Chapter 36
Chapter 36
ba, ba'a shiga tsakanin Bawa da ubangijinsa ni bana aikata manyan aiyuka bana shan giya bana sata, kisa bare fashi da makami, to menene a ciki kawai don mutum yayi rayuwar da yake ra'ayi tajin dad'i sai ace ya sab'i Allah? Ina sallah, azumi da bin iyayena to menene saura kuma?" "Haka ne to amma ina batun b'angaren Mata naji ka keb'ance shi ko shi baya cikin manyan lefuka? Ba wani inkari da zakayi don kai Gwani ne ta wannan fannin" ya sosa k'eta "kin gane Allah gafurur rahim ne, wannan va wani abu bane kawai lokaci ne daga na aure ki zan daina, don nasan zaki gamsar dani bani da lokacin bin wasu matan" ta dubeshi "hali zanen dutse, a duniya babu abinda nake k'yamata kamar miji mai neman mata, kai kuwa ya zame maka jiki duniya ma ta shaida haka, to saboda me ni kuma zankai kaina ga halaka?" Wani abu ta gani a idanunsa da alama maganarta ta tab'ashi sosai, bai ce komai ba ya fita, tayi d'an murmushi ta k'arasa aikinta. Yana parlor bai tafi ba ta ajiye musu abinci ta koma d'akinta ta gyara don da bata nan yayi k'ura, saboda tunda ta tafi Nawaz ya koma wajen daddy'nsa da kwana. Tayi sallah a gajiye take ta kwanta cikin tunani daban daban, tun daga sanda Faheem yaje gidan Umma, tana jiyo kalaman Umma ko ya ta d'auki Faheem? Lallai yana da k'ima da girma a gunta bata tab'a yi mata maganganu masu zafi haka ba................ *by* *Mamyn Najmah* [10/26, 9:25 PM] Maman Najma Author P1: 📝🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *RAYUWA* page3⃣6⃣ *NA* *MAMYN NAJMAH* 🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓🍓 *DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION* D.B.W.A *DEDICATED TO AYSHA ALIYU GARKUWA* Washe gari da safe ta shirya zata tafi school taga Nawaz bai tafi ba yama cire uniform tace "Nawaz ina shirin makarantar?" "Aunty Hibbah daddy ne yace yau bazan je ba uncle d'in mu ya bani hutu sai gobe," tayi murmushi "to haka ake so Nawaz Allah ya k'aro sauk'i, ni kuma zan tafi school saina dawo" "aunty Hibbah ki tawo min da chocolate" ta shafa kansa "a'a Nawaz doctor ya hana shan zak'i saboda ciwon ciki" tana rik'e da hannunsa suka fito har bakin gate suka gaisa da Isah, yana tsaye a wajen Isah ya d'aga mata hannu "Aunty Hibbah bye bye sai kin dawo," ita ma ta d'aga masa hannu gami da fita daga gidan, ta soma tafiya har ta k'arasa bakin titi. Ta jima a tsaye bata samu mota ba, duba agogo tayi taga ta kusa latti ta soma tafiya ko zata samu a gaba. Hon don haka ta kauce ta basu hanya, "Aunty Hibbah" juyowa tayu don jin muryar Nawaz, shine da Daddy a motar, sanye yake da T shirt ta d'an d'ame shi, sai ya koma mata kamar Faruq don shi bai saba d irin wannan shigar ba yafi sabawa da shigar manyan kaya. Nawaz ya fito ya bud'e mata baya, dak'yar ta shiga tace "daddy barka da safiya" "lafiya lau Hibbah, wane school kike ne? Ko kema kina inda su Saudat suka gama?" Tace "eh" Shiru ya ratsa sai Nawaz dake ta suruntunsa, Hibbah kuwa zancen zuci take tana mamakin Faheem wane irin mutum ne shi Wanda ta kasa saboda dashi har yau. Sun iso makarantar ya ajiyeta a bakin gate, tana k'ok'arin fita taji yace "k'arfe nawa zaki tashi?" "K'arfe biyu ne" "ok ki jirani" a sanyaye ta fita daga motar, ta kasa shiga school d'in tabi motar da kallo. Ji tayi an dafata ta d'an tsorata ta waiwayo Fauzy ce tana mata dariya "Hibbah me kike jira ko har