Chapter 16
Chapter 16
ta kalleshi a tsorace tayi tsuru tsuru, ya cillo mata key d'in d'akinshi yace "kije ki gyaramin d'aki," abinda ya fada kenan ya juya yayi ficewarsa. Hibbah ta kalli Hadiza tace "wallahi baba Hadiza Faruq tsoro yake bani shiyasa mafa banason fitowa parlor saboda kar mu had'u dashi, sau tari ina jiyo dariyarsa dasu Saudat amma nake k'in fita gashi yanxu kuma ya Sani wai gyaran d'akinshi." Dafa kafardarta Hadiza tayi tace "Hibbah Faruq d'in da kika Sani da Bashi bane yanxu, Faruq ya sauya ko lokacin da abin nan ma ya faru tsautsayine kawai don tuni Faruq ya sauya halinshi tun sanda Alhaji yayi masa fad'a ya nuna masa bacin ransa, don haka ki kwantar da hankalinki kije kiyi aikin daya Saki." D'aga Kai Hibbah tayi tare da fita daga kitchen d'in ta nufi d'akin Faruq d'in badon ranta yaso ba. Tana zuwa ta bud'e d'akin tare da shiga kallon d'akin tayi babu wani datti, tsarin d'akin ya burgeta babu wani tarkace, ta d'aga kanta hotunansa ne iri iri duk a kafe a jikin bangon d'akin, wasu ya rik'e ball a hannunsa wani kuma yayi tsalle kamar zai kamo ball d'in wani kuma ya k'ame da alama ma suna taken Nigeria ne aka d'aukeshi a hoton, a zuciyarta tace "kenan Ya Faruq d'an k'wallone," yayi kyau sosai kaminninsa da momy sun kuma fitowa, don duk 'ya'yan momy kamansu d'aya da ita babu Wanda ya d'auko kamanin daddy duk da bata tab'a ganin daddy'n nasu ba. Ta shiga toilet d'insa, ta fara dirza saidata wankeshi tas sannan ta saka air freshener ta turo toilet d'in sannan ta dawo d'akin. Blanket d'in kan gadon ta shiga linkewa ta ajiye gefe ta gyare gadon, sannan ta share d'akin tas ta fito da sharar ta debo ruwan mopping tayi ta goge masa wardrobe, tana cikin gogewa Faruq yaH shigo tare dasawa d'akin key ya zare key d'in ya zura a aljihun jeans d'insa, kallonsa tayi ta d'auke kanta duk da zuciyarta na cike da zoranshi, ya k'araso kusa da ita yana d'an murmushin mugunta yana jifanta da wani irin kallo. Batasan yazo dap da ita ba sai numfashinsa data ji daf da ita, da sauri ta d'ago kanta tana kallonshi kanne mata ido d'aya yayi, baya ta fara yi yana binta ji tayi ta zo bango, ta kalleshi idonta ya circuko da k'walla baki na rawa tace "Ya Faruq kayiwa Allah da manzonsa ka k'yaleni don allah," sai kuma ta saki kuka. Dariya ya saki saida yayi mai isarsa har ta fara zargin anya Faruq yana cikin hayyacinsa kuwa irin wannan dariya haka, sai kuma ya tamke fuska kamar Bashi ba ya nunata "Hibbah kinsani abinda bantab'a yiba wato tunanin 'ya mace, na Saba duk yarinyar datayi min kuma naji inada sha'awarta direct nake zuwa na biya buk'ata ta. Amma ke kin hargitsa min shiri tundana Saki a idona zuciya ta ta kwad'ata da wannan durin naki," cikin kuka Hibbah tace "wai mene a jikina me nake dashi da maza suke son b'ata min *RAYUWA*?" Faruq ya Saki dariya yace "ashe muna da yawa bani kad'ai bane, idan su sun k'yale wannan durin ni bazan k'yaleshi ba wallahi yau ko ana muzuru ana shawo saina d'and'ani wannan durin," bata Ankara ba ya fincikota tare da buga kanta da bangon d'akin k'ara ta saki ya wurgata kan gadon. K'arar data saki yayi dai dai da shigowar Aunty parlor zabura tayi cikin sauri tayi d'akinsu Hibbah bata ganta ba sai Hadiza kawai ta gani, a hargitse take kallon Hadiza tace "baba Hadiza ina Hibbah?" Hadiza bata kawo komai cikin ranta ba tace "Faruq yasa ta gyran d'akinsa tana d'akin.........." Kallon mamaki aunty tayi mata tace "Faruq?" D'aga mata kai Hadiza tayi. Aunty