarsa yace "Hibbah naji dad'in ganinki da baki fito ba bazanji dad'i ba sai na tafi zuciya ta tana wasi wasi kina jin sak'ona wajen Aunty Aysha na dameta da batunki, Hibbah ki godewa Allah dan ba k'aramin so nake miki ba," tayi murmushi "uhm to na gode itama tana fad'amin," ya kuma murmushi "Aunty sarkin yak'ina ce koda yake itama tasan irin son da nake miki so ne na tsakani da Allah, gashi kuma rowar magana kike yi min so nake naji muryarki dad'i take yi min," ta d'an kalle shi "to me kake so nace?" "Hibbah kenan nidai fatana ki amince min muyi aure, amma fa ban b'oye miki ni mutum ne magidanci mai iyali da mata na da yara na uku ban miki tsufa ba dai ko?" Ta kuma murmushi "aure nufi ne na Allah," "nasan hakan kina nufin kin amince kina so na kuma zaki aure ni?" Tayi shiru, ya karyar da kai yace "hmm Hibbah kinyi shiru har cikina ya d'uri ruwa fa," tayi dariya "sai kace wani mai lefi?" "Ai gara ace lefi nayi zuciyata ta kasa nutsuwa," tad'an sauke ajiyar zuciya "to ka bari sai naje na fad'awa ummana." Ya dubeta a nutse "shikenan iyaye sune gaba da komi Hibbah na baki dama Amman dai ki tausayawa bawan Allah nan, Zan Kira ki a waya naji yarda kukayi," ya bawa Nawaz kud'i "Nawaz rik'ewa Auntyn ka ko?" A daidai sanda motar Faheem ta sanyo kai ko kallonsu baiyi ba ya shige cikin harabar gidan, 'yar hantar ta saida ta motsa sukayi sallama da Jabeer ya huce sukuma suka tawo gida. B'angaran Faheem kuwa yana shiga ya zauna kan gado gami da jefar da takardun yayi jim zuciyarsa zafi take da tana tafasa sai yaji gumi ta kowanr kofofin gashinsa kamar Mai had'iyar wuta, ya kasa sanin wannan abu ciwo ne ko lalura ne ya rasa meke masa dad'i, ya huro iska mai d'umi a bakinsa zafi dad'a k'aruwa yake a ko ina na jikinsa, mik'ewa yayi ya shoga toilet ya sakarwa kanshi shower snyin ruwan ya ratsa shi had zuciyaarsa, bai san iya lokacin da ya d'auka ba sannan ya fito ya kunna AC ya kwanta ya d'ora kansa bisa pillow ya lumshe idanunsa. Yana tunanin wai shin me yasa ya damu kansa da yarinyar nan? Shi fa ba sabgarta yake shiga ba don me yake jin zafo don ya ganta da wani ina ruwanshi da sabgarsu? Don me zai tunzura haka don ta fit a bada izininshu bane ko kuwa metayi masa ya b'ata ransa har hankalinsa ya tashi haka? Ji yayi anyi masa kiss gami da shafo sajensa, juyowa yayi ya rumgumota yayi ajiyar zuciya, ya lalubo abinshi duk lefinta ne da bata tarairayarsa bare ta kwantar masa da hankali in ya shiga damuwa. Juyowa tayi suna kallon juna abinda ta gano a idanunsa ya tabbatar mata akwai rikici wani abu ya tab'o mata shi. Ta kuma k'ura masa ido "dear me yake damunka ne naka ka sauya ba kamar yadda nake dawowa na sameka ba," bai fad'a Mata abinda me zuciyarsa ba sai dai yace Mata wai baijin dad'i tunaninta da kewarta suke damunsa, nan ta shiga yi masa kisses masu zafi don k'ok'arin mantar dashi dan tasan lefin tane Sam bata bashi kulawa kullum ita tana wajen aiki kamar agogo.. *** Hibbah na zaune a d'aki taga mutum kawai a gabanta a karo na biyu ya kawo mata ziyarar bazata yunk'urun guduwa tayi ya kuwa yi azamar cafkota kamar 'yar tsana ya rik'e ko motsi bata iyawa, tasa kuka mai ban tausayi yau ta gamu da gamonta kashinta ya bushe in dai kisa ne yau Faruq ya karta. Ya tallafo hab'arta ya juyar da kanta gefe, tsananin bugun zuciyarta yasa taji zata fad'i don dai ya rik'eta ne amma da tuni ta fad'i. Shi kuwa Faruq tamkar wata sabuwar halitta yake ganinta d'an hakin da ka rain a shike tsone maka ido, wai Hibbah ce macen da ya kasa jimiri da dakewa akanta so guda ne kamar Hibbah babu abinda yake buri fiye da ita a *RAYUWA RSA*, duk tsarinsa ya wargaje d'aya bayan d'aya abin har mamaki yake bashi ya tashi hankalinsa idan yana zancen zuci sai ya fito fili yaji yana sambato. A yau tausayi take Bashi a yau ji yake ba mace mai k'imarta, a yanayin sonta da yake addabarsa, don't me why not baisan dalili ba? Ya sassauta murya "Hibbah why? Why Hibbah? Me yasa nake son ki wallahi babu dad'i akwai wani abu ne daga Allah, ni fa na haukace akanki Hibbah ke baza ki Sani ba har sumbato nake idan sonki da tunaninki sukayi min zabi, ranar dana ganki da wannan guy d'in kasa barci nayi Hibbah, son nan shu'umi ne ya canzani Hibbah ya canza min manufa a kanki ki manta da baya daya kasance kuskure ne don a da can ban iya tantance sha'awar da nake miki yanxu kyauta kika mallaka min kanki bazan iya yi miki komai ba sai Allah yasa aure a tsakanin mu Hibbah bud'e idanunki ki dubi masoyinki." Hawaye ne yake zuba a idanunta, yasa hannu ya lakuto hawayenta ya shanye kuma sassauta murya yayi "Hibbah kina sona kuwa?" Saura kad'an ta fad'i yayi saurin tarota kanta yayi gingirim. "Hibbah" ya fad'a da rad'a, wani abu ke taruwa cikin idanunsa, tsorone yasa ta gyad'a mishi kai alamar wai tana sonshi don tasan Faruq sarai baida tausayi da imani kwanda ta bishi su rabu lafiya. Ya kafeta da ido can kuma yayi murmushi "matsoraciya ban yarda da wannan amsar ba ki bud'e bakinki naji muryarki kiyi magana da yawunki," "uhmm ina sonka" muryarta a sark'e ta fad'a. Ya shiga tsantsar farin ciki "are you sure? Kin tabbatar alk'awari ne fa," ta rufe bakinta da hannunta yadda zuciyarta take bugawa zai iyasa jininta hawa saboda tsoro. Ya ja da baya "ina k'aunarki Hibbah zan tabbatar miki da hakan idan kin samu nutsuwar zuciyarki, don Allah ki daina jin tsorona ki amince dani," ta gyad'a kanta, Nawaz ya k'ank'ame shi "uncle kullum kazo sai kasa aunty Hibbah tayi kuka saina fad'awa daddy na." Bata san sanda ta zube k'asa ba ta had'a kanta da gwaiwa, ya shafa kan Nawaz ya zare masa ido tare da d'ora

Table of Contents

Chapters

63 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});