kin fara duty ne yau?" Hibbah tayi dariya "a'a Fauzy ai kema kinsan bana fara duty da wuri, yanxu fa nazo" fauzy taja hannunta "zo muje class da labari fa su momy sun amince da Ya Nazeef" Hibbah tana murmushi tace "da gaske?" "Wallahi kedai muje na baki labari," suka k'arasa class. Ranar wani yanayi ne mai dad'i a ranta kawai tunanin Faheem ya tsaya mata a rai haka komai nashi take gani harta yarda yake yin tuk'i a nutse da kalamansa masu saka nutsuwa, Allah mai iko wai har takai matsayin da zai kaita school bayan ba komai bace ita sai 'yar aikinsa, Anya kuwa zak'ewar batayi yawa ba, ko da yake Faheem da Aunty halinsu iri d'aya ne sun d'auke ta ne a matsayin 'yar uwa ne ba 'yar aiki ba, kuma yana girmamata gashi akwai kunya da nauyinsa da take ji don bata iya hawa motarsa don dai bata iya yi masa musu. Wani tunani tayi, yanzu idan Kausar ta gano tana shigar mata motar miji ai ta shiga uku, Anya kuwa bazata gudu ba idan yazo yaga bata nan ai zaiyi tafiyyarsa, kuma tunda ba wata magana suke yi ba bazai tambaye ta ba. Ana tashi kuwa tayi sauri ta had'a komai nata suka yi sallama da Fauzy, tana fitowa gabanta ya fad'i ras, mamaki take yi kamar a mafarki anya Faheem ne kuwa? Ikon Allah, tasan ya ganta babu maganar tserewa. Yana kallon ta ta cikin glass ya Gaza d'auke idanunsa, magana yake a waya amma duk hankalinsa yana kanta sai yaji maganar ma tana neman gagararsa, ya had'iyi wani abu sai kace sihiri ya manne mishi kamar mayan k'arfe. Kamar ta nutse Sam ta kasa dubanshi tunda ta shiga motar ai gara d'azu da Nawaz shi yana gaba ita tana baya, wai wannan wane irin nauyi ne da kunyar Faheem Allah ya d'ora mata. Haka sukayi shiru a motar tamkar kurame, Faheem akwai shi da nutsuwa da lafazi a tausashe "Hibbah" ikon Allah saura kad'an numfashinta ta d'auke, shima sautin muryarsa ya sauya. "Ina son muyi wata magana kin shirya saurare na?" Muryarshi tayi sanyi duk sai yasa ta wani yanayi da bazata manta shi ba a ranar, "nafi son ki bud'ame baki kiyi min magana tunda nima mutum ne kamar ke ki daina wani d'ari d'ari Dani, ni na d'auke kine tamkar 'yar uwata" yayi murmushi dayaga ta d'an Saki ranta "mene a tsakaninku da Faruq? Ki fad'amin gaskiya kinsan dai Faruq k'anina ne ke kuma amana ce a hannuna Hibbah" shiru tayi, "Hibbah bakice komai ba" "daddy shine yake zuwa........." "Nasan shine yake zuwa ma'ana maganar daya shafi soyayya" ta d'anyi shiru "gaskiya batun wannan bansan a muhallin da zan iya ajiye Faruq ba, shidai a cewarsa wai zai aure ni...." " kin tabbatar kina sonshi?" Zuciyarta ta shiga harbawa a ganinta cin fuska ne tace bata son d'an uwansa ciki guda. Ya sauke ajiyar zuciya "baki ce komai ba hakan na nufin kinason shi kenan?" Ji tayi gabanta yayi mugun fad'uwa tace "Daddy magana ce mai nauyi zan fad'a amma ba'a wannan lokacin ba" yay d'an murmushi yaji dad'in wannan furucin nata. Yayi parking a wani babban shop ya shiga ya d'an jima a ciki kafin ya fito, tunda ya fito ta k'ura masa ido ta glass d'in tana kallon sa da yake glass d'in a rufe yake kuma mai duhu ne, tabbas wani abu take ji yana ratsa zuciyarta ko mene wannan d'in? Yabshigo motar k'amshinsa kawai yana mata dad'i mutum ne gentle, ya ajiye ledojin a kujerar baya suka tafi. Nawaz yana ya biyo su, yana gama parking ta shige gida ta barsu anan. Tana
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63