cikin tashin hankali tace "baba kina me har yasa ta aiki bayan kinsan k'udirinsa a kanta?" Hadiza itama da yanayin damuwa tace "wallahi Aysha gani nayi ya gyaru yanxu ya........" Aunty bata ma tsaya sauraronta ba ta fice daga d'akin. Shi kuwa Faruq bayan ya wurgata kan gadon binta yayi tare da hawa kanta yayi mata rumfa yana kiciniyar fidda rigar jikinta. Duk da cewa Hibbah kanta ya bugu amma hakan bai gusar da hankalinta ba, don tare suke kiciniya dashi hawaye nabin fuskarta. Ihu takeyi tana kiran sunan Hadiza da Aunty Aysha suzo su ceceta, Faruq yasa hannunsa ya toshe mata baki da hanci kamar zai mata k'amshin mutuwa cikin sa'a ya zuge zip din rigarta, ita kuwa Hibbah ganin yana k'ok'arin kasheta ba shiri ta sakar masa kanta, tasa hannunta akan nasa tana k'ok'arin cire hannusa daga bak'inta cikin sa'a k'aramin d'an yatsanshi ya shiga bakinta ita kuwa ta gantsara masa mugun cizo, cika mata bakin yayi yana yarfe hannu. Yunk'urin tureshi ta Fara yi, shi kuwa kamar cingam sai kuma manne mata yakeyi, tuttureshi takeyi tana kuka mai sauti tana kiran ummanta, mari ya shiga zuba mata ta ko ina, Aunty tana fita tayi d'akin Faruq tana zuwa taji ansawa d'akin key, da gudu tayi hanyar stairs direct d'akin momy ta shiga ta nufi wata k'aramar wardrobe inda momy take ajiye spare keys ta janyota ta dudduba babu su babu alamarsu, hankalinta ya kuma tashi ta janyo ta biyun suma basa nan, ata ukun ne ta gani cikin azama ta kwasosu duka. Da gudu ta sauko daga stairs a matattakala ta k'arshe wani key ya fad'i, ta kalli k'asan bata ganshi ba kawai tayi gaba tana zuwa jikin k'ofar taga Hadiza itama duk ta rud'e, suna jiyo ihun Hibbah tana kiran sunansu dana ummanta tazo ta taimaketa, jikinta har b'ari yake ta shiga gwada keys d'in, hankalinta ne ya kuma tashi jin Hibbah ta saki wata gigitacciyar k'ara gashi kuma gaba d'aya keys d'in sunk'i yiwa d'akin. Allah ne ya bawa Hibbah sa'a ta hankad'e Faruq daga kanta ya fad'i k'asa tayi hanyar fita da gudu ya fizgota ta fad'o kansa, stool d'in dake kusa dashi ya dinga buga kanta dashi har saida yaga ta fita hayyacinta sannan ya d'auketa yayin gado da ita. Ya zubeta shikuma ya shiga cire kayan jikinsa, har wani b'ari yake duk ya k'osa ya kusanceta. Parlor Aunty da hadiza suka koma suka shiga duba k'ark'ashin stairs ko zasuga key d'in amma shiru kakeji gashi hankalin Aunty duk ya tashi, Hadiza ce ta hangoshi k'ark'ashin kujera hannu ta zura ta d'auko tace "Aysha ga mukullin nan," da sauri aunty ta waiwayo tare da amsa tayi d'akin Faruq tana zuwa tasa key d'in kuwa ya bud'................. *by* *Mamyn Najmah* [10/26, 9:22 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *RAYUWA* page2⃣3⃣ *NA* *MAMYN NAJMAH* 🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION* D.B.W.A *DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA* *Masu cewa kirarin dana yiwa AYSHA ALI GARKUWA yayi yawa, to kuyi hakuri ba laifina bane k'aunace tasa na fad'a da babbar murya AYSHA ALI GARKUWA GAGARA BADAU CE BABU KAMARTA.* *A*unty tana bud'e k'ofar ta danno kai cikin d'akin abin da ta gani ya d'aga mata hankali, Faruq ne akan ruwan cikin Hibbah daga shi sai trouser ita kuwa ya cire mata Riga bra ce kawai a jikinta sai skirt d'inta dake manne a k'ugunta, kukan kura aunty tayi cikin b'acin rai ta hankad'e shi ya fad'i k'asa. Ta d'ago Hibbah a gigice take kiran sunanta amma Hibbah ko motsi batayi, hankalin